Showing 51001 words to 54000 words out of 63585 words

Chapter 18 - FEERYAL Part 2 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.txt

magana akan Daddy, yadda kike auren shi haka nima nake auren shi,
'ya'ya kuma wannan kin shiga hurumin Alla dan shi ya tsara hakan,
dan Allah Hajiya Karima ki barni naji da abin da ke dami na."
Aunty ta karasa maganar tana had'a hannayen ta biyu zuciyar ta na d'aci.
Mommy ta ce
"Mttss aikin banza sai arika nuna an fi kowa damuwa da Alhaji,
idan gurin magani ne ma ina ne za'a kai shi, a fidda shi makiya su ji dad'in samin galaba a kanshi."

Hajiya ta ce
"Eh to nima dai zuwan Baba Salehu na Yelwa kafin su koma yake min maganar ko za'a had'a dana gida ne, sai a gwada a gani baza'a fasa na asibitin bama."
Umma Karima tayi saurin cewa
"To idan ma za'a had'a dana gida mu bamu amince a d'auke shi a kaishi ko ina ba, sai dai a kira mai maganin yazo gida nan,
kuma mu zamu nemo mai maganin idan akayi ba'a dace ba sai ta nimo nata,
ko ba haka ba Hajiya Halima?."
Mommy ta ce
"Kwarai kuwa."
Hajiya ta ce
"To ai shike nan mudai sauki muke fata masa, sai ki kirashi mai maganin yazo gobe idan Allah ya kaimu,
idan baiyi ba ni da kaina zan d'auke shi mutafi Yelwan Shendam, abokin turawa yaje yana masa nasa jinyar ana kuma na gida,
ni wannan ciwo na Abubakar ma yana min kamar aljanu ne, amma dai mai maganin yazo dai mu gani."
kowa yarika tofa albarkacin bakinsa a gurin Aunty bata kuma cewa komai ba.
tana rayawa a ranta ita da kanta zataje ta karb'o masa magani tazo ta masa.
su Abdurrahim suna fita ta shiga.
batabar sashin ba sai kusan karfe 1 bayan tayi masa addu'o'i ta shafa masa.


Washegari Aunty tana idar da sallah taje ta duba Daddy,
tayi mamakin ganin sa har lokacin yana bacci.
Ajmaal ya ce mata ya tashi ya yi sallah yakuma komawa ne.
ta tofa masa addu'a kana ta koma sashin ta ta soma had'a masa gwaten acca, wanda shi ne yanzu yake d'an iya ci.

Wani irin zabura Feeryal dake bacci tayi.
da karfi ta ce
"Ammie kar ku barshi ya shigo gidan nan!."
Aunty da ta fito rike da basket mai d'auke da abincin Daddy ciki,
cikin hanzari ta shige bedroom d'inta.
akwance ta isketa idanunta a rufe da alamu dai bacci take.
Aunty ta juya tana kokarin fita.
taji an kuma fad'in
"Kar ku bari ya shigo gidan nan!."
da sauri Aunty ta juyo, jin wani irin murya ne ya yi maganar ba irin na Feeryal d'in ba.
ido Aunty ta waro ganin yadda jikinta ke jijjiga hatta gadon jijjiga yake, tamkar zai karye.
kafin tayi aure tayi wani irin
mikewa tsaye da kafafunta a kan gadon.
cikin wani irin hargitsastsen murya ta ce
"Kar ya shiga ya dakata a gurin!!."
tayi maganar tare da fasa wani irin kara mai firgitarwa.
da sai da gidan gaba d'aya ya d'auki amon sautin mai tarin tsoratarwa da rikitarwa.
kafin Aunty ta ankara har ta duro a gadon tayi waje a guje.
Aunty ta bi bayanta tana kira dan kayan bacci ne riga da wando a jikin ta.

Umma Karima da me maganin da ta kawo suna daf da shiga side d'in Daddy.
Feeryal kamar mai gudu kan walkiya ta iso gurin,
wani irin damka tayiwa rigar sakin da ke jikin sa ta baya, ta finciko shi kamkar kwali ta d'auka ta jefashi can ya fettu da jikin garu. ta saki wani irin. haniniyar ihu, tayi kansa ta mika hannu zata damko shi......!


