Showing 3001 words to 6000 words out of 91674 words
Chapter 2 - SALON SO SABON SALO COMPLETE Book by Momyn Fareesa.txt
damunka dazaka tsaya kana sa'insa da mace?"nura yakatse wa noor mgn"wlh nura sai tasan taga yamun mgn"wannan banzar ,y'ar cikina zata gayamun mgn haka na barta"yafad'a cikin zafin rai yana k'ok'arin danna kansa cikin nafef d'in sbd ya fisgo noor yadaketa"fuskarsa bbu alamar mutunci atare da ita"ga haushin b'ata masa jiki da akayi da lokaci kuma"saidai nura be bari yashiga ba ya rik'e hannunsa iya k'arfinsa" yana dakawa me nafef d'in tsawa akan yaja subar wajen"noor ta zuro kanta suka had'a ido da sadeeq ta masa gwalo"aikuwa atsiyace me nafef yaja suka bar wajen"sadeeq ya hank'ad'a nura ya fisge hannunsa yayi gaba yabarsa bece uffan ba" dukda kuwa tsaidashin da nura yakeyi"mutane nata kallo kowa yayi gaba"sadeeq yyi tafiya me nisa kafin yayi waya da iro driver"yasanar masa 10minit yabashi yazo ya d'aukesa a Inda yake" muddin be isoba kan time bakin aikinsa....yana kashe wayar yafara jan tsaki babu k'ak'k'autawa"zuciyarsa na zafi da k'una"akanme nura zai masa haka ya hanashi ya d'auki mataki?"ko namiji d'an uwansa ai bai isa yagaya masa mgn ba balle wata mace"kuma yarinya k'arama"yatabbatar wannan banzar yarinyar batayi 20yrs ba"amma nuran zai gane kuransa ta yadda idan akace wata ran yamasa haka bazaiyiba koda wasa"wayoyinsa nata ringing yamusu banza dan bayajin zaiyi lokacin kowa"koda costomers nashine kuwa" yana tsaye abakin wani gurin shakatawa"mutane nata kallonsa jefi jefi"shi kansa idan ya kalli jikinsa sai yaji ya muzan ta"gashi farar t shirt nasa ta b'aci sosai...wani irin mugun tsanar yarinyar yaji aransa"yanajin inama yakoma ganinta....hmm! da shine kawai yasan meye zai mata.....yana ahaka saura 1 minit time d'in daya d'ibarwa iro yacika"aikuwa iron ya iso takashi zage sbd beson akoresa dan ba k'aramin alkhairi yake samu awajen ogan nasa ba"saidai yadda yaga fuskar sadeeq da jikinsa ya tabbatar ransa ab'ace yake"hakan yasa ya kama kansa sosai"ko mgn beyiba sbd kar yayi laifi "kawai bayan yafito ya bud'e masa back sit"shima beyi mgn ba yashiga ya zauna.....wajen 5:15 pm suka iso gida"mamy na zaune a parlourn itada zahida"sadeeq ya shigo babu ko sallama"mamy tabishi da kallo atake ranta yabata bbu lafiya"sannu da zuwa sweet heart! cewar zahida"doguwar tsuka yaja cikin zafin zuciya sadeeq yabita da kallo da jajayen idanuwansa yace"duk ranar dakika koma kirana da wannan banzan sunan jikinki zai gaya miki....sadeeq lafiya zaka shigo mana bbu ko sallama?"cewar mamy fuska ad'aure tana kallon jikinsa"beyi mgn ba yanufeta kawai"yana mamakin rashin tarbiyya da kunyar zahida"agaban mamy take kiransa da sweet heart"zahida kuwa kallonsu takeyi kamar tv"ranta ya sosu da irin wulak'ancin da sadeeq ke mata"tamkar k'aramin yaro haka yazo ya zauna gefen mamy"ya aza kansa asamqn cinyarta ya lumshe idanuwansa yana sakin ajiyar zuciya"ta shafi tattausan bak'ar suman kansa tace"sadeeq bakaji ko?"dan Allah karage wannan zafin zuciyar da saurin fushin naka"yanzun miye haka ajikinka?ina kuma nuran?"shiru yayi yak'i mgn"mamy nata kallonsa can tace"kaje kayi wanka tunda bazakayi mgn ba"amma mamy waccan k'azamar na zaune zanyi mgn ?