Showing 39001 words to 42000 words out of 57158 words
Chapter 14 - YAYA FAHAD NAWA NE COMPLETE by Nasmatu Muhammad .txt
in komayin wani abinda Abba na zai tsane ni" ya koma fashewa da kuka Allah sarki gabad`aya tausayin sa suke ji, dakyar Baffa ya rarrashe shi da kalamai masu sanyaya rai tareda bashi wasu manyan addu'oi na neman tsari da kariyar Ubangiji (s.w.a) yace yaje yaji da matanshi duka biyun ya kasance mai adalci a agare su". Nan ma yayi godiya ya mike ya fita
Suka bishi da kallon tausayi Mai martaba ya kalli Liman yace "gafarta Malam yanzu kuma sauran aikin naka ne kaje ka d`ebi sauran Malaman dake fada kuyi karatu a sauke Alkur'ani mai girma a yanka dabbibi ayi sadaka a gayawa Allah damuwar nan na tabbata zai yaye mana Yarima zai sami kanshi" gaba d`aya suka amsa da "insha Allah" yace "to na sallame ku" suka tashi suka fita d`akin ya rage daga shi sai Baffa da Goggo da kuma Bashir nan suka shiga ja'jantawa juna da godewa Allah daya bayyana musu wannan da wuri daga bisani su Goggo suka koma masaukin su suka bar Mai martaba ya huta.
Yarima kuwa tafiya yake yana nazari yarasa inda tunanin sa ke zuwa idan yaga fateema gaba d`aya sai yaji ya tsane ta, idan ta kaucewa ganinsa kuwa ba abinda yake tunani sama da ita yasan yana mutukar Son Fateema amma idan yaganta sai tsanar ta ce take maye gurbin ti meye wannan? Ya tambayi kansa a lokacin da yake shia gidan nashi
*Yar'mutan Arkilla* ✍
💞💞💞 *yaya*💞💞💞
💞💞 *fahad*💞💞
💞💓💞
💓
💞💞💞 *Nawa*💞💞💞
💞💞 *ne*💞💞
💞💓💞
👯💓👯
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
*Writing by*
_Nasmatu Muhammad_✍
*•246/250•*
*Wannan shafin kuma naku ne Ilahirin members na NASMAT NOVELS GROUP ina mika d`inbin godiyata gareku sakamakon so da kaunar da ku ke nunawa littafi na, haka ku ma KING BOY ISAH NOVELS bazan manta ku ba Allah yabar zumunci da kauna Allah ya Albarkaci rayuwarmu da ta yaran mu Ameen* 🙏
Kamar yanda yabar Fateema haka ya dawo ya same ta hard`e akan kujera. Da sauri ya kauda kanshi daga kallon nata, dan gujewa jin haushinta. Ita kam ko kallon gefen shi batayi ba saida ya shigeta sannan tabi bayan sa da kallo, sai taga yayi sanyi kalau ko a yanayin tafiyarshi ma mutum zai fahimci hakan. Kai tsaye d`akin baccin Lazeera ya nufa kwance ya same ta ta kifu kan gado tana ta faman aikin na ta wato chat. Jin shigowar tashi ne yasa ta tashi ta zauna tana kallon shi cikeda mamakin yanda yayi sanyi ga wani uban ja da idonshi sukayi wanda ya tabbatar mata da kuka yayi. Mikewa tayi ta taro shi tareda rungumo gefen jikin shi "Ya Prince lafiya kuwa? Ya naganka haka?" dakyar ya d`aga hannu ya shafi gefen fuskarta "bakomai dear Mai martaba ne ya kirani yace yana so...." Sai kuma yayi shiru sakamakon fad`uwar gaban daya riskeshi a lokacin da ta kafeshi da ido sai yaji yanajin nauyi da tsoron gaya mata ance ya maida Fateema
