Showing 24001 words to 27000 words out of 63585 words
Chapter 9 - FEERYAL Part 2 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.txt
annoba wayyo Allah mun shiga uku zata kashe 'yar gida, wayyo jama'a ku kawo mana d'auki za'ayi kisa."
Umma Karima da rahoto ya kaimata ta iso yanzu take fad'a.
ta ci gaba da fad'in
"Ku harbeta da bindiga idan bata sake ta ba, kuna gani zata kashe ta, dalla ku kashe mara amfani."
sai kuma ta juya da gudu tayi sashin Daddy tana ihu.
Ta fad'o cikin parlour'n Daddy tana fad'in
"To Alhaji gashi can za'ayi kisa a cikin gidan ka,
ka aje gamasheka ta bunkasa tafara cire wuyan 'yan gida,
ga mayyar Aljanar 'yarnan can ta makure wuyan Ameerah har jini na fita, ko numfashi bata yi wata kila ma ta mutu yanzu,
wani irin bala'i ne wannan ka ajiye mana a cikin gida."
Daddy ya dubi Umma Karima da take haki d'ankwalin ta a hanu ya girgiza kai,
kana ya gyaza zamansa ya d'aga kafarsa d'aya ya d'aura kan d'aya sannan ya dubi, Abdurrahim dake zaune a gefen sa kasan Carpet ya ce
"Abdurrahim je ka suna fad'a ka rabasu."
"Alhaji ka taso kaje ka ganewa idon ka kasheta fa zatayi."
Daddy ya d'au tsiririn gilashin sa ya saka sannan ya d'au jarida ya bud'e yakuma gyara zamansa yasoma karantawa.
Abdurrahim ya mike ya nufi waje domin isar da umurnin da Daddy ya basa.
Umma Karima ta bi bayan sa da gudu tana cewa
"Yauwa Abdurrahim yi sauri kafin ta kashe ta tun da shi ya ki zuwa bare ya d'au mataki, gata can zata kashe maka kanwa 'yar autarku, mayya ce fa taki sakin ta."
bai kula ta ba yaci gaba da tafiyar sa.
Mommy na baje a kasa tana kururuwa ta kasa ta shi.
Hajiya ta fito kafa ba takalmi,
tana ganin hanun Feeryal a wuyan Ameerah tasa hanu a ka ta kawo ihu ta saka,
"Wayyo Allah zata kashe min jika,
me kuka tsaya yi baku nemo itace kun buga ma 'yar banza ba, ku d'auko itace ku jinke ta da shi,
kuna gani zata kashe ta, wayyo Allah na shiga uku zata kashe min jika."
Hajiya tayi kan Feeryal da duka tana jan rigarta.
"Sake ta bazaki kashe min ita ba gayyan tsiya yau zaman ki ya kare a gidan nan."
bata rufa baki ba ta jita a kasa bip ta ture ta.
Hajiya ta yi kururuwa tana cewa
"Ni Abukabar zai kawo abin da zata kashe ni da jokikina a gidan nan."
Aunty ko hannu bibbiyu ta had'a tana roko da magiya had'i salati.
security kuwa suna ta kokuwan b'anb'are hannun Feeryal a wuyan Ameerah da jikin ta ke b'ari numfashinta na sama-sama.
babu makogoron yin ihu.
Suna ganin sa suka sake ta suna cewa
"Sir akwai matsala fa, ina ga sai an kira liman ya mata rokiyya, mun kasa cire hannunta a wuyanta."
"Abokin turawa ku had'u ku jata ku fidda ita a gidan nan, ku kai ta can cikin ruwa ya tabbata wannan 'ya ba mutum bace,
ina zan iya da gayyar tsiya, bazata kashe ni ta kashe min jikoki ba."
fuska ya dad'a murtukewa tare da gyara tsayuwarsa ya saka hannunsa a kafad'arta ta baya ya fizgota, ya fincikota ta da karfi tayi tangal-tangal ta zube kasa.
Ameerah ma ta fad'i kasa tare da sakin wahallen kara tana dafe wuyanta.
Feeryal tayi wani irin mikewa tare da calla kara tayi kan Ameerah dake kasa tana rike da wuyan ta,
Aunty tayi saurin shiga sakanin su tana fad'in
"Haba ku kuwa bakusan girman Allah da manzon sa bane,
me yasa kuke irin haka."
tuni ta kauce ta gefen Aunty
ta mika hanu tana kokarin kuma shako Ameerah, ya sa mata kafa ta fad'i kasa rip.
ta kuma calla kara ta shiga birgima a kasa tana bige-bige, can kuma ta mike flat gaba d'aya jikin ta ya sake, tashiga mai da numfashi.