Mommyn Twins ce




Da karfi aka rike hannayenta duka biyu ta baya, tayi wani irin ihu tare da kokarin fisgewa.
tana wani irin gurnani tana sunkoyowa kan boka Mali, ya yin da fuskarta ke rufe da gashin kanta.
Abdurrahim ya yi baya tare da kuma janyo hannayen ta daya rike duka biyu ta baya, har sai da bayan ta ya garu da kirjin sa.
da sauri boka Mali ya dafa jigin bango ya mike ya tattari kwaryar da ya toho da shi a hannunsa wanda sanadin feud'e shi da akayi jikin bango ya tarwatse.
yashiga tattara fasassun da sauri jikin sa na kyarma.
Feeryal na ihu tana tuma niman kwacewa a hannunsa tayi kan boka Mali.
ai yana gama kwashe fasassun kwaryar ya d'au sandarsa ya zura a guje.
Umma Karima ta bi bayansa tana kira tuni yafita a gidan da mugun gudu.
Aunty ta sa hannu a kai tana salati ganin yadda Feeryal take niman kwacewa a hannunsa.
tuni ya murd'eta ta zube kasa ya danneta.
kana ya shiga karanto wasu ayoyi daga cikin alkur'ani yana tufa mata.
Umma Karima ta dawo da sauri kamar hauka sabon kamu,
tana fad'in
"Gantalalliya asararriya kin fasa kwaryar hankalin ki ya kwanta."

A ciki kuwa Daddy na kan azabtuwa cikin bacci.
yau abubuwan da yake gani masu firgitarwa da ban tsoro sunfi na kullum.
wannan hasken da yake zuwa taimakon sa cikin bacci shi yakuma zuwa a yanzu ma, dai-dai sanda aka danna masa mashin wuta a kahon zuciya ana daf da burma masa.
wannan hasken ya bayyana.
hasken ya tarwatse halittun, da suke zagaye da Daddy suna azabtar da shi. kana hasken ya wuce.
daga can ya soma jin muryar da ke magana a duk san da hasken nan ya gifta.
"Kar ka bari tayi nesa da kai ka janyo hasken can cikin rayuwar ka, idan yau ka kub'uta gaba ba lallai ne ka kub'uta ba, tabbas za'aga bayan ka, kar ka bari ta yi nesa da kai ka janyo sa cikin rayuwar ka, ana daf da ganin bayan ka,
hasken kub'utar ka ce ka rike ta kar ta tsere daga rayuwar ka!!."
da karfi yake jijjiga daga d'aurin da akayi masa,
da igiyar wuta, dake shiga sokar jikin sa.
yana ta fafutukan niman ta inda zaiyi ya kunce ya juya yaga hasken kub'utar sa.


Su Mommy Hajiya da ihun Feeryal tun na farko kafin ta iso gurin ya fito da su daga sashin Daddy.
Mommy da jike ke rawa ganin tashin hankali a idon ta ta ce
"Wannan yarinyar ban yarda da ita ba, ke nan jinyar Alhajin ne bata so ayi, saketa ta tafi duk in da zataje Abdurrahim!."
Hajiya kuwa kirji ta buga ta ce
"Yau naga siddabaru to baza'a kawo min tashin bori cikin gidan d'ana ba, daina tofa mata addu'ar nan abokin turawa jata ka fita mana da ita anan."
Aunty ta maso da sauri hankali tashe ta ce
"Dan Allah Abdurrahim ka tai make ni ka kaimin ita side d'i na, dan Allah."
ta had'a hannayen ta biyu.
baiyi magana ba har ya kai karshen ayar da yaja.
ya d'ago yaga kaf 'yan gidan maza da mata idanunsu a kan su,
Zaraddin na ta gaba-gaba ya kafe ababen kirjinta tarr da ido.
wan da babu bra iya rigar baccin ce mai tsamtsi a jikin ta.
daga kasan rigar ma yad'an bud'e har kusa da cibiyarta, ana ha hango farin fatar shafaffen cikin ta.
da hannu ya yi musu alamun kowa ya watse.
Zaraddin yad'an sosa keya yawani lumshe ido tare da jan numfashi.
yana jin hannunsa na kaikayi ina ma ace yaje ya damki balambalon kirjinta.