"meye yace wai?" Ta tambayeshi cikin d`aga murya, yayi shiru kanshi na sunkuye a kasa. ya Rabbi abinda yake nanatawa a ransa kenan baisan daliliba kawai tsintar kansa yayi da mugun tsoron bacin ran Lazeera. Kanshi na kasa yake gaya mata "kiyi hakuri ki had`o kananan kayanki zamu koma d`ayan part d`in can mubar mata wannan" Lazee ta zaro ido "mene?" "Inbar gidannan nan wai? hmmm ai bazai yuwu ba wlh bazata sabu ba wai bindiga a ruwa, kaje ka gaya mishi bazan fita ba nasan dai ba wanda zai ce haka sai shi to wlh bai isa ba..." Keee! Yarima ya katse ta da wata irin tsawa mai firgitarwa "mahaifin nawa ne bai isa ba?" ya tambayeta yana kallon cikin idon ta. Mamaki ne karara ya bayyana a fuskarta kodai asirin ya karye ne? Ta tambayi kanta sai kuma ta cije dan koma jarrabawa tace "eh shi d`in ko rama masa zakayi?" Yarima yaji kamar ya rufeta da duka amma ina azahiri rarrashinta ya hauyi da ban baki akan ta taimaka masa su barwa Fateema gidan, tare da alkawarin zai kara gyara mata wancan ita ma. Dakyar yasamu shawo kanta, da taimakon shi suka tattare duk wani abu dasuka zo dashi sannan ya fita yashigo da kuyangi biyar suka kwashe kayan suka fita, sannan su Yariman suka fito Lazee na gaba yana binta a baya d`auke da babbar jakar ta, ta wuce tana wurgawa Fateema kallon banza tanaji a ranta kamar ta rufe ta da duka, sosai tabawa Fateeman dariya, ta kuwa dara. sannan itama ta raka su da harara kafin ta make murya tace da yarensu na fulatanci ("kord`o reube") wato "bawan mata" da harshen hausa, a fusace ya juyo "me kika ce min?" Tace ni? Ta fad`a tana yatsina fuska bance komai ba. yanda tayi maganar ma abin kallo ne, ji yayi ta kara fusata shi ya dawo dabaya da nufin dukan ta, ta mike da gudu ta shige d`akin ta tana masa gwalo. ya tura kofar yaji a rufe gam sai kuma ya tsinci kansa dajin haushin hakan yaso ta tsaya yayita ganin ta koda yanajin haushin ta ne
Lazeera ce ta daka masa tsawa a fusace to wai meye hakan? Wasa ma zaka tsaya yi da ita? Yarima ya turbune fuska da me zan tsaya wasan? yaja tsaki sannan ya rufawa Lazee baya dan ita tuni tayi gaba zuciyar ta na mata zafi da tiriri. Wai an maida Fateema yanzu zaman kishi zasuyi kenan? ta tambayi kanta uhum tayi wani murmushi inaa wlh bazata sabu ba ta dai dawowa gida amma ba Yarima na ba. Da wannan tunanin suka isa d`ayan part d`in wanda yake kusan had`e da na Fateema suna fuskantar juna ginin duk iri d`aya ne komai da ke nan akwaishi a can banbancin d`aya ne na gyare-gyaren da akayiwa na Fateema kaman sabanta fenti da zuba sababbin furnitures da kayan kitchen.
