Showing 27001 words to 30000 words out of 63585 words

Chapter 10 - FEERYAL Part 2 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.txt

kwanciyar hankali.

Da sauri ya karaso bakin gadon yashiga bubbugashi yana fad'in
"A.A wai bacci ka wanta yi a wannan lokaci?
ai kai da bacci sai bayan biki, dalla tashi ga ba ba'i can suna jiran ka."
tsaki ya ja
"Wai meye haka ne kam Imran ina ruwan ka da bacci na."
"Da ruwa na mana taya za'ayi ma ka kwanta bacci ne kam, to ko ni nan tun baccin jiya da daddare da na tashi da asuba ban kuma komawa ba har yanzu,
bare kuma kai uban gayyar da kanka,
mutanen Germany fa sun iso gana Abuja ma,
ko wanne nasa an musu masauki a hotel daban daban,
ya kamata ka tashi kaje ku gaisa dan kai fa sukayi tattaki suka zo,
musamman ma wad'an da suka taho daga wata kasar."

Kwafa ya yi tare da mike wa zaune yana aikawa Dr Imran mugun kallo
"Amma nace ban yarda ka gayyaci ko wanne daga cikin su ba ko."
"Au da so kake sai dai suji kayi aure, haba su da kullum suke maganar Allah ya kaisu ranar auren ka,
nasan suna yi maka fatan kar ka mutu tuzuru ne,
suma jajayen fata sukayi aure a kan lokaci bare kai da ka fisu kwari da lafiya,
taso kaje kayi wanka ka shirya da'alla mu tafi,
kar ka mance dai 8:30 na dare akwai kamu kuma kasan dole zamu je."

Tsaki yaja ya mike ya nufi bathroom yana fad'in
"Ai sai ka jani ka kai ni."

Kafin ya fito Dr Imran ya zab'ar masa kaya cikin sababbi kuma tsadaddun d'inkunan da Daddy ya yi masa.
ya feshe su da turaruka masu dad'i da sanyin kamshi.
ya d'auko hula da takalmin da zasu shiga da kayan suma duk sababbi ne, ya aje masa su kusa.
yana fitowa ya ce
"Yauwa yi maza ka hanzarta ga kayan da zaka saka."
baiyi magana ba sai hararar sa da yayi.
ya wuce gaban mirror ya zauna ya d'au Body lotion yasoma shafawa fuskarsa a murtuke.
Dr Imaran ya ce
"Yi da jikin ka mana kayi ka sa kaya."
ta cikin mirror ya hararesa
"Kai kafa dame ni ba maganar ka ce zata sani fita ba,
sai dun kada wad'an can mutanen da ka gayyato su suce sunzo kasar mu anyi musu wulakance,
badun haka ba babu abin da zaisa na katse bacci na."
"Eh na dai ji tun da zakaje ai shike nan karb'i kasa."
ya mika masa kayan.
sai da ya kuma hararar sa kafin ya amsa ya saka.
tun kafin ya gama shirin ai nihin kyansa da cikar halittarsa da kwarjinin sa had'i da cikar haiba suka bayyana a gare sa.
kayan ba karamin amsar kalar fatar sa wankan tarwad'a ya yi ba.
sai wani sheki fatarsa chocolate color keyi.
ya d'aura tsadadden agogo a tsintsiyar hanunsa kana ya murza huta a kansa,
ya zura takalmi a kyawawan kafafunsa masu d'auke da zarazaran yatsu da fafaren farce.

Dr Imran ya bud'e baki da hanci yana kallon sa,
sai yau ya dad'a ganin ainihin sagwaran kyansa a fili.
duk da shi ba fari bane amma ko kyawawan fararen fatan da suke kasashen ketare, basu isa su nuna masa ko mai ba.
ganin yadda Dr Imran ya bud'e baki da hanci yana kallonsa.
yaja tsaki ya zari makullin mota ya yi waje.
da gudu ya biyo sa na fa d'in
"Innalillahi kai ka ganka kuwa had'uwa iya had'uwa, wlh aure rahama ce tun ba'a d'auraba har ka kara kyau."

Bai kula shi ba ya yi gaba.
sai da yafito harabar side nashi ya dubi parking lot nasa, yaga motoci hud'u ne a ciki,
makullin motar daya d'auka kuma ya mance jiya ya faka motar a babban parking lot na gidan.
gajeren tsaki yaja,
sam baya son fita cikin gidan ya had'u ma da kowa, sai dai kuma ya fito baya son kuma komawa.
haka ya nufi get d'in sa badun ya so ba,
Dr Imran ya rufa masa baya.