(zahida)" murde masa kunne tayi tana d'aure fuska tace"karna koma ji"Allah mamy nura saiya san ya hanani nayiwa yarinyar nan hukunci.....wace yarinya kenan sadeeq?"cewar mamy tanajin fad'uwar gaba wanda bata san daliliba"sannan kuma girarta ta dama taji tana fat fat fat"shiru sadeeq yayi dan beso yayi sub'utar bakiba mamy taji"sannan yasan wannan magulmaciyar zahidan itama taji"sai kawai yatashi zaune yace"mamy bara naje nayi wanka"dato kawai ta amsa"shi kuma yamik'e tsaye yanufi upstairs"shi kansa yasan mamy itace farin cikin sa"gaba d'aya da b'acin rai yashigo amma yanzun yaji sanyi aransa damuwar ta rage"amma har yanzun haushin nura da kucakar yarinya data masa rashin kunya na'a ransa"da wannan tunanin yayi wanka yana jan tsaki"yasha alwashin shida kayan har abada" dama yau yafara sakasu kuma yagama....sai wajen 6:30 pm ya sakko down stairs da farar jallabiya ajikinsa zai tafi masjeed"yanada niyar sai 9 pm yadawo gidan dan kar mamy takoma masa zancen dayake gudu.....yana k'ok'arin fita dg cikin parlourn yaji muryar mamy tana fad'in sadeeq masjeed zakaje?"Eh mamy saina dawo ko?"amma kidafamun coffee"to shikenan Allah yatsare"ya amsa da Ameen yafita"tabishi da kallo har yab'acewa ganinta"taja ajiyar zuciya tana masa fatan Allah yasa yasamu mace ta gari me sonsa wacce zata bashi farin ciki.....zahida na d'aki tanajin motsinsu"saidai gabanta nata fad'uwa da zancen yarinyar da sadeeq yace zai hukunta"fatanta Allah yasa ba budurwarsa bace.....
*wanene sadeeq marafa?*
Alh muhammad marafa shine mahaifin sadeeq"asalinsu y'an kaduna ne kasuwanci na siyar da fata yakawosa baushi da zama"har ya had'u da Amina anan bauchi"sukayi auren soyayya"bayan aurensu da shekara 2 ta haifi sadeeq"wanda ya d'akko kamanin mahaifinsa sak dan daddy kyakykyawa ne"tun dg sadeeq bata koma haihuwa ba"dangin daddy nata cewa yak'ara aure amma ya nuna bayada buk'ata"cikin ikon Allah sanadin fata arzik'in daddy nata bunk'asa"sadeeq yataso cikin gayu da gata agun iyayensa"da sauran dangin mamy dan kowa nata na anan garin bauchi yake"tun primary skul sadeeq ya had'u da nura suke abota har suka gama primary sukayi secondary school atare"anan kuma sadeeq mahaifinsa yafiddashi k'asar waje"kasancewarsa tun kafin asashi skul yana masifar son zane"to kuma bayan yashiga skul sai abun yacigaba"gaba d'aya skul nasu bbu wanda yakaisa iya zane"hakan yasa daddy yafidda shi k'asar UK"tun sadeeq na SS3 mata suka fara nuna masa soyayya"tun a time d'in be wuce 17yrs"shi kuma yana yarfasu"kasancewarsa miskili magana bata damesa ba"dakaga yana doguwar mgn abune mai mahinmanci"ko kuma tare da iyayensa ko nura shine zai saki jiki yayi mgn"mahaifin nura Alh Hamza abokin daddy ne"shi nura fannin kasuwanci ya had'a digree nasa "shi kuma sadeeq ya had'a digree nasa afannin Architecture"time d'in yanada 25yrs daidai"yakoma zama santalelen saurayi mai jini ajika"dg shi har nura bbu wanda keda budurwa"nura nason yayi soyayya amma sadeeq daya dawo nigeria saiya hanashi"wanda nura harkan kasuwancinsa yakeyi da taimakon mahaifinsa" yanada super market"watan sadeeq biyu da dawowa dg UK"daddy yarasu sanadin