Aunty ta yi kanta tana jijjigata da kiran sunan ta.
Da sauri Hajiya tayi kan Ameerah ta rungumo ta tana duba wuyan nata
Mommy ma ta zo ta rungume ta na dudduba jikin ta.
Hajiya ta ce
"Sannu kinji Ameerah Allah ya isa miki sai ta bar gidan nan taje can ta karata, haka kawai so take ta kashe ki kina zaman zaman ki tazo ta same ki ta shakure miki makogoro anya ma ba turo ta akayi ba,
dan ta had'a kai da 'yan ta'adda dama,
to wlh ba a gidan nan ba,
ina ji ina gani bazata kashe min jika ba,
ke Fatima d'auki tsiyar ki kisan yadda dare ya yi muku."
Miemie da tun d'azu take hawaye da sauri ta ce
"Hajiya wlh ba laifin Feeryal ba ce, zamu tafi gyaran gashi ne Ameerah ta tsare mu tarika zagin ta, takuma d'auki kyanwa ta jefa mata a jiki,
kuma tana tsoron mage."
Abdurrahim ya yi tsaki ya juya ya bar gurin.
Mommy ta ce
"To ai dole taji tsoron mage tun da ba gaskiya a lamarin ta, bazan zuba ido a cutar min da 'ya ba sai na d'auki mataki."
"Matakin ke nan yanzu-yanzu ta bar gidan nan."
cewar Umma Karima.
Hajiya ta ce
"Ai dama kam zama ya kare mata a gidan nan dan gobe bamusan wa zata kuma cirewa makogwaro ba,
kuje ku kira min Abubakar, sannu kinji 'yar nan tashi muje zai zo ya same ni."
Hajiya ta d'ago Ameerah da bakin nan nata ya mutu murus, suka tafi sashin ta.
Mommy ma ta koma nata shashin bayan ta gama zazzage bala'i.
Umma Karima ta juya kan Aunty dake ta kokarin ganin Feeryal ta dawo hayyacin ta.
tana ta aika mata habaici.
bata ma san tana yi ba burin ta d'iyarta ta dawo hayyacinta, tana ta tofa mata addu'o'i.
zuwa can ta dawo gayyacin ta,
da taimakon Baba Rabi suka tallafe ta suka tafi da ita side d'in Aunty.
Dole Daddy ya je kiran da Hajiya take ta ai ka masa.
ta in da take shiga batanan take fita ba,
dole Feeryal ta bar gidan.
Daddy ya ce
"Hajiya ai ba laifin yarinyar ba ne idan kika duba Ameerah ita ce me laifi, yau duk Miemie ta fad'a min irin tsokanar da Ameerah take mata kuma bata tab'a ramawa ba,
kuma yau d'in ma ai ba ita ce ta rama ba mutanen kanta ne suka tashi, sakamakon abin da bata so take tsoron sa ta jefa mata mage a jiki,
Hajiya duk ki bar maganar nan sab'ani ne kawai irin na yara, idan aka fiye magana irin haka sai na rikajin ciwo na kamar zai tashi,
yarinyar da ta kusan tafiya ma."
Hajiya ta walalo ido
Daddy ya yi maganar da bata son ji game da lafiyar sa.
"To to ai shike nan amma irin wannan shaka da tayi mata kamar zata kasheta, in yazo da sautsayi ai sai ya tafi da rai,
amma Abubaka kana ma shan maganin ka kuwa,
Kulu kira min Ajimi yaje ya kira min abokin turawa,
yazo ya duba ka imma zai baka wani maganin ne du yazo ya baka, ai yazo da sauki ma tun da yana gidan."
"Hajiya ba damuwa zan je na same shi dan naji kirjin na min zafi."
"Yi maza hanzarta kaje ka same shi, ina amfanin tara mutane a gida hankali na tashi in kaga yaya kaje can Yelwa ka huta ka bar musu gidan."
Daddy ya yi waje.
Hajiya ta dubi Ameerah tana cewa
"Ungo karb'i ki sha ruwan sanyin nan, zakiji wuyan naki ya yi sanyi, ai takusa ta tattari tsiyarta ta tafi kowa ma ya huta."
Ameerah ta karb'i ruwa ta shanye tana maida numfashi.
"Jeki kiyi wanka ki rire wad'annan kayan da sukayi kuran ki sauya wasu,
zan sa abokin turawa ya baki magani."
Ameerah ta mike bakin nan mud'us ta koma sashin su.