"Daddy Daddy! innalillahi wa innailaihirraji'un Mommy Hajiya kushigo kuga yadda Daddy yake yi Ya Abdurrahimmmm!!.."
Ajmaal ya ke fad'i a gigice ganin yadda jikin Daddy'n ke jijjiga kamar wanda aka jona da wutan lantarki, ya had'a gumi daga kai har tafin kafafun sa.
Da karfi Daddy ya dafe kahon zuciyarsa har lokacin idanunsa a rufe ya kasa farkawa daga baccin da yake,
sai da hasken ya yi nesa da shi kafin ya juya izuwa halittar mutun, yana daf da b'acewa ganin sa sannan ya juyo garesa,
annuri shinfed'e a fuskarta tana murmushi kamar ko da yaushe a cikin rayuwarta.
tayi jifa da hannunta ya isa ga inda Daddy yake.
a take igiyar wutan dake tabaibaye da shi ya b'ab'b'alle ya zube kasa.
wani katon kasko yafashe ya tarwatse.
"FEERYAL!."
Daddy ya ambata cikin baccin amma sai da lab'b'ansa suka motsa.
Hajiya Mommy Aunty har suna rige-rigen shiga sashin Daddy jin kiran da Ajmaal ya ke.
Abdurrahim ya mike tsaye daga sunkuyon da yake rai b'ace.
ya fincikota ya mikar da ita tsaye, ya janyo ta tana tirjewa, ya yi da ita sashin Aunty.
yana zuwa bakin kofar parlour ya turata ciki.
ta zube kasa ta kuma yunkurin tashi.
rai b'ace yasa kafa cikin parlour'n tare da d'auke ta da mari ta kuma komawa tayi flat a kasa.
cikin kakkausar murya ya ce
"Idan kuka kuma fitar da ita da wad'an nan kayan na rantse sai na kashe ku!,
kar ku kawo wa mutane iskancin banza a gida."
jikinta ya sake gaba d'aya, ta ja numfashi mai d'an tsawo kana ta shiga sauke numfashi a hankali a hankali idanunta a lumshe,
sai kawai ta gyara kwanciya taci gaba da baccin ta.
tsaki yaja yana d'auke idanunsa a kanta.
ya juya har yakai bakin kofa sai ya kuma juyowa ya dawo.
hannun rigarsa ya gyara ya sunkuya ya sa hannu ya d'agota cak.
wani irin bugawa kirjinsa ya yi sanda yake had'a ta da jikin sa.
a hankali ya shiga d'aga kafarsa yana nufar bedroom d'in ta da ita.
ajiyan zuciya mai sauti ta sauke,
ta dad'a manna kanta a kirjin sa, tana kara lafewa cikin jikin sa.
hannun guda ta sakalo wuyan shi, d'aya hannun nata kuma ta tura ta bayanshi ta kankame rigarshi ta baya.
da d'an sauri ya kalli fuskarta bacci take da gaske.
yana isa bakin gado ya cirota a jikin sa ya wurgata kan gadon yana gyara zaman rigarshi
baki ta cuno har lau udanunta a lumshe.
cikin siririyar muryarta mai cike da bacci ta ce
"Ammie kaina ciwo."
sai kuma ta gyara kwanciya tayi d'ad'd'aya da kafafun ta, rigarta duk ya tattare ya koma sama gaba d'aya cikin ta yana waje.
da sauri ya yuya yafita yana mai dad'a jan tsaki.
ya janyo mata kofar.
acan wajen sakar gidan ya ga Miemie ya kirata ta karaso in da yake da sauri.
ya ce
"Je ki same ta tana."
yana fad'in haka ya juya ya nufi sashin Daddy.

Yana shiga d'akin Daddy ya ja ya tsaya daga bakin kofa yana kallon Daddy dake zaune, su Hajiya suna zagaye da shi, kowa bakin sa yakasa rufuwa.
Hajiya na ganin sa ta ce
"Kai abokin turawa kai ma mamaki kake na ganin sa zaune,
yana magana tiryan-tiryan kamar bashi ne ke kwance d'azu shame-shame rai a hannun Allah ba,
har waje na fita duba ka kazo kaga halin da yake ciki amma ban ganka ba,
uban ka yana nan a kwance kai katafi taran aljanu 'yar da ta so kashe mai magani,
ina zaka iya da ita,
irin wannan jifa da tayi da shi Allah kad'ai yasan a wani hali yake ciki yanzu."
Mommy ta harare shi tare da yin kwafa wato bazaiji ya daina taimakon aljanar nan ba.
ya karaso yana cewa
"Ya jiki Daddy."
ya ce "Alhamdulillah Abdurrahim kamar an zare min ciwon haka naji, kirjin ne dai ke min zafi har yanzu."
"Insha'allahu shima zai daina."
bai bar d'akin ba sai da ya bashi wasu allurai da magunguna.

Umma Karima ta rasa ina zata sa kanta, tarika dibi-dibi tayi nan tayi can daga karshe tasa direban ta ya jata zuwa dajin Mali.
tana shiga kogon boka Mali ta ganshi zaune yana ta aikin zuba tsafe-tsafe da surkullensa.
ya d'ago da jajayen manyan idanunsa masu muni cikin murya maraddad'i ya ke fad'in
"Wace ce ita da muka kasa ganin ta a zahiri kamar yadda muke ganin duk wanda muka kira shi cikin wannan kwaryar!?
akwai wani abu a tare da ita mene ne shi,
mene ne shi na kasa ganin shi!!."

