Showing 57001 words to 60000 words out of 91674 words
Chapter 20 - SALON SO SABON SALO COMPLETE Book by Momyn Fareesa.txt
waya ashe vedio yake mata"yaya sadeeq kaje mana"murmushi na tsaya kimun saina tafi"lura da wasu y'an mata da matan aure dake gefe suna kallonsu yasaka noor tayi murmushin badan ta shirya ba"sadeeq ya juya yatafi beyi mgn ba......bayan an idar da sallah noor tayi addu'a da godema Allah daya bata sadeeq amatsayin masoyi"domin ita kanta shaidace akan yanada halayen kirki be a cikin mazan wannan zamanin"tana anan Inda yace ta jirashi"mata da maza anata hayaniya wasu na tare da y'an matan su wasu matansu"ahaka sadeeq da nura da sauran abokansu suka tafo"noor tayi k'asa da kanta tana mik'ewa tsaye ta ninke abin sallar"sadeeq ya iso gefenta yana fad'in beauty nah baki gaji da jira ba?"murmushi kawai tayi tak'i mgn"nura yakama dariya yana zolayar noor"itadai kanta ak'asa ta gaishesu gaba d'aya"marafa na tab'e baki yace"malamai kuje mota karku firgitamun mata da muryoyinku"duk suka kama dariya suna tsokanarsa sukayi gaba"bayan tafiyarsu murya can k'asa yace"my noor wai meyasa kink'i yarda mu had'a ido dake?"kodai da gske bakya sona?"yafad'a yana marairaice murya"sosai yabama noor dariya"duk yadda taso ta dake saida tasaki murmushi har fararen jerarrun hak'oran ta suka bayyana"marafa yabita da kallo na burgewa yana k'ara shige mata yace"Allah ban yardaba saikin fad'amun matsayina agunki....pls yaya sadeeq kadena mun haka bbu kyau "nidai muje mota zan sanar maka ko?"gaba d'aya jikin sadeeq yamutu murus sakamakon jin muryar noor"beyi mgn ba yayi gaba ta biyosa abaya"da kansa yabud'e mata front sit tashiga"bayan yashigo ya kalleta yana fad'in kinsan Allah kisanarmun kona rungumeki ba damuwata bace"tunda harna furta miki kema yaka mata ki sanar mun kinyi accepting ko kuwa??"to idan banyiba fa?"my noor kenan"ai shi SO ba'a masa dole saina hak'ura dana so wacce bata sona"amma ina mai tabbatar miki da wuya na rayu idan bani tare dake.....sosai kalamansa suka mata sanyi arai"cikin sanyin murya tace"yaya sadeeq kanason marainiya y'ar talakawa marar gata??bayan kai kanada gata"anya tafiyar zata yuyu?"d'aure fuska yayi yana fad'in irin wannan zaton kikemun kome?"to ba haka sadeeq yakeba noor"yaka mata ace ayanzun kinsan kaf halayena"koma micece ke ahaka nake sonki har k'arshen numfashi na noor"mamy tajima da mana kallon muna soyayya"saidai kawai nayi shiru"ko yanzun so takeyi Ayi aurenmu "nima kuma inaso in har iyayenki sunyi bincike akaina sunga na cancanci zama miji agareki.....cike da gamsuwa da kalamansa noor tace"toba dama ina sonka ba!sosai ta bashi dariya"sai bayan yaja motar yace"fad'amun dg yaushe kika fara jin soyayya ta aranki??"bazan iya ganewa ba"Allah sarki my noor nima wlh bazan iya ganewa ba kawai dai naganni akogin soyayyar ki"murmushi tayi ta b'oye fuskarta"kinsan Allah ajiye wata kunya zakiyi sbd nidai tsarin turawa nake dashi"sannan kuma bana son wannan gudun nawa da kikeyi kina zama nesa dani"shiru kawai tayi