Ai kuwa yana fita hankalin jama'a ya dawo kansa.
aka sunkuya masa kirari irin na ango.
Dr Imran kuwa sai washe baki yake yana d'agawa mutane hannu, har suka isa parking lot.
ya jefa ma Dr Imran key'n motar, ya cab'e yana cewa
"Ai dole na tuka ango."
ya shiga mazaunin direba shi kuma ya zauna d'aya gefen, Dr Imran ya yi wa motar key mai gadi ya bud'e musu get.

Suna fita hotel in da aka sauke 'yan Germany suka fara nufa.
yaga ko mai an tanadar musu na bukata
ya yi musu barka da zuwa, ya zauna suka d'an tab'a hira, kana suka fita suka je d'aya hotel d'in da aka sauke ma'aikata likitocin su na Abuja.
suma an tanadar musu komai na bukata,
bayan d'an hirar da sukayi da su ma.
kana yasa Dr Imran ya dawo da da shi gida.

Suna shiga gida ana kiran sallar magriba.
dan haka suka sauka suka nufu masallaci, sai da akayi sallar isha kafin suka shigo gida.
yana shiga bedroom d'in sa yashiga rage kayan jikin sa.
Imran ya karaso yana cewa
"Yauwa A.A yi wanka ka sauya kaya da sauri kaga time na zuwa kamun nan ya yi,
na gayawa Dr Sharif da Dr Taj mu had'u a can,
bai kyautu ace bamu je musu ba."
"Kai nifa babu in da zani, ka dai na cika min kunne zaka iya tafiya dan bacci zanyi."
yana kaiwa nan ya shige bayi bai jira jin amsar sa ba,
tun da ya shiga kuwa bai fitoba.
Dr Imran yasan sarai so yake ya tafi kafin ya fito.
ya lekashi ta jikin glass d'in kofar bayin,
ya hango sa kwance a cikin bathtub daya cika sa da ruwa.
idanunsa a lumshe.
kai ya girgiza ya juya ya fita dan yasan dama da kamar wuya yaje.
yaje ya had'u da sauran abokan nasu suka tafi gurin kamun........!






*Nima ina da biki yau da gobe da jibi sai kuyi hakuri bazaku ji ni ba sai an gama,
kafin nazo muje mu leka bikin Abdurrahim da amaryar sa Kuraiba*🤗



13
Ahankli ya bud'e idanun sa da suke a lumshe ya mike ya fice cikin bathtub d'in.
ya ja towel ya d'aura a kugun sa ya fito.
ya tako zuwa in da fridge ya ke ya d'au gorar ruwa mai sannyi ya bud'e ya kai bakin sa, ya kusa san rabin gorar sannan ya mayar da ragowar.
ya tako izuwa gaban wardrobe yabud'e ya ciro gajeren wando da singilet ya saka, ya isa gaban mirror ya feshe jikin sa da turaruka masa dad'i da sanyin kamshi kana ya fito parlour.

Ya haye kan doguwar kujera ya kwanta tare da d'aukar rimut ya sauya tasha izuwa MBC2.
Ajmal ne ya shigo da sauri had'e da sallama, ya karaso cikin parlour'n ya d'an rusuna tare da sosa bayan keyarsa
"Bar ka da dare brother."
da kai ya amsa shi
yana d'an kallon shi ganin kamar da magana a bakin shi.
Ajmal ya dad'a sosa bayan keyarsa yana fad'in
"Am Ya Abdurrahim dama so nake so ka d'an bani hula nawa sunyi datti sauran suna gurin wanki."
"Je ka d'auka."
yafad'a a takaice.
da sauri Ajmal ya ce
"Godiya nake bro."
ya wuce da sauri cikin bedroom d'in nasa ya zab'o hula cikin tarin hulunar sa yafiyo yana washe baki, da gwada hular a kansa,
har ya hango had'uwar da zaiyi da wannan tsadadden hular.
yana fita ya dad'a yi masa godiya bakinsa ya kasa rufuwa,
har ya isa bakin kofa zai fita ya kira sunan sa.
"Ajmal je ka karb'o min Sudan tea a gurin Aunty."
ya ce to.
da sauri ya fice yana duba agogo tara saura.
kuma karfe goma amarya Kuraiba ta ce masa za'a tashi a hall d'in, gashi sai kiran sa take yazo-yazo, dan tasan yayan nasa kam ba zuwa zaiyi ba,
so take shi d'in yazo ta b'adda kafa gun kawayen ta.