Ameerah na zaune a parlour kusa da Mommy tana cin abinci bayan tayi wanka, Ajmal ya shigo ya dube ta yana zama kan kujera ya ce
"Ke Ameerah wai kije in ji Ya Abdurrahim."
baki ta turo sannan ta aje plt d'in abincin ta mike ta fita.
A parlour'n shi ta iske shi zaune ya d'aura kafa kan d'aya.
Laptop na kan cinyarsa yana latsawa.
d'an nesa da shi ta tsaya ta ce
"Gani Ya Abdurrahim."
"Zo nan."
ya fad'a yana nuna gabansa tare da sauke kafafunsa kasa ya aje Laptop d'in saman table, ya gyara zaman sa.
Ameerah ta ja kafa tazo gaban sa, tana waige-waigen ganin ko akwai wanda zai ceceta kusa dan tasan babu tuntub'i sai ta sha dukan da bata san laifin ta ba.
a gaban sa ta sunkuya tana wiki-wiki da ido.
ya d'au belt a gefen sa, tana kokarin gudu ya janyo ta sai da ya yi mata bulala goma kafin ya sake ta,
yana cewa
"Idan kika kuma sa ta sake d'aga mana aljanu a gida, ta tara mana jama'a sai na d'aye miki fata,
Stupid Get out."
Ameerah ta mike da gudu tayi waje tana kuka.
Da kuka ta fad'o parlour'n Mommy da sauri Mommy ta mike tana fad'in
"Kuma tare ki tayi zata kashe ki?."
cikin muryar kuka ta ce
"Ya Abdurrahim ne ya bige ni."
"A wani dalilin laifin me kikayi tun baki dawo daga jinyar da aka d'aura miki d'azu ba."
"Ai tasan laifin ta shegen niman magana ne da yarinyar nan, ina ruwan ta da Feeryal me ta tsare mata a gidan nan,
kullum ke kenan niman tsokana,
ai da fasa miki jiki ya yi sosai ta in da gobe bazaki sake niman wata yarinya da tsokana a gidan nan ba."
cewar Ajmal yana hararar ta.
Mommy ta rike hab'a ta bud'e baki
"Au dama akan ta ne yamiki wannan dukan, bayan kashe ki da ta so yi."
"To Mommy ko ma me ai ita ta jawo."
"To shanyayye ai dama kai da shi kamar wa Hajiya Fatima na haifa mata, duk ta lashe ku ta barbad'a muku magani cikin abinci."
Ajmal ya mike ya fita yana hararar Ameerah........!
12
Tun daga ranar Aunty ta hana Feeryal fita ko nan da can, ko da Miemie ta zo sai dai su karaci hirar su a nan ta tafi.
jin guri shiru hajiya bata kuma cewa ko mai ba, hankalin Aunty yafara kwanciya.
Tuni shirin biki ke dad'a matsowa, uwar ango Mommy da uwar amarya, Hajiya Luba ba zama, ana ta shirin yadda biki zai tafi ta yanda baza a ji kunya gun kawaye ba.
tuni gidan Alhaji Abubakar A.A FIYA yafa d'aukar baki 'yan biki dangi na nesa da na kusa.
Su Hajiyan Dubai da 'ya'yan ta Umaima da Unaisa, suma sun hallaro.
Kamar yadda Mommy ta fad'a satin aure za'a kai lefe,
aure na da sati guda ke nan su Hajiyan Dubai da wasu dangin Mommy da Daddy da kawayen Mommy suka kai lefe gidan amarya.
abun da ya yi mugun tadawa Siyama hankali ganin irin tulin
kayan da aka kaiwa Kuraiba.
a haukace ta shigo d'akin Umma Karima, Umma Karima tana zaune tana waya da bokan ta.
Siyama ta shiga kai kawo cikin d'akin ta kasa zama.
"Boka a maganar da nake maka saura sati d'aya fa bikin nan,
sai yaushe ne za'a wargaza auren aure saura kwana kad'an.
boka ka taimake ni kar kabari ayi auren nan."
"Maganar waya bazata yi ba kizo kiji binciken kaddarar ki."
"To to gani zuwa ni dai buri na naji daddad'an kaddadar bincike, dan Allah boka a zurfafa bincike, sai nazo."
Umma Karima ta sauke waya ta dubi Siyama tana fad'in
"Akan ido na aka fita da kayan nan bakin ciki ya hanani fita, ta turo nazo muje kai kaya nace ace mata yau na tashi da ciwon kai,
boka ya ce nazo ya yi bincike ya gano wani abu, zan je naji dan nasan bazai bamu kunya ba."