accident"fad'in tashin hankalin da mamy da sadeeq suka shiga b'ata bakine"ko 40 days beyiba da rasuwa"danginsa su biyu dasuke uwa d'aya uba d'aya sukazo dg kaduna"Alh labaran da Alh dauda "da wasu mutane (police)" wai Alh labaran nabin daddy bashin million 10 harda wasu takaddu na shaida"kamar abin magani"sadeeq ya amince shida mamy bbu bincike"sai gashi sauran gidan dasuke da mota 2 da wani gida da sauran million 2 suka rage na dukiyar Daddy"acikin y'an watanni suma sukayi k'asa"sbd dama sadeeq be sami aiki ba, abinda aka tara aketa ci"abin mamaki kuma Alh labaran yadawo baushi da zama shida matarsa da yaransa 3"Ahmed ,zahida da maryam"kuma shima yafara harkan siyar da fata"abin yabama sadeeq mamaki"tun dg lokacin sadeeq yaji yatsani mutumin"mamy dataga sadeeq bashida aiki gashi kuma yanada takardu masu kyau annemi aiki ba'a samu ba"ta kira Alh labaran ta masa zancen koya aro masa kud'i yagina ma'aikata"sarai yanada su amma yace babu"sadeeq yadinga yiwa mamy fad'an meyasa ta tambayesa?"tun dg lokacin saiya kama sadeeq ke zuwa gidan Alh labaran"sannan kuma zahida Allah yadasa mata son sadeeq aranta"wanda daya fahimceta yaci gaba da disgata da mata wulak'anci"danshi soyayya haushi take bashi yana mata d'aukar wahalar da kai"bayashiga cikin mata"ko course mate nasa mata baya sake musu fuska"hakan yasa wasu ke masa kallon me girman kai"kuma abin ba haka bane"sadeeq yana masifar son mahaifiyarsa da son farin cikin ta"ya k'ware sosai wajen iya zane"ko siffar mutum yasani tsab zai iya zanashi bawai saiya kalli photo nashiba"wata ran wani abokinsa d'an gidan governor yyi bathday shine ya zanashi yakai masa gift"shinefa kowa na family d'in yaron yagani"anata mamaki"har mai girma governor yace akira sadeeq yaji idan Architect ne shi?"aikuwa sadeeq koda aka sanar masa bama dan yasoba yazo"sai gashi zuwan yazamar masa alkhairi"yasami aiki kuma a office na gwabnati"duk wasu ma'aikatu ko titina, ko zana wasu makarantu da sauransu shine ke zanawa agina"da abin yacigaba saima aka dinga bashi kwangilar ginawar"idan yazana yasaka agina"shi kuma abiyashi"anan sadeeq yasami d'aukaka"har ya gina company nasa yana zana furnitures da kujeru ak'era"sannan yana zana ma'aikatu suma agina"hakama yana zana mutum abiyashi.....acikin shekara 10 kacal sadeeq yazama hamshak'in mai dukiya"dan company nasa *marafa interprises* babu Inda ba'a sanshiba a nigeria"yanzun sadeeq nada 36yrs aduniya amma beyi aureba"kuma bashida niyama balle yayi"tunda Alh labaran yaga sadeeq yayi kud'i yakeso yasamu ya auri hjy Amina "wacce sadeeq ya hanata aure tun bayan rasuwar daddynsa"dan manyan mutane nata sin tirin zuwa wajenta"yayinda zahida ta goge tasha bleeching"yanzun tanada 25yrs"ta haukace a soyayyar sadeeq bataji bata gani"mahaifinta da ummanta hjy kuluwa sunsha alwashin koda boka koda mlm saita auri sadeeq sbd su yagi rabonsu ta dukiyarsa....nura kuwa sati 2 kenan da aurensa"wanda sati 1 dayin bikin sadeeq yatafi Abuja" sbd anyi inviting nasa a wani company "shine yaje yayi sati 1 ya zauna a hotel"