Umma Karima ta zabura ta zube gaban sa tana fad'in
"Boka a gafarce ni, wannan yarinyar ta zame min karfen kafa na rasa ta in da zanbi na yakace ta a wannan gida,
duk wani makircin da zan gina mata sai ta sallaka,
yau ana daf da idda cin nasara tafi to tana shirin lalata nasarar,
yanzu haka boka nasashi ya tattaro duka takardun kadarorinshi,
yau nake shirin sashi ya juya sunan ya dawo nawa, da zaran ka bashi maganin cikin kwaryar nan,
shine shegiyar yarinyar nan ta fasa kwaryar,
boka a taimaka a kuma d'aukar wata kwaryar muje a bashi maganin."
boka Mali ya kece da dariya
"Hahahaha kin rigada kin tafka asara, aiki ya wargaje, je ki leka cikin tukunyar tsafi ki gani."
jiki na b'ari Umma Karima ta mike ta je ta leka tukunyar tsafin.
kirji ta buga ta waro ido cikin tukunyar, da kullum ke tafasa yau babu ko alamar d'igon abu a ciki, hasali ma tukunyar a bushe take kamas kamar tun da yake ba a ta ba'a amfani da shi ba.
ta juyo gareshi hankali a mugun ta she ta ce
"Boka babu komai cikin tukunyar ina abun ciki suke?."
"Hahahaha a gidan ki kwarya ta fashe fashewar kwarya kuma yana dai-dai da rasa abun da suke cikin tukunya,
shi kansa tukunyar a fashe yake kece bazaki gani ba,
do le sai kin kuma samo wasu a had'e guri guda masu kwari a saka cikin tukunyar, kafi aikin ki ya farfad'o a ci gaba."
jikin Umma Karima ya tsanan ta rawa murya a daburce ta ke fad'in
"Boka kasan da ya na samo wannan na karshen, shekara nawa nayi ina nema kafin na samu,
daya na samo wannan d'in ma, wannan tsinanniyar yarinyar tayi ajalin abin da na jima ina nima wlh bazan kyale ta ba,
yadda ta rushe min mafarkina sai na hanata ko da dai-dai da rumtsawa ne,
yanzu boka ai ki ya tsaya ke nan?."
"Ai ki ya tsaya da alamun faruwar wani lamari, ki gaggauta nimo lakanin ki a sake gina miki aikin ki."
Umma Karima ta mike a haukace tayi waje tana tsinewa Feeryal..


A b'angaren Dad ba karamin girgiza ya yi da ganin Daddy ya farfado ya dawo hayyacin sa ba.
shi da yake ta kan shirin yadda zaiyi ya kwashi dukiyar sa duka, ya barshi cikin latauci da jinya.
ya ciza yatsa yana buga teburin gaban sa.
"Ban so haka ba amma zamu had'u next time ni zanyi nasara, sai ka d'and'ana bakin cikin da kuka jefani ciki kai da mahaifiyar ku, sai na fanshi dukiyan mahaifina da aka yi rufarufa akace duk mallakin ka ne,
daga karshe na fanshe ran mahaifiyata da taku mahaifiyar."
ya mike ya rufe office d'in sa ya nufo gida.

Gaba d'aya gidan tun daga kan 'yan gida da ma'aikatan gidan kowa murnar samin saukin Daddy ake.
in a ka cire Umma Karima da Dad Mom.
farincikin da Aunty ta ke ciki bazai fad'u ba.
tana nan a nanike da shi.

Kwana uku da farfad'o war Daddy yana zaune a bedroom d'in sa,
gaba d'aya ya nisa cikin tunani tun ranar da ya dawo hayyacin sa, yake ta tunanin mafarke-mafarken da yarikayi abun da yafi tsayuwa masa arai shine hasken da yake zuwa ceton sa.
da maganar da ake masa kan hasken.
da kuma fuskar da ya gani daga karshe,
abun da ya d'au re masa kai.
me yasa ake cewa karya bari ta tsere daga raguwar sa, ta zauna cikin rayuwar sa.
bayan a cikin gidan sa take tamkar d'iyar da ya haifa,
yakan mance da ba shine ya haife ta ba har sai in magoratan gidan sa sun goranta.
wani irin kusanci ne ake nufi daya yawuce wannan,
gashi ana gaya masa zai kuma shiga wani tarkon nan gaba, idan baiyi gaggawar kusanto ta cikin rayuwar sa ba.
sosai kwakwalwarsa ta hargitse da tunani ire-ire.......!