Da sauri ya shigo parlour'n Aunty d'auke da sallama a bakin sa.
Aunty na kichin ta fito tana amsa sallamar nasa.
"Aunty barka da dare."
"Yauwa barka dai Ajmal "
"Aunty wai inji Ya Abdurrahim wai ki basa Sudan tea,
amma dan Allah Aunty ki d'ansa wani ya kai masa, wlh sauri nake tun d'azu amarya take ta kira na, gashi ko wanka banyi ba bare na shirya."
Aunty ta ce to.
"Yauwa Aunty nagode." da sauri ya juya har ya kai kofa ya juyo
"Aunty dan Allah kar ace ban tsaya na karb'a ba, ace natafi ne zan dawo in karb'a da aka gama kuma aka kai masa kafin na dawo."
Aunty ta yi dariya.
shima dariyar ya yi kana yafita da sauri.
Aunty ta koma kichin da sauri, dan girkin Daddy take yi.

Nan da nan ta had'a masa Sudan tea ta zuba shi cikin Mug kana ta fito.
d'an jim tayi da tunanin wa zai kai masa, gashi Baba Rabi ta gama aikin ta ta koma b'angaren su na masu aiki.
kira ta kwad'awa Feeryal ta fito tana amsa kiran.
"Zo ki kaiwa Abdurrahim tea d'in nan yanzu ki dawo,
babu wanda zai kai masa, yi sauri girki na zai kone."
d'ankwalin material d'in kanta ta warware tayi mayafi da shi, kasan cewar yana da d'an girma, kana ta karb'i Mug d'in.
Aunty ta koma kichin tana cewa
"Kina kai masa ki dawo."
har ta nufi kofa ta tuna da abun da su Chuchu suka bata suka ce ta sa masa ya tab'a jikin sa.
ta juya cikin sand'a ta na kallon kofar kitchen gudun kada Aunty ta ganta.
ta shige d'aki ta isa in da ta aje ganyen da suka bata silli d'aya ta d'auka, har yanzu yana nan kore sharr d'in sa.
ta fito da sauri tayi waje.
magana taji a bayanta ta juya da sauri sai kuma ta saki murmushi.
ganin wad'an da suke bayan ta.
"Ai mun d'auka kin mance da abun ne, ashe kin tuna muje to mu rakaki."
suka soma tafiya tana cewa
"Na tuna ai ko na saka masa cikin tea d'in ne.'
"Aa kar ki sa a ciki jikin sa kawai muke so ya tab'a."
kai ta gyad'a dai-dai san da suke fitowa daga sashin Aunty.

Cikin gidan tamkar rana hasken wuta ta ko ina,
mutane ba'i 'yan biki suna ta zirga-zirga, bazakace dare bane.
a sannu suka isa bakin get d'in b'angaren nasa.
Chuchu da Chulu suka ce
"Anan zamu tsaya ki shiga muna jiran ki, kar ki bari ya gani kisan yadda zakiyi yad'an tab'a jikin sa kawai."
"Amma dai bazai duke ni ba ko?."
"Har yanzu tsoron sa kike ji ne?."
"Da ne yake bani tsoro da yawa amma yanzu ba sosai ba."
"Yauwa to ai gamu a nan kina sa masa zamu iso in da yake, bazamu bari ya yi miki ko mai ba."
"Kun tabbata dai ko?."
kai suka gyad'a mata.
ta tura karamar kofar ta shiga, tsayuwa tayi tana karewa side d'in nasa kallo,
wan da tun da take gidan bata tab'a shiga ba.
iyaka ta hangi get d'in da ido.

plat ne guda biyu a cikin side d'in gefe da gefe sai
Upstairs a tsakiyan su, amma kusan a had'e suke.
shima farfajiyar side d'in lungu da sako kamar rana ko ina hasken wuta wanda ko allurar ka ne ya fad'a kasa zaka ganshi.
tsayu tayi tana tunanin ta ina zata fara.
a hankali ta soma d'aga kafarta tana nufar sakiyan wato kofar parlour'n kasan Upstairs d'in in da take hango window sa a bud'e ga kuma iska na d'aga labulen window.