sadeeq kyakykyawan gaske ne ajin farko"baya dg cikin mazan banza na wannan zamanin"har ransa beson miye soba"shifa ko zama bayayi yace wai yanajin sha'awa"bema saka abin aransa "in dai yayi mafarki shikenan"miskili ne sosai na bugawa ajarida"sannan beson raini da shishshigi sbd yanada masifar son girma"ga bak'ar zuciya da Allah yamasa"be cika fara'a ba sai agaban mamy"wacce har shagwab'a yakeyi hankalinsa kwance"idan kuwa mamy ta masa zancen yayi budurwa ko yayi aure aranar bata gane kansa"harma tana zaton ko bashida lafiya ne"amma dg baya ta gane sarai lafiya qlau yake"dan dg bayama idan ta masa mgn sai yace ai lokacine idan yayi zaiyi"mamy nason rik'e ko yaran dangi y'ay'a mata"amma sbd miskilancin sadeeq yasaka ta fasa"saidai yawanci y'an matan dake zuwa week end gidan ko hutu duk suna zuwane sbd shi ko sunja hankalinsa"amma bema san sunayiba"dg zahida sai hafsat y'ar k'anwar mamy da suka nace sunk'i hak'ura akansa"sadeeq bashida aminin daya wuce nura suka she su rufe da juna"kuma yana jure halayen sadeeq"yyinda sadeeq ayanzun bashida wani babban mak'iyi irin *Alh mansur* wanda aikinsu iri d'aya ne amma sadeeq marafa yafishi samun d'aukaka"sannan Alh mansur yanada masifar son mata"ba kuma wani babba bane "acikin 6yrs ya auri mata 4 yana saki"kuma be haihu ba"ba kuma girman sadeeq yayiba"sunan *marafa* yasamo asali tun suna secondary school friends nasa ke kiransa da haka"sadeeq nada son yara"amma miskilin be nunawa"kawai dai yana yawan kallon tashoshin da ake nuna karatun yara ko wasannin su ko kuma ya kalli tom& jerry"sannan idan yaga yaro to zai kallesa amma bazai kirashiba"kuma yara basu zuwa wajensa sbd be sakin fuska"hakane yasa bbu wanda yasan yanada son yara yadai barma ransa ne kawai... sadeeq nada kyauta ta bazata"wacce idan yayiwa mutum zaiji dad'i ya yaba masa"shiyasa idan lokacin dayakeyin zakka yayi mutane sunta suntiri kenan zuwa gidan mamy"wasu kuma acan office suke zuwa neman taimako"sadeeq nada tsabta ta tashin hankali,sbd yanada k'yank'yami"sannan yanada son abincin gargajiya"yyinda sallah bata wucesa kan lokaci yakeyi.....idan sadeeq na mgn cikin muryarsa duk macen dataji baza taso yadena ba"bayan baiwar kyau akwai ta murya"saidai wankan tarwad'a ne ba fariba"๐คช sadeeq dogone bai cika jiki ba amma yanada manyan k'wanji da faffadan k'irji"dan ma'abocin motsa jiki ne"doguwar fuskarsa na d'auke da saje bak'i daya zagaye da sallaya bak'i k'irin atsakkiyar goshinsa"yanada red lips"yyinda yanada manyan idanuwa"abin saidai ace masha Allah........hjy Amina mace ce me kirki da kyauta da taimakon na k'asa da ita"kullum addu'ar ta naga sadeeq" kuma alhmdllh duk Inda zai shiga lafiya zai fito yanata samun d'aukaka"saidai sadeeq be sani ba a company nasa mamy nada yara 2 maza amintattu dake kamata labarin rayuwar da sadeeq keyi a office"shiyasa ko korar ma'aikata yyi saidai yaji tace yamayar dasu"idan yace taya tasani?"zata sanar masa sune sukazo sukace tabashi hak'uri....babu yadda zaiyi zai kuma mai dasu wannan kenan anan gaba zakuji abinda bakujiba.....cigaban labarin
Afannin noor kuwa.......โ๏ธ
wannan book d'in nakudine
Normal grp 300
Vip grp 1000
Special people 2k wato 3pages in a day
zaku biya kud'in ku ta wannan acc number๐2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne
banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraโ
Y'an nijar kutuntub'i wannan n๐ +227 88 01 90 50
Normal grp 500f
Vip grp 1000f
Special people 2000f
dan girman Allah da darajan iyayenki karki mun mgn idan baki shirya biya ba๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
๐น๐SALON SO ๐น๐
(sabon salo)
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
It's rometic love story๐โคโ๐ฅ
Story & written by mommyn fareesa
Free page 5&6
.........afannin noor kuwa time d'in da suka bar wajen ta saki ajiyar zuciya"tana tuna duk Inda tasan wannan masifaffan mutumin ta sanshi"amma ta kasa tunawa"saidai ranta yabata k'ilan a tv ko a jarida ta sanshi"kalmar mahaukaciya daya kirata dashi yabata haushi sosai"yakuma tsaya mata arai"da wannan tunanin suka iso anguwar water board quarters"me nafef ya tsaya bakin k'ofar wani had'add'en gida me farin get"fuska ad'aure yace"bazan jirakiba ki biyani hakk'ina nayi gaba kawai"in bacin wannan bawan Allah (nura) da yanzun ina police station"haka kawai kijamun masifa"noor batayi mgn ba dan tasan muddin ta tankashi zasu kwashi y'an kallo dan itama bata d'aukar raini"200 ta ciro dg post nata ta mik'a masa ta jawo hannun yaron suka fito dg cikin nafef d'in"noor na sanye doguwar riga ta atamfa da hijab k'arama iya gwiwa ajikinta"kai tsaye get d'in gidan ta tura tana rik'e da hannun yaron suka shiga.....kimanin mintina15 ta fito ita kad'ai dg cikin gidan ta iso bakin titi ta tari nafef"saidai zuciyarta acunkushe take"kamar tayi kuka"innalillahi wa inna ilaihir raju'un kawai take maimaitawa aranta"sbd gudun kar tabi son zuciyarta"dan halin data tsintsi kanta aciki sai addua kawai....da wannan yanayin aka sauketa a anguwar kaduna road"kai tsaye gidan Alh salis kaita ta shiga"a part d'in uwar gidan ta nufa hjy wasila"domin ta sanar mata takai yaron gidan su"(d'an y'ar matar ne yazo musu yini shine yake kuka akace ta maidashi gida sunansa khalil"a hanya yaga me sob'o yace"yanaso shine noor ta siya masa)
hjy wasila na zaune hakimce kan kujera tana kallo, y'an aiki nata aikinsu ana musu izzah da tsawa"noor tayi sallama ta russinah tana fad'in hjy na maidashi tace"agaisheku"hjy na wani yatsina fuska tace"kije part d'in Al'ameen ki gyara masa"dan Allah hjy kiyi hak'uri asaka su sahala su gyara yanzun marece yayi zan tqfi gida ne...ke kin isa inyi mgn kimun musu?"karki manta ba kyauta zakiyi ba biyanki akeyi"ko kuwa aikin kikaji dashi kinaso ki fad'a karuwanci tunda kinada kyau?"subahanallahi! Allah yatsareni su kuma masuyi Allah ya shiryesu"hjy na k'ok'arin mgn Al'ameen yashigo cikin parlourn yasha gayunsa cikin manyan kaya"saurayi d'an kimanin 30yrs"wanda ya goge da harkar bariki idanuwansa sun bud'e"tunda yaga noor agidan kimanin wata 2 kenan yakeson jan ra'ayinta su aikata sab'on Allah ita kuma tak'i yarda"shine ke cewa ummansa aturota ta gyara masa d'aki"ita kuma idan taje yadinga yimata zancen banza kenan" ko kuma yyi k'ok'arin tab'ata"bata yarda ta gudo tana kuka"shiyasa tayi k'aryar marece yyi asaka sahala ta gyara masa"saida noor taji fad'uwar gaba dataji muryar Al'ameen"kan kujera ya zauna yana binta da wani shegen kallo yace"hjy bafa agyaramun part nawaba"ga wannan