gabanta nata fad'uwa"fatanta itadai ba yanzun za'a yi auren ba.... kisanarwa innah suyi bincike akaina sannan naturo magabatana idan anbani dama"da sauri haka yaya sadeeq?"furtawarce nayi amakare amma dg had'uwarmu zuwa yanzun wata nawa my noor??"amma yaya sadeeq kasan ummana bata k'asar nan?"hakane my noor nafiso dama kafin Ayi aurenmu dake musan Inda umma take ko?"kanta ak'asa tace"hakane"to yanzun muje ka kaini gida"ah ah gidan mamy zamuje muci abinci sannan muje shan ice cream saina kaiki gida"gobe kuma make up zan kaiki amiki sbd ranata ce nikad'ai zamu shiga gari"murmushi kawai tayi tana mamakin tab'ararsa"Ahankali tace"nidai kana bani kunya wlh yaya sadeeq"dama mamy haka take mana kallon masoya?"eh mana ko basu bane?"azuciya muke soyayya kema kin sani"yanzun kimun shagwab'ar sai naji ko?"shiru tayi tak'i mgn"kinji?"uhmm! nidai yaya sadeeq kadena mun haka zance nama fasa soyayyar dakai"dariya yayi mai sauti yace"lallai my noor kin rainani da yawa"dama ana yiwa soyayya haka?"nidake ai mutu ka raba insha Allah"hakane yaya sadeeq dan Allah kuntab'a soyayya da wata?"ta fad'a tana turo baki bata yarda ta kallesaba"nooryn yaya sadeeq itace first love nasa"kamar yadda shima shine first love nata"yafad'a yana yin parking aharaban gidansu"yaga motocin abokansa"tab'e baki yayi yace"ashe wad'annan gardawan sun iso tuni"yaya sadeeq meyasa wai bakada tsoro ?"my noor kenan! ai matsoraci bai tab'a zama gwani har abada"muje kiyima mamy barka dashan ruwa ko?"dato ta amsa suka fito dg motar"yakama hannun ta"jikinta har rawa yakeyi tana so ta k'wace"murmushi yayi yacika hannun"yana fad'in muje ki cire hijab kisha Iska ko?"to yaya sadeeq zan cire"yauwa my noor dama kinsan bana son musu"hakane amma nidai bazaka jimaba awajen friends naka?"banaso kabarni nikad'ai"bakyaso najima ne?"yafad'a murya can k'asa"kanta ta gyad'a masa"beyi mgn ba yatura k'ofar main parlour sukashigo"mata 2 y'an mata da wasu yara na zaune suna cin abinci"amsa sallamar su sukayi suna gaida sadeeq"ya amsa bbu yabo bbu fallasa"noor tace"ko mamy na ciki?"inaga tana ciki" zomu zauna nasan gardawan can na parlou nah"yafad'a yana amsar hand bag d'in noor"ita kuma ta zauna"bud'e hand bag d'in yayi yazaro veil red colour"sannan yasaka mata rafar y'an 500 guda 2 aciki yazuge zif d'in"kafin ya ajiye mata agefenta shi kuma yaduk'a gabanta yana fad'in cire hijab d'in ga mayafi kisamun"sosai noor taji kunya gashi gaba d'aya yashige mata yanata aikin kallonta har tana jin hucin numfashinsa"y'an matan dake cikin parlourn nata kallonsu"sanin beson musu kawai yasaka ta cire hijab d'in"amma bata bud'e kantaba"ta amshi mayafin"meyasa bakya so nayafa miki da kaina?"yafad'a murya can k'asa yana murmushi stiil yana duk'e gabanta"noor kasa mgn tayi ta amshi mayafin ta yafa sannan tajanye hijab d'in"kawo na ninke miki ko?"bbu musu tabashi yana ninkewa mamy ta fito dg bed room d'in ta"kallo d'aya ta musu ta d'auke kanta"sbd sak kamar amarya da ango suka mata"tana murmushi tace"ga y'ata ga y'ata"yau b'atan