"Aunty Karima kin ga kayan kuwa ashe Hajiyan Dubai ta kuma zuwa da wasu, cikin mota uku fa aka tafi da shi, ban da wan da suka saka a sauran motocin da suka tafi."
"Ke duk wannan ba wani abu bane in zamu sami abun da muke so nawa ne wannan kayan da bai wuce kud'in shan shayi ba,
ki natsu cip zan je naji me boka zai ce."
Umma Karima ta mike ta zari mayafi ta fita.
Umma Karima zaune gaban boka Mali ba mayafi ba d'ankwali ba takalmi ta nad'e kafa kamar mai niman gafara.
boka Mali ya d'ago ya dube ta bayan yagama zane-zane da buga kasa ya ce
"Akwai yuwuwar yin auren nan babu yadda za'ayi dole sai anyi sa,
idan kuma aka matsa wajen hana yiwuwar sa to wasu aiyukan zasu iya rushewa, musamman aikin cikin tukunyar can shima zai iya tarwatsewa."
ta girgiza kai da sauri
"A'a boka bana son aikin can ya rushe zan iya hakura ayi auren, amma bazan iya jure rashin wancan aikin ba."
"Hahahaha kinyi nazari mai zurfi."
ta mike tana fad'in
"Yanzu boka babu wani d'an taimakon da za'a iya yimin,
amma dan Allah kar ya tab'a aikin can."
"Bazamu iya yin komai ba yanzu ki bari ayi auren."
"Nagode ubanmu maganin kukan mu idan ina bukatar wata taimako zan dawo dan kai ne kad'ai mai iya share min hawaye,
duk abin da na nima na samu in kana numfashi Allah ya kara tsoron rai."
Ta fice daga cikin kogon inda ko da yaushe take tub'e mayafi da d'ankwali da takalmin ta ta isa,
ta d'auka ta saka kana ta karasa gurin mota in da direban ta ke zaune cikin mota yana zaman jiranta.
ta bud'e gefen mai zaman banza ta shiga ta zauna sharap.
Liti direba ya dube ta yana fad'in
"Ina muka dosa hajjaju?."
gajeren tsaki ta ja ta ce
"Mu tafi hotel gaba d'aya yau raina a b'ace yake."
"An gama ranki shidad'e."
yaja motar suka nufi in da ta umurcesa..
"Feeryal yi sauri dan Allah mu tafi, idan fa bamu je mun zaunawa telan nan bafa ba bazai mana d'inki kan lokaci ba."
"Miemie wai dole kuma sai munje bayace zai kawo da kansa ba, mu jira mugani ko zaikawo anjima."
"Ke baki san halin teloli ba ne,
ba ga su Sahla sunje sun amso nasu jiya ba, kuma ai duk tare ya ce zai kawo mana, me yasa bai kawo mana ko ya basu su kawo mana ba,
muje kawai mu amso muma."
Feeryal ta mike tana gyara gyalen abayar jikin ta, ta saka takalmi mara tudu suka fito.
A can jikin get d'in side d'in Hajiya suka hangi Hajiyan Dubai da su Unaisa.
Miemie ta ce
"Taho muje Feeryal ga Hajiyan Dubai can yanzu sai tace mun ganta bamu zo mun gaishe ta ba, shegen son a gaishe ta matarnan ko me gaisuwar yake badawa oho mata."
Tun kafin su karaso Hajiyan Dubai ke bin Feeryal da kallo har suka karaso.
a tare suka had'a baki wajen gaishe ta ta amsa tana dad'a karewa Feeryal kallo
"Lafiya lau sannun ku."
har sun juya zasu tafi Hajiyan Dubai ta ce
"Ke Miemie a ina kika samo wannan, ko cikin ba'in Lebanon ne da suka iso."
"A'a Feeryal ce yarinyar Aunty."
"Wacce Aunty wai Hajiya Fatima, Aunty naku yaushe ne ta haihu bamu sani ba,
au kar dai ace 'yar da ta tsinto d'in nan ce."
Umaima da Unaisa da suke jingine jikin mota dukansu rike da waya suna latsawa,
da alama fita zasuyi da uwar tasu,
sai a lokacin suka d'ago suka kalli Feeryal.
Unaisa ta d'an yi murmushi
"Miemie sannun ki."
Miemie ma guntun murmushin tayi mata.
dan tasan halin su ko wannen su d'an ji da kai ne suna ganin sun fi kowa, suna rayuwa a Dubai.
ta ce "Sannun ku kuma Feeryal muje ko."
cewar Miemie tana jan hanun ta.