Tana isa bakin kofar ta gyara rukon tea d'in hannunta, kana tayi knocking d'in kofar.
tad'an tsaya kad'an kana ta kuma yi har sau uku a jere.
a hankali ta kai hannunta kan handle ta murd'a ga mamakin ta sai taga ya bud'e.
numfashi ta sauke a hankali a sannu ta zura kafarta ciki bakin ta d'auke da siriruwar salla.
wani sasanyan kamshi ne yabi hancinta.
ta shaki iskar tare da lumshe idanunta a lokaci guda ta bud'e.

Ido ta shiga rarrabawa cikin had'ad'd'e kuma rantsastsen parlour'n da tsaruwar sa ya kai tsaruwa.
can ta hango sa kwance da baya saman doguwar kujera, ya yi pillow da hannayen sa, idanunsa a kan TV.
a sannu tashiga d'aga kafafun tana takowa cikin parlour.
sanyi da kamshi suna dukan ilahirin jikin ta,
har sikar jikin na na tashi.
yana kwance bai motsaba tamkar bai san da shihowar mutum parlour'n ba.

Ta karaso ta tsaya d'an nesa da shi, cikin siririyar muryarta mai fita da yanayi shagwab'a ta ce
"Wai gashi inji Ammie na."
kamar bazai motsa ba bare ya yi magana, tsawon mintuna biyar tana tsaye, bai kalli in da take ba.
zuwa can ya zare hannunsa guda da yayi pillow da shi, ya yi mata alama da ta miko masa.
a sannu ta d'aga kafarta ta maso inda yake.
a hankali ta kai hannunta d'aya dake rike da ganyen nan ta had'a shi da jikin Mug d'in, ya zamana da ta rike Mug d'in da duka hannayen ta, kana ta miko masa.

Bai rike ba sai zaro d'aya hannunsa da yayi, ya rike Mug d'in da d'aya hannun d'ayan kuma bazato taji ya cafko hannunta mai rike da ganyen.
wani irin waro ido tayi, kirjinta ya buga rass,
ya aje tea'n saman table d'in gabansa,
batayi aune ba taji ya fisgota, ta fad'o kansa.
wani irin d'auke numfashi tayi tare da sakin kara.
hannunta mai ganyen ya kama ya dad'a dunkule shi ya matse da karfi.
kara ta kuma sakewa tana jujjuya fuskarta cikin kirjinsa, jikin ta na b'ari.
ya saki hannun nata tare da ware tafin hannun, ganyen da yake kore ya dawo jajazir, ya ciro shi cikin hannunta ya cusashi ta d'an bakin rigarta ta saman kafad'ar ta kana ya ture ta a jikin sa, ta fad'i tim a kasa.
da sauri ta mike tana wiki-wiki da ido, tare da yarfe hannunta da take jin sa kamar ba nata ba.
ta waiga gefe da gefen ta wayam babu su Chuchu da sukace zasuzo su taimake ta.
ya mai da hannayen sa ya dad'a yin pillow da su,
yana aika mata dugun kallo.
baya ta shiga yi kana
da sauri ta juya cikin sassarfa tana fita daga parlour'n ta jingina jikin garo tana mai da numfashin tsoro.

Sai kuma da sauri ta nufi get har tana had'awa da sassarfa.
a in da ta bar su Chuchu a nan ta same su.
fuska ta kwab'e kamar zatayi kuka.
"Ya dai Feeryal kin sa masa kuwa?."
suka had'a baki wajen tambayar ta.
narai-narai tayi da ido sai ga guntun hawaye ta d'ago hannunta daya matse shi tana jin sa kamar zai fita, ta ciro ganyen a hannun rigarta ta gefen kafad'ar ta.
da sauri Chulu ta karb'a tana fad'in
"Ya tabbata ke nan shugaba ya yi gaskiya koren yanye ya dawo ja."
a tare suka saki murmushi ita da Chulu.
cikin rashin fahimta take duban su suda zasu nuna damuwar su, ya b'ata musu shirin sai kuma taga suna murna.
murya na rawa ta ce
"Ya gani fa shine ya matse shi a cikin hannuna har sai da ya canza kala, kamar zai b'alla min hannu, shine ina baku zo ba."
Chuchu ta ce
"Wayo yake da shi ya yi saurin ankare wa ne da akwai abu a hannunki duk da baisan mene ne ba,
sai dai daya karanci idanun ki yaga d'aukar fansa cikin sa,
shi yasa ya miki haka,
amma kar ki damu shike nan yanzu dai tun da haka ne ya gane sai a canza tsari."
baki ta cuno ta ce
"Aa ni dai bazan sake ba karya min hannu zaiyi,
ni na barshi da Allah mugu kawai."