kai kikayi ne noor?"sadeeq daya saka hijab d'in a hand bag nata yamik'e tsaye yana murmushi yace"gata nan dai ai mamy"yafad'a yana nufar upstairs"noor na murmushi cike da kunya ta sakko k'asa ta gaisheta da mata barka dashan ruwa"mamy ta amsa cike da kulawa"tana k'walama mairo kira"bayan ta iso tace"maza kawoma noor abinci da abin motsa baki....lah mamy na k'oshi"ban aminceba"to abarshi sai anjima"to shikenan.... sadeeq kuwa dama kafin yatafi idi yasanarwa mamy ashirya komai acikin parlourn sa "su nura na isowa ta k'ofar baya yabud'e musu suka shige parlourn marafa"aikuwa yana shiga yasamesu sunyi d'aid'aiya"kowa yayi k'at yayi hani'an"suna zancen saida la'asar aje gidan nura da wani sufyan"sauran kuma duk gwabraye ne"sadeeq na tab'e baki yace"k'attin banza yaka mata kuyi aure hakanan"harda kai acikin mu"cewar wani salman"hmm kake gani ko?"to bari kaji! girkin madam d'ina ne dana mamy kuka ci"haka nura yafad'a mana"gsky kayi dace Allah ya tabbatar da alkhairi"sadeeq ya amsa da Ameen "ya zauna sunata shegantaka da zancen y'an matansu"abin mamaki har sadeeq na saka baki"wanda Inda adane zaibar musu wajen yana tsaki...sai wajen 11 am suka sakko down stairs"mamy ce kawai da bak'i a parlourn"bayan sun gaishe da mamy"sadeeq yaga bbu noor besan time d'in da yace"mamy ina beauty nah??kan mamy ak'asa tace"tana d'akina bacci takeyi"okay kar atayar da ita mamy dan Allah"dato kawai ta amsa"su kuma suka fita"sai asannan bak'in ke tambayar mamy ko noor ce sadeeq zai aura?"ta amsa musu da eh.....noor kuwa dama jiya batayi bacci sosai ba sbd sunsha aiki"tayiwa kuma zainab kitso da dare"koda ta shigo d'akin mamy"prayer mate ta shimfid'a ta aza pillow ta kwanta bayan tacire mayafinta"bbu jumawa bacci yayi awon gaba da ita.....bayan tafiyar su sadeeq mamy ta turo mairo ta duba noor idan k'asa ta kwanta tace"ta koma saman bed"in kuma tayi bacci ta barta kawai"mairo na zuwa taga noor kwance k'asa tanata bacci"hakan yasa mairo tabar d'akin ta kama wata hidimar daban......
sai wajen 12 pm sadeeq yadawo gidan" sbd yaga noor ta tashi taci abinci??da sallama yashigo cikin parlourn"bak'i ne dai y'an yawon sallah"mamy da alama tana kitchen"bed room d'in mamy yanufa yana murmushi....anutse yatura k'ofar yashiga"da noor yayi tozali kwance tana bacci ta tsuke d'an bakinta"yabi bak'in gashinta da kallo tumbuji guda"had'e rai yayi yana fad'in aka barmun ke ak'asa my noor?"be koma mgn ba yafito dg cikin bed room d'in"mamy kuma ta fito dg cikin kitchen"tana rik'e da plate d'in dake d'auke da snacks"ta ajiyewa bak'i"suka gaishe da sadeeq"mamy ta zauna tana kallon yadda yawani d'aure fuska"agefenta yazo ya zauna yak'i mgn"lafiya kaida baka gajiya da saurin fushi??sadeeq yayi saurin cewa" mamy meyasa aka bar mun noor k'asa ga samqn bed pls?"yafad'a yana b'ata fuska"ohni sadeeq"wlh dama nayi zaton idan kazo zakayi korafi" shiyasa nace mairo taje ta duba mun idan k'asa ta kwanta ta koma saman bed ashe bata sanar mata ba"d'aure fuska yayi yana fad'in dg yau na sallameta