Shine ya nemo wasu kuyangin suka gyare musu sashen tas! Akwai komai a ciki duk ba kowa a sashen hatta kayan abinci babu wanda babu sai dai ba wani dad`in ganin hakan yaji ba kasancewar gimbiyar tashi ba girki take ba a cewarta ba aikinta bane shi kuma Yarima baya iya cin abincin masu aiki sai dai su siyo su ci kullum suna hanyar restaurant abin na damun sa, haka dai aka gyare ko ina aka feshe da turaruka. Lazeera kam zaune take tamkar gumki ba um ba um'um hatta chatting d`inda ta mayar sana'a yau gagararta yayi duk abin duniya ya isheta, tunani take ta inda zata bullowa zaman ta da Fateema hanyoyin dazatabi ta killace Fahad take nema sai saka take tana warwarewa
Fateema kam tana shiga d`akin tashiga gyare-gyare dan a cewarta bazata kwanta akan dettin su ba, tana cikin yi Bilki tashigo tareda Rukayya su suka taya ta ta canza was bedsheets ta kwashe kayan make-up dake kan mirror ta zuba wasu sababbi nacikin kayan lefenta, kayan ta kam suna nan ba'a taba mata ko tsinke ba. Lokaci d`aya sashen ya d`auke da kamshi na had`ad`d`un turarukan wuta sannan ne tasami damar fad`awa bayi tayo wanka su Bilki suka can cara mata kwakliya taji da fad`a sannan suka bata wuri tasaka wata doguwar riga ta material wadda awayiwa zubin ado na stones kamar ba d`inkata akayiba
Wohoho wani irin kyau da sheki yadin ya kara mata hatta Rukayya da Bilki dasuka ganta saida suka kusan zaucewa gaskiya Fateema kyakkyawa ce ta gaban kwatance abinka da sabon jini kuruciyar ta gabad`aya ta bayyana a wannan kayan. Ta kalli kanta a nadubi tayi shiru a hakan na d`an lokaci kawai saiga hawaye suna bin kuncin ta,, cikin kad`uwa da mamaki yan'matan suka fara tambayar ta Rukayya tace "subhanallah anty Fatee lafiya kuwa, meyasa kike kuka?
*Yar'mutan Arkilla* ✍
💞💞💞 *yaya*💞💞💞
💞💞 *fahad*💞💞
💞💓💞
💓
💞💞💞 *Nawa*💞💞💞
💞💞 *ne*💞💞
💞💓💞
👯💓👯
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
*Writing by*
_Nasmatu Muhammad_✍
*•251/252•*
Fateema taja numfashi sannan ta share hawayenta da bayan hannunta tajuyo da jyau ta fuskanci Bilkisu da Rukayya tace "kuka ya zame min dole Rukayya ki kalleni, ki kalli kyan da Allah ya bani wanda ni kaina nasan inadashi, ga farin jini, bazan iya kirga muku samarin da suka soni ba, amma sabida jarraba ta rayuwa ban taba jin son wani namiji samada wanda nakeyiwa *Yaya Fahad* ba tun daga kurciya har girma haka yayita bautarda zuciya ta yana azabtar da idanuwa na, babu wani zuwa dazaiyi kauyen mu batareda ya sakani kuka ba, tun ina karama ya tsane ni, ba abinda yakeso samada ganin hawaye na, ni kuma ganin fuskarshi kad`ai ya ishi zuciyata farin ciki mara misaltuwa, yau takai ta kawo nazama matar auren shi amma duk da haka baya yimin kallon mutum ballantana inkaiga darajar matar shi, taja numfashi tareda share kwalla a karo na biyu tace tunda nake sau d`aya na taba ganin sona a idon Yarima a ranar da nazo nan a matsayin matar shi tabbas na hangi soyayyata a idon shi wannan ranar sai kuma daga baya ta rikid`e ta dawo kiyayya da tsana irin wadda bai taba nunamin ba koda a shekarun baya, wannan ne dalilin daya sa nayarda da maganarki tacewa asiri akayi masa ya ki ni kuma ya tsane ni domin kafin rabuwarmu naga sauye-sauye dayawa a tattare da shi,"