Har bakin kofar parlour'n Aunty suka rakata ita ta shiga,
su suka juya domin isar da sakon da suka gani.


Washegari ta karance ranar juma'a

Dubbanin d'arurruwan jama'a ne suka shaida d'aurin auren Abdurrahim da amaryar sa Kuraiba.
auren da ya had'a al'umma daban-daban na kasar nan da ma wajen kasar nan.
biki ya yi biki duk wan da ya ziyarci gidajen bikin nan sai ya jinjina irin bajindar da ake zubawa.
musamman gidan A.A FIYA.
nera takoka a wannan ranar.

Gaggarumin liyafa Mommy ta had'a a babban filin taro da ke cikin birnin Lagos,
inda ta gayyaci manya-manyan mawaka dan su kwankwaje basirar su dan nuna farincikin wannan aure.
da misalin karfe 8 na dare za'a fara gudanar da shagalin,
in da za aje a d'auko amarya awuce da ita can gurin liyafar,
idan aka gama gudanar da shagalin bikin a garzayo da ita gidan angonta.

'Yan uwa da abokan arziki anata shiri domin halartar filin taron.
su Mommy anata shiga da fita na kayayyaki masu tsadar gaske.
ko yanzu ma wani dokakken leshin da akayi mata odan sa daga can ketare ta saka, wan da dashi zata fantama a filin taron.

Umma Karima da kyar ta iya danne damuwar ta ta fito cikin mutane tana dariyar yake, itama ta saka kaya masu tsada, duk da kasan ranta bakin cikin zuwan wannan ranar take.
amma tayi imani da abin da bokan ta ya fad'a mata.
haka ta tausasa Siyama da kamar zatayi hauka sabar kishi, ta yi wanka ta fito.
Aunty ma tayi kwalliyar ta sosai duk wanda yagani sai ya yaba.

Tun da yamma masu kwalli da aka gayyace su suka zo.
suna ta cab'awa
kannen ango kwalliya, zuwa magriba kannen ango sun fita ras, kamar wanda za'aje gasar kyau.
ana isha'i motoci suka fara jidan mutane zuwa filin taro.
su Hajiyan Dubai da wasu 'yan'uwan su Daddy da suka zo daga Yelwan Shendam akayi da su gidan amarya idan suka d'auko ta su wuce da ita filin taron.

Dr Imran ne tsaye a kan sa, yana ta fama da shi ya tashi ya shirya su tafi,
antafi d'aukar amarya bai kamata ace amarya ta isa su basu isa ba, su yakamata su jira zuwan amarya.
ya ce bazaije ba idan yana da karfi yajashi ya kaishi.
ganin da gaske ba zaije ba, yafita yaje sashin Mommy ya sanar mata.
Mommy sun fito da kawayen ta zasu tafi, Imran yake sanar mata da abun da ya ke faruwa.
da kanta taje ta same shi,
ta ce har idan ita ta haife shi to ya tashi ya shirya,
tun bai had'u da mummunar b'acin ranta ba,
ita da tayi zaton ma har ya tafi yana tare da amaryar sa.
badun yaso ba ya tashi ya shirya cikin wasu kaya masu shegen kyau.
suka fito suka nufi filin taron da sauran abokan sa.


Ko da Miemie ta zo suje da Feeryal ai mata kwalliya,
Aunty ta ce ita bazataje gurin bikin ba, su tafi kawai.
Miemie kamar zatayi kuka tayi ta had'a Aunty Allah da annabi.
suna cikin haka Daddy ya shigo ya ce su tafi.
Miemie murna har da dariya
ta janyo Feeryal zuwa sashin Ammah bayan ta kira me kwalliya can.
Miemie sai mita take mata
"Ke wlh Feeryal gaba d'ayan ki sai a hankali,
ki duba kiga kowa ya yi kwalli tun d'azu nake ta kiran ki kizo amiki kikaki zuwa,
gashi har an fara tafi su Ameerah duk sun tafi,
da nima fa na tafi jiran ki nake tayi tun d'azu,
haba dan Allah."
"Ke Ammie na ne fa ta ce bazan je ba, dama ni ma ba wani son zuwa nake ba, ni wlh dama yanzu nayi bacci na, tun da ina off ba salla zanyi ba me zan zauna yi."
hararar ta Miemie tayi, ta ce wa me kwalliyar tayi mata da sauri dan Allah.

Simple makeup akayi mata a hakan ma da kyar ta tsaya dan cewa tayi ita bata so.
mai kwalliyar ta ce ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login