aiki agidan nan"to shikenan me gida"cewar mamy fuska ad'aure tana mamakin wane irin sone sadeeq ke yima noor haka??"sassauta murya yayi yadda bak'in bazasujiba yace"amma mamy kinsan bata kyautaba ko?"to idan anyi kuskure ai gyara akema mutum"kuma nidai banga laifin mero ba anan "sannan kasan noor da kunya da kawaici kasan bazata kwanta samqn bed d'ina ba ko?"hakane kuma mamy"bara na dubata nagani"mamy batayi mgn sadeeq yamik'e tsaye yanufi bed room d'in mamy.....✍️
wannan book d'in na kudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki bamiki ba"..........yana tura k'ofar noor na kawowa itama zata bud'e ta fito"kusan fad'awa jikin sa tayi"da sauri tayi baya tana turo baki tak'i kallonsa balle masa mgn"cikin cool voice yace"kin tashi my baby?"uhmm"kinyi mafarkina?"nidai kasan mamy na nan kabani hanya na wuce ko?"idan kinada k'arfi ki tureni ki wuce mana"yafad'a yana kallonta"canza topic d'in tayi da cewa kaci abinci?"ah ah"meyasa yaya sadeeq?"sokake yi duk karame ko?"ta fad'a cikin sanyin murya tana b'ata fuska"kema me mgn baki ciba"gashi kina jini kin kai har wannan time d'in baki....kukan shagwab'a tasaka tana turo masa k'ofar ta tsaya abayan k'ofar"sadeeq yadinga dariya"mamy na satar kallon su tana murmushi"yaya sadeeq kabani hanya na wuce bbu ruwana dakai tunda kunya kake bani"gsky my noor ki denamun haka" sai kace wata y'ar kauye ko wacce bata je skul ba??"Eh naji itace ka bani hanya nidai"tafad'a tana sakin kukan shagwab'a"sadeeq ya jingina jikinsa da bango yanajin kamar ya janyota jikinsa ya rungumeta"my noor rigimarki tayi yawa wlh "yanzun fad'amun mekikeso Ayi?"nidai kaje kaci abinci kamayar dani gida tunda natashi dg baccin"ai d'azun nashigo kinata bacci bbu d'an kwali naga gashin da aketa b'oyemun ko?"dan Allah da gske kashigo?" ta fad'a tana kallonsa ta wani zaro ido"sadeeq yasaki murmushi yana fad'in kinyi kyau my noor"itama murmushin tayi kafin yace"zo muje muci abinci saina mayar dake gida"sanin idan ta masa musu bazasu kwashe lafiya ba ta amsa dato"shine yayi gaba"ita kuma tabiyosa tana sinne kanta k'asa"y'ata kin tashi?"cewar mamy"Eh mamy"masha Allah yaka mata kici abinci yanzun ko?"eh mamy ,ita tasa kamun rigimar banci abinciba ashe itama bataciba?"yafad'a ko ajikinsa yanayin gaba"mamy tayi murmushi kawai tana tunanin gara dai azo Ayi auren nan ta lura rawar kan sadeeq yayi yawa....da wannan tunanin tabar parlourn sbd noor ta sake sosai"sadeeq kuwa zafafan kalamaine na soyayya yaketa fad'ama noor suna cin abincin a plate guda"amma kowa da kansa yakeci sbd tana jin kunya akwai masu shigowa y'an yawon sallah"wajen k'arfe 1 suka gama"sai bayan sadeeq yayi sallah sannan yazo noor tayi sallama da mamy"wacce ta had'a mata abin arzik'i"sannan suka nufi mota"Ahankali noor tace"nagode sosai yaya sadeeq da k'aunar daka nunamun da kulawa kaida mamy"Allah yasa kad'ore haka"sbd ana cewa wasu mazan bbu tabbas"indai kin yadda da irin yadda nakejinki araina toki cire wannan tunanin noor"kuma ki dena mun godiya haka"insha