Tayi shiru kamar mai nazarin wani abu su Rukayya kuwa jikinsu ne yayi sanyi lis maganganun Fateema sun ratsa su hakika soyayyar datakeyiwa Yarima ga'garuma ce kuma abar kwatance. Can ta d`ago ta kalle su tace "shin ku bakuyi mamakin amincewata ta dawowa gidan auren Yarima ba? " gabad`aya sukayi shiru. Tayi murmushi tace "hmmm nasan zakuyi mamakin hakan saidai sam ba abin mamaki bane idan kukayi la'akari da irin son da nakeyiwa d`an'uwa na, sai dai fa kusani inada babban kalubale a gaba na" a tare suka kalle ta cikeda mamakin jin kukanta na neman tsananta cikin kukan tace "wlh yanzu gaba d`aya rayuwa ta abar tausayi ce na sadaukar da farin cikina domin ceto na iyaye na, na sadaukar da rayuwata gayin abinda ko alama banida ilmi da sanin yinshi, ya ake zama da miji ma bansani ba balle takaini yin kishi kishin ma da gogaggiyar mace yar'bariki, maibin bokaye da malaman tsibbo nashiga uku ni fateema na sanya kaina a hallaka" ta fashe da kuka rairas tayita raira abinta dakyar yan'matan suka rarrasheta tayi shiru Bilkisu ce ta fara magana "kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki anty Fatee indai wannan ne nayi miki alkawari zan taimaka mki da akwai wata Hajiya a babban layi take aikinta kenan horarda mata akan zamantakewar aure musamman kanana kaman ke, tana koya musu girke-girke da make-up, sanin makamar namiji, tana gyaran jiki, mace ta goge ta iya kowane irin dressing Hajiya Binta bata tsaya nan kad`ai ba akwaita da sani na ilmin addini a wurinta zaki sami addu'oi da nafilfilin da zaki rike domin kare kanki da kuma ceto mijinki daga hannun waccan shaid`aniyar"
Cikin zumud`i Fateema "tace kai amma nagode Bilki a ina wannan Hajiyar take?" Bilkisu tace "a babban layi take nan bayan gidan sarauta saidai matsalar ita ce nan gidan ba'a fita kasafai haka sai dai na tabbata in akwai isassun kud`i Hajiya Binta zata iya zuwa har nan ta koyar dake komai. Fateema tayi shiru tareda kurawa Bilki ido kamar mai karanta wani abu a fuskar ta'ta, sannan ta nisa tace "to yanzu Bilki kamar nawa kike gani za'a bata kuma a ina zamu same su?" Bilkisu tayi shiru tana nazari kafin tace "wurin mijin ki za'ki samu mana, adadin su ne dai ban sani ba". Rukayya tace "kibari gobe idan mun fita zamu tambayo miki ita, kuma ma zamu karbo miki harda lambar wayar ta sai kuyi magana ko?" Fateema batasan sanda ta sake dariya ba tace "banda abinki Rakayya aini ban taba rike waya tawa ta kaina ba, sai dai tazo muje can mu same ta sai ayi maganar koya kuka gani?" Rukayya da Bilki suka kalli juna kafin suka fashe da dariya dukkan su Bilki tace "kai anty Fatee da abin dariya kike shin kin manta yanzu da da ba d`aya bane? Yanzu fa ke matar Aure ce "Rukayya ta cafe da "matar ma ta gudan Yariman gombe" suka koma saka dariya. Abinka da kurciya nan da nan suka manta da damuwar su suka bige da hire-hire, Fateema taji dad`in hakan sosai dan koba komai ta manta da damuwar Yarima. Haka Goggo tashigo ta same su sunata hira taji dad`i sosai da taga yarinyar tata bata saka damuwa a ranta ba, su Rukayya suka fice suka barta daga ita sai Goggo nan ne Goggo ta sami damar zaunar da Fateema tayi mata nasihohi masu shiga jiki tareda jan kunnen ta gameda kiriniya ta jaddada mata yanzufa tariga ta girma ba kaman da bane, harma ta tsorata ta da cewa "muddin ta fita bada sanin mijinta ba kafarta d`aya zatafi d`aya tsawo ta dawo d`ingishi" ai kuwa ta tsoratan dan harda kukan ta. Tace "to dan Allah Goggo ki rokamin shi yadinga barina idan na tambayeshin". Gogga tace "wannan ba matsala bane in Allah ya yarda zai barki" hakadai tayita lallabata har suka tashi tafiya. har wurin mota ta raka su tana makale da Goggo sukayi sallama harda kukanta, sai taji wani iri kamar ba gidan da tasaba zama ba
*Yar'mutan Arkilla* ✍
💞💞💞 *yaya*💞💞💞
💞💞 *fahad*💞💞
💞💓💞
💓
💞💞💞 *Nawa*💞💞💞
💞💞 *ne*💞💞
💞💓💞
👯💓👯
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
*Writing by*
_Nasmatu Muhammad_✍
*•253/254•*
Da gudu ta juya tanufi bangaren su,Mai martaba yabi bayanta da kallo na tsayin lokaci kafin ya gyad`a kai ya koma sashen shi. Sosai take bashi tausayi na zaman da zatayi a gidan Fahad saboda tabbatarwa da akayi baya cikin hayyacin sa.