nan dana sakq ta gyara" ba kowan kowa ba galadiman kashi tace"asaka sahala ita gida zataje"noor ranta ab'ace ta mik'e tsaye tace"hjy kiyi hak'uri dg yau nadena aiki"dama jiya kud'in wata yacika"abani kawai Allah ya had'a kowa da rabonsa"wani banzan kallo hjy ta mata tana jan tsaki tace"saiki bari Alh yadawo yabaki 10k d'inki"aiki dan kin bari wata tsiya ce Allah na tuba"ai dama matsiyacin mutum be iya cin arzik'i ba"ya isa haka hjy"ke ki cigaba da aikin ki zan ninka miki kud'in ki.....bazata yiba wlh tunda ta zab'i ta dena"umma ki barta in har zata iya.....bazan yiba! noor ta katsesa tana kuka tabar parlourn"Al'ameen yamik'e tsaye dan yabita hjy ta daka masa tsawar karya bita"tana kuka gwanin ban tausayi ta fito a haraban gidan"sai Allah yasa me gidan yafito dg cikin mota kenan zai wuce ciki"anan yaganta ta gaishesa"ya tambayeta meyasa take kuka?tasanar masa ta dena aiki kuma hjy bata bata albashintaba"hak'uri yabata sbd yasan mugun halin hjy wasila"yazaro kud'i 50k yabata "tace" 10k kawai zata fidda sune iya hakk'in ta"yana murmushi sbd ya fahimci yarinyar tanada tarbiyya yace"kije kinyi wata hidimar sbd Allah na baki in har kin daukeni matsayin uba kinji?"godiya ta masa ta fice dg gidan"tana tuna meyasa wasu masu kud'i ke taka talaka kamar sune suka bama kansu arzik'in?"bayan Allah ne yabasu badan yakuma fi son suba sai sbd adalcinsa"gaba d'aya abinda zqinab maman khalil ta mata d'azun dataje maida yaron yatsaya aranta"dan itama tarban wulak'anci ta mata sbd bataso mijinta yaganta"dan noor akwai kyau na d'aukar hankali....ga abinda yafaru d'azun ahanya ga wannan ga matsalar cikin gidansu"tana kuka ta hau nafef "anguwar inkil aka ajiye ta"wato gidan Abba dahiru (k'anin mahaifin ta)gabanta nata fad'uwa sbd bata san yaya zasu kwashe ba idan ta fad'i ta dena aiki"kud'in ta fiddo ta fidda 40k ta b'oye ajikinta"kafin ta wuce cikin gidan nasu na masu k'aramin k'arfi"lokacin anata kiran sallar magrib.......
*sumayya haruna* shine cikakken sunanta"ana mata alkunya da noor sbd sunan kakarta ne aka saka mata ta wajen uba"mlm haruna haifaffen garin bauchi ne kowa nasa na anan" su ukku ne awajen iyayensu"haruna dahiru da saude"mahaifinsu yarasu tuni sai nene mahaifiyarsu"kasuwanci yakai haruna k'asar agadaz anan ya auro matarsa mariya"fara kyakykyawar gaske buzuwa kuma"yataho da ita a baushi"suna zaman mutunta juna da soyayya har ana cewa ta mallakesa"tun bayan aurensu mariya keta faman yin b'ari"data samu ciki saiya b'are"kusan sau 5 tanayin b'ari sai na shidda juna biyun yatsaya wanda a lokacin kusan shekararsu 8 da aure"fad'in murnarsu itada mijinta bata bakine"bayan wasu watanni ta haifi y'arta mai kama da ita"saidai bata d'akko hasken taba"wankan tarwad'a ce ita"aka saka mata suna sumayya"ta taso cikin gata"tun bayan noor basu koma haihuwa ba"umman noor na bata kulawa da tarbiyyar datace"tanada 6yrs aka sakata boko da islamiya"yayinda mahaifin noor ke sana'ar siyar da kayan fruits"kuma Alhamdllh yana samu dan basufi k'arfin komai ba"ahaka noor ta fara tasawa"tanada 13 yrs tayi saukar alk'ur'ani me girma ta kumayi JSCE"a time d'in tafara girma"tun tasowar noor matsiwaciya ce sosai"ta iya jan