Allah sadeeq bazai canzaba kamar yadda nake fatan kema bazaki canzaba my sweet baby"bazan canzaba yaya sadeeq inajinka sosai araina"fatana Allah yabarmu tare yakaremu"Ameen yah Allah my noor"yauwa yaya sadeeq kud'i nagani a cikin hand bag d'ina?"tafad'a tana b'ata fuska"my noor kenan"niban tab'a ganin wanda ke k'in kud'i ba sai ke"ko kuwa kud'in da suka fito wajenane kike k'i?"bafa haka bane yaya sadeeq"to yanzun nidai bani bane na baki mamy ce ta bani d'azun da safe tace"nabaki idan mun fito sbd tasan bazaki amsaba"Allah sarki mamy akwai d'awainiya da mutane"Allah yasaka mata da alkhairi"Ameen yah Allah"sai kuma kice Allah yabamu baby girl bayan aurenmu muyiwa mamy takwara ko?"kasa mgn noor tayi tsabar kunya"saima asannan ta tuna da abinda akeyi a samu ciki a haihu"sosai taji tsoro tana kauda tunanin aranta"sadeeq kuwa dariya yadingayi"yanata tsokanarta ita kuma tak'i kulashi"har suka iso wajen shan ice cream"bbu kunya sadeeq yashigema noor yanata bata abaki"datace mutane yace"zai rungumeta agaban su idan bata tsaya ba"adole ta hak'ura"bayan sun gama suka nufi gidan inna"saida noor ta shiga ciki tasanar ma inna sannan ta dawo suka shiga ciki atare da sadeeq"innah nata masa maraba"ta shimfid'a masa tabarma atsakar gidan"yazauna yana yafito noor da hannu wai tazo" ta nok'e kafard'arta"kan sadeeq ak'asa yagaishe da innah da mata barka dashan ruwa"kafin anutse yace"Alhmdllh ! inna anyi sallah lafiya angama"inaso dan Allah kimun wata alfarma inna"kar kuma ki kalli sbd noor ne "ah ah" ki dubi abun da sbd Allah nayi"ina jinka Abubakar sadeeq fad'amun ko menene?"cewar innah"dama innah ba wani abu bane" inaso jibi in Allah yakaimu zanzo da marece na d'aukeku keda su noor da sauran y'an gidan naki ku koma sabon gidanki dana baki halak malak"dan Allah innah karkice ah ah"nayi dan Allah badan sbd ina son noor ba"masha Allah Abubakar sadeeq! zanyi shawara da magabatana tukum naji ta bakinsu "amma hidimarka agaremu tayi yawa"ko kayan abincinnan daka kawo wlh sunyi yawa ga kayan sallah kamana kayiwa noor"dan Allah innah kidena fad'i yiwa kaine"hakane Allah ubangiji yajikan mahaifin ka da rahama"Allah yayi maka albarka"ya amsa da Ameen yana murmushi cike dajin dad'i"inna Ahankali tace"dama inaso kazo zamuyi mgn dakai game da noor"ina tambayarta soyayya kukeyi sai tayita mun yawo da hankali tana cewa ah ah"ni kuwa nasan ba haka bane kuna ganina tsohuwa kar nake kallanku"sadeeq yayi dariya"inna taci gaba da cewa"sadeeq idan da gske kakeyi kana son jikata marainiyar Allah kasanarmun nasa Ayi bincike akanka"wlh inna da gske nake son noor da aure"kuma ko yanzun akace nafito ashirye nake"sannan Ayi bincike akaina kafin asanarmun naturo iyayena"to shikenan Alhamdllh"Allah yazab'a mafi alkhari"sadeeq ya amsa da Ameen"ya ajiyema innah kud'i yatashi yafita yanajin tana fadin bazata amsaba"noor dai na d'aki tana jin firan sadeeq da innah"aranta tanajin haushin masa mgn da inna tayi wai da gske yana sonta...bayan fitarsa itama ta fito sbd ta masa rakkiya.....