"Yanzu ke Miemie baki jin kishin kanki, kina yawo da wacce ta fiki,
taya za'ayi saurayi ya ganki ya ganta ya d'auke ki a kanta,
ni sam bana son yarinyar data fiye kyau haka tana huld'a da 'ya'ya na,
ita uwar taki ma bata san me take yi ba da ta zuba miki ido ta barki kuna yawo tare da ita."
Miemie bata ce kala ba ta ja Feeryal sukayi gaba, tamkar basuji me take fad'a ba.
Acikin mota ne Miemie ta dubi Feeryal da jikin ta ya d'an sanyi.
ta ce
"Hm matar nan fa duk bakin ciki ne ya dame ta, dan taga saura kad'an Ya Abdurrahim ya yi aure,
ai da ta so had'a shi da Umaima shi yaki."
Hmm kawai feeryal ta ce tana juya lamarin cikin ranta.
Ko da sukaje suka samu telen ya gama d'in kin su,
babban shago ne da ma'aikata da yawa,
har zasu tafi d'aya daga cikin telolon ya ce musu ga sauran kayan Ameerah su tafi mata da shi.
Miemie ta ce bazasu karb'a ba tazo da kanta ta karb'a,
ai suma da suka zo suka karb'i sauran kayan su basu karb'a musu nasu da aka gama ba.
Feeryal ce ta karb'i kayan suka nufo gida Miemie na ta mita.
"Yarinyar da ba a yi mata gwanin ta ba burgeta zakiyi ba."
"Nima ba so nake na burge ta ba, kawai taimako nayi yiyyar yi mata."
Miemie ta yamutsa fuska.
Suna isa gida Miemie ta dubi Feeryal tana cewa
"To ai sai ki kai mata tun da wulakanci bai ishe ki ba dan ni dai bazan kai ba."
"Ni ma ba zuwa zanyi ba zan dai baiwa masu aiki su kai mata."
tana rufa baki suka hango ta ita da su Unaisa da Umaima Sahla Nabila Sumayya, sun fito daga sashin Hajiya.
"Muje daga nan ki mika mata mu wuce."
suna zuwa sashin Mommy su suna tafiya sashin Aunty a tsakiya suka had'e.
Sumayya ta ce
"Yauwa Miemie Hajiya ta na niman ki."
"To daga gun d'inki nake sai na je na ajiye kayana kafin naje, me zata min ma tukun."
Sahla ta ce
"Ina zamu sani mu, yauwa ya gama miki d'inkin duka kuwa?
mu ma can zamuje mu amso sauran kayan Ameerah."
"Ya gama duka har da na Feeryal, d'in ki ya zuba kyau sai kowa ya saka a tantance,
Feeryal mika mata kayan ta, gashi nan ta karb'a mata."
laidar kayan Feeryal ta mikawa Ameerah da tayi gum da bakin ta kowa yana magana ita bakin ta a suke kamar ruwa ya shanye ta.
sai cika da basewar da take ita fa a dole boss ce a cikin su.
ta amshi laidar har lau bata ce kala ba ta soma tafiya.
Unaisa ta dubi Feeryal ba yabo ba fallasa ta ce
"Feeryal sunan ko ba laifi kam akwai kyau."
takaotaccen murmushi tayi mata.
Nabila ta ce
"Mujen ku dan Allah."
suka bi bayan Ameerah suka nufi sashin Mommy.
Miemie ta juya tana kallon bayan su, dariya ta tuntsure da shi tana cewa
"D'an iska na kauye sai tsoron d'an'sanda, dubi Ameerah yadda ta nutsu,
karyar iskanci take,
duk shan kwayar ka ai akwai wanda ya d'are ka,
gargad'in ya shige ta ke nan."
Feeryal ta bita da ido dan bata fahimci abin da take nufi ba..
Ana saura kwana uku biki Farida da mijin ta suka duro Nigeria da baby girl d'in su mai suna Neezrah.
sun kuma dawo akan dai-dai kab'ar da mijin nata ya kammala aikin da ya ajiye shi a Uk.
gida ya cika makil da 'yan'uwa da abokan arziki.
in da tuni sabbin ma'aikatan da Mommy ta d'ibo damin bikin suka had'e dana gidan suka cigaba da d'aura manyan tukwane suna sauke wa.
Dr Imran ne ya shigo bedroom d'in Abdurrahim cikin shigar sabbin kaya masu kyau.
tsayuwa ya yi cikin d'akin yana binsa da kallon mamaki ganin sa kwance, yana baccin sa cikin