Fateema na shiga falon ta ta zube kan Capet ta shiga raira kuka mai ban tausayi, hakika ayanzu nikaina lamarinta ya fara bani tausayi. Tambayoyi ta shiga yiwa kanta a zuci "shin wane irin zama ne zatayi a gidan Fahad? Meye matsayin ta gareshi? Taya zata iya zama batareda fita ko'ina ba?" Sallamar su Bilkisu ce ta dawo da ita daga duniyar tunani-tunanin data tafi, a sanyaye ta amsa musu sallamar idanun ta sharaf da hawaye. wuri suka samu suka zazzauna shiru na d`an lokaci kafin Rukayya ta kauda shirun da cewa "Anty Fatee yanzu fa ba lokacin kuka bane, lokaci ne da zaki tashi tsaye da kafarki kiga kin kwaci mijin ki".
Fateema ta kalle ta cikin yanayin rashin fahimta "ban gane ba" ta bukaci karin bayani. Rukayya tayi murmushi domin sanin wace ce Fateema da tayi. tace "da sannu zaki gane" ta kalli Bilki ta kashe mata ido. Bilki ta mike ta shiga bayi na d`akin Fateema ba jimawa ta fito tana Fad`in "na had`a" Rukayya ta mike rike da hannun Fateema suka shiga d`akin kai tsaye bayi ta zarce da ita da shigar su wani dadda'd`an kamshi ya musu marhaba Fateema ta lumshe ido tareda bud`e hancin ta ta shaki kamshin mai matukar kwantar da hankalin wanda ya ji shi, ta sake mata hannu tareda cewa "kiyi wanka ki fito, muna jiranki". tana gama fad`ar hakan nan ta juya ta fice tareda ja mata kofar
Fateema ta since kaya ta shiga cikin bahon wankan ta kwanta shiru na wani lokaci mai tsawo dad`i da kamshin ruwan sun hanata tabuka komai, shiru kawai tayi kamar mai nazarin wani Abu. Karar bugun kofar ya farkar da ita daga nisan da tayi daga wannan duniyar wanda batasan abinda ya d`auke ta ba tsakanin bacci da tunani. muryar Rukayya ta ji tana fad`in Anty Fatee kiyi hanzari lokaci na tafiya.
Sauri-Sauri ta wawwatsa su tafito badan tana so ba. Sallar azahar suka fara gabatarwa suka ci abinci sannan suka zaunar da ita akan dressing mirror suka fara tsantsara mata kwalliya Masha Allah. Fuskar nan ta fentu tasha kyau harta gode Allah. Bilkisu ce ta fiddo mata wata koriyar riga doguwa asalin rigunan gidan Sarauta tareda mayafin ta suka ce ta saka, sannan suka fice falo suna jiran fitowar ta
Masha Allah wa tabarakallahu Ahsanal khalikeen! Bawai su Rukayya ba hatta ni Nasmy baki na sake ina kallon ikon Allah Fateema ce ta fito cikin koriyar rigar nan da Bilki ta fiddo mata tayi kyau tamkar yar'tsana kamar ba Fateen Goggo ba. Rukayya ta dafe hanci tareda rangad`a gud`a "gafara mahassada ga fitila, uwar gida sarautar mata, farar mace alkebbar mata, matar Yarima ikon Allah" gabad`aya suka kwashe da dariya. Yau ce rana ta farko da Fateema taji wani irin dad`i da aka kirata da matar Yarima! Ta zauna akan kujera tana kallon su tace "to ai sai ku gayamin dalilin wannan Uwar kwalliyar da kuka min?" Bilkisu tace "kina dai so ki sami kud`in da zamu biya mu d`auko Hajiya