zaune Alh labaran yake agaban wani mushirikin boka"wanda kallo d'aya zaka masa kasan besan miye imani da tausayiba"babu kaya ajikinsa sai ganye daya d'aura a k'ungunsa yab'oye tsiraicinsa dashi"wata tukunyar k'asa na gabansa yana surkulle aciki"yyinda Alh labaran yayi shiru yana kallonsa"can saiga fuskar sadeeq da noor data mamy ta bayyana"boka yakama wata iriyar mahaukaciyar dariya"yana nuna tukunyar"Alh labaran ya kallesu yace"tabbas sune wa'annan kuma inaga itace yarinyar da sbd ita yamari y'ata....cikin wata iriyar murya boka yace"zamu baka magani ka zuba sadeeq yataka ya wuce koya tsallaka"sannan zamu baka wanda za'a zuba masa acikin abin sha "idan yasha shikenan zai kamu da lalurar rashin lafiya da d'oyin jiki"ta hakane kowa zai gujesa harda mahaifiyarsa da wannan yarinyar da nan gaba kad'an zata zama matarsa"kai kuma saika auri mahaifiyarsa kayi yadda kakeso da dukiyarsu..... Alh labaran na washe hak'ora yace"to amma boka bbu wata hanyar daza'a bi maganin yayi aiki dole sai an zuba masa yasha ya tsallaka??"boka na wata iriyar dariya yace"bbu wata hanya saita nan"dan mutum ne shi mai yawan addu'a"kuma mahaifiyarsa da wannan yarinya suna masa addu'a"yana cikin kariyar ubangiji shida mahaifiyarsa shiyasa kwanaki bakayi nassara akantaba"sannan wannan aiki yanada had'arin gske"muddin ka kuskure koka zuba be tsallaka ba kobeshaba tofa reshe zai juye da mujiya....bangane ba boka?"cewar Alh labaran yana zaro ido"wata iriyar dariya ta mugunta boka yakece da ita yana d'aga hannu sama"atake wasu k'ullun magunguna guda biyu suka sauka asaman hannun bokan"ga wannan na bak'ar leda shine zaka zuba acikin abin sha"gudan kazuba yataka koya tsallaka ya wuce"zakayi hakane idan kasami dubarar ta yadda zaka zuba masa"sannan bazai auri y'arkaba, wannan yarinya itace matarsa.... Alh labaran yace"bbu matsala indai buk'atata zata biya"yafad'a yana ajiyewa boka daman kud'i yatashi yafita"bokan yakama dariyar mugunta....
*Bayan sati 2*
Alhmdllh acikin y'an kwanakin sadeeq da noor anata zuba soyayya"dukda noor najin kunya kuma tana ja masa aji da wanashi"yanzun haka sun tashi sun koma sabon gidan daya basu bayan innah tayi shawara da danginta"sun kumayi na'am"sbd a bincikensu sun gane sadeeq da iyayensa mutanan arzik'i ne akwai mutunci"ayanzun haka kwana 3 da suka wuce an saka ranar auren sadeeq da noor wata 3 masu zuwa"fad'in murnan da mamy da sadeeq ke ciki b'ata bakine"sannan yanzun noor ance tadena zuwa aiki sbd shine zata aura"wadda dama noor d'in fushi takeyi da sadeeq sbd ansaka musu rana"bayan ita ba haka tasoba"tafiso Ayi auren nanda shekara guda sannan taje gun mamanta"gaba d'aya dg jiya zuwa yau noor tasaka sadeeq acikin damuwa"bata d'aukar wayarsa ko masa reply na messages daya turo mata"yanzun haka kan bincike yakeyi acikin anguwar ankil game da Abba d'ahiru da halayensa"dan ta haka yake ganin zai san Inda mahaifiyar noor take" wanda anan yasami labarin abinda yafaru da y'arsa harta rasu"kuma har yanzun ba'asan Inda hamisu yakeba"wanda ayanzun kowa dangi da y'an uwa sunsan komai"noor dataji zancen abinda yakashe halima har kuka tayi"ta tuna itafa Abba yaso aketa mutuncinta amma ga yadda hukuncin Allah yakasance"gaba d'aya yanzun Abba dahiru baya a hayyacinsa"yyi bak'i yarame"ga fushin uwa akansa shiyasa abu goma da ishirin yahau kansa"dan tunda inna tace"yazo za'a kawo kud'in gaisuwar noor yace"bazai zoba bbu ruwansa da ita da aurenta beda babbar makiyiya aduniya sama da noor"dg nan innah ta kama fushi dashi"amma ko a jikinsa"noor kuwa ta koma wayewa da gogewa"ta zama y'ar gatan sadeeq"idan tana masa shagwab'a tana wanashi bazakace itace y'ar 18yrs ba"gaba d'aya yanzun goggo saude tajata ajiki sosai tana k'ara nuna mata hikimar zaman aure da k'issar kula da d'a namiji....
Ayau yakama week end"gaba d'aya sadeeq duk yadamu da fushin da noor keyi dashi"yana ganin zaije yau ya rarrasheta idan bata son auren yanzun sai a fasa sai sadda takeso"zai samu yashawo kan mamy......cikin nutsuwa sadeeq yashigo parlourn mamy"cikin takunsa irin na zaratan maza"yana sanye da kayan ball yellow ajikinsa riga da wondo