Mommyn Twins ce




25
Umma Karima zaune a parkour'n ta ita da iyalan ta,
abin duniya duk ya taru ya dame ta.
shike nan duk bojet d'in ta ya rushe da yanzu ba wannan maganar akeba, da yanzu bata ma kasar ta milla wata kasar.
tsaki ta ja akararo na sau ba adadi.
Nabila dake danne-danne a wayarta ta d'ago tana fad'in
"Kai wai dama wannan duk gidajen Daddy ne da suke Abuja, ai da ya rasu ni cikin wad'an nan gidagen za'a bani da suke Abujan nan."
Bilkisu Saddiqa Rahma suka d'ago a tare Bilkisu ta ce
"Amma Nabila baki da hankali Nabila yanzu har tunanin Daddy ya mutu dan ki sami gidaje kike,
duk cikin mu babu wan da ya tab'a wannan tunanin sai ke
ai ki gansa a raye yafi miki wad'an nan gidajen."
Nabila ta mike ta nufi bedroom d'in su tana fad'in
"Mutuwa ai wajibi komai daran dad'ewa ai dama zai mutu."
"To sai ki bari lokacin nasa ya yi tukun."
cewar Saddiqa.
Umma Karima ta ce
"Kai dalla ku rabu da ita haka, in da ku d'in ne ma hakan zakuyi idan ya mutu sai kunji kuna son wasu gidajen fiye da wasu,
haba dan Allah ku barni naji da abin da ke damu na."
Rahma ta ce
"Umma ai dai bai mutun ba tukun meye na maganar nata, Umma wai me ke damin ki ne kam?."
Umma Karima ta girgiza kai kawai tana jin kamar ta mutu dan bakinciki.
Siyama ta fito tana gyara mayafi ta dubi Umma Karima tana fad'in
"To Aunty Karima ni bari na fita nayi bako a waje."
Umma Karima ta d'ago ta kalleta sama da kasa wasu d'amammun kaya ne a jikin ta.
ta ce
"Wai ni wane ne kika samu ne me zuwa babu dare babu ranar nan, kuma ya d'auke ki kuna fita?."
fuska ta yamutsa ta ce
"Kawai hirar rage zafi ne kafin wancan ya shigo hanu,
d'an fita zamuyi yanzu zamu dawo."
Umma Karima ta juya kai bata kuma cewa komai ba tacigaba da tunane-tunanen niman mafitan ta...


Aunty ce zaune cikin bedroom d'in ta rike da waya a kunnen suna magana da Hajja Umma.
daga cikin wayar Hajja Umma ta ke fad'in
"Ikon Allah kuma tana bacci tasan wani mai magani ya shigo gidan, kinsan masu jinnu irin haka a kusa basa son marasa gaskiya,
gidan nan naku akwai wani abu ke dai kar ki yada addu'a babu abin da ya fi karfin Allah,
amma yanzu ya jikin Alhajin babu komai dai ko."
"Jikin sa da sauki sosai mafarkan ma duk ya daina, sai dai kirjin da yaje kukan sa dama shi tuntuni Abdurrahim ya d'aura shi a kan magani."
"To Allah ubangiji ya dad'a yaye masa,
dama Abban ku najiran yasa mi lafiya ne,
ya same shi da batun wannan yaro Sadam iyayen sa sun zo nima masa auren Feeryal ya ce sujira yasami uban ta idan sukayi magana ya amince sai ya turo su nan Lagas d'in,
to yaron wai shi a sonshi a had'a auren shi da abokin sa Nasir,
Abban ku ya fad'a musu yanzu zata fara karatu matsalar da aka samu da 'yan tawagar d'aukar amaryar nan ne ya tsaida batun tafiya makarantar ta,
sun ce babu damuwa idan akayi auren sai ta cigaba da karatun ta,
sau biyu fa suna zuwa, ban da shi yaron da yazo yafi a kirga."
Aunty ta ce
"Hajja Umma da wurwuri haka bikin Maryam da saura wata d'aya, a dai bari idan aka yi natan sai ayi na Feeryal d'in daga baya,
ni nafi so Feeryal ta kara girma tafi haka kafin tayi aure."
Hajja Umma ta ce
"Fatima a wannan hali da ake ciki na ko da yaushe samari suna kawo mata hari dan ma Allah yana ketar da ita, ai a aurar da ita

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login