Showing 42001 words to 45000 words out of 63585 words

Chapter 15 - FEERYAL Part 2 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.txt

bubbuga kafa kasa
"Ammie duka wardrobe d'in fa babu."
"Ai shine nace ni zan nimo, tun da sun b'ata miki ni zan samo su."
tabi Ammie'n nata da sauri suka shige d'akin tana dariya da fad'in
"Ammie numfashi fa yake hanani."
"Ni dai a barni na nimo kawai tun da b'ata sukayi."
cewar Aunty

Aunty ta bud'e wardrobe ta rike baki tana kallon side d'in bra, tari guda har da sabbin da bata tab'a sawa ba.
ta ciro mata d'aya ta ce
"Gashi na samo miki daga in da suka b'atan,
maza karb'a ki saka."
ta na kokarin rufe wardrobe d'in ta hango laida, ta zaro shi tana cewa
"Mene ne acikin nan ko har laida aka nemo na b'oye su ciki."
ta yi maganar tana bud'e laidar
ganin pant da pat da riga a ciki ta zaro rigar tana kare masa kallo.
ido Feeryal ta waro ita sam tagama mancewa da rigar a gurin.
tun ranar da suka dawo ta jefashi duka da laidar cikin wardrobe ta mance da shi.
"Wannan rigar fa kamar ta maza ce ai wannan."
cewar Aunty tana duban ta.
"Laa namance na wannan ne daya bani a hotel d'in nan da suka yaga min kaya na saka."
"Wai na Abdurrahim ke kamma Feeryal akwai shiririta, shine tun washegari baki mayar masa da kayan sa ba,
to ai sai ki kai masa kayan sa kya aje a nan."
ta mika mata rigar.
"Kai masa yanzu ki dawo karb'i hijab ki saka."
ta miko mata hijab ta karb'a ta saka.
Aunty sai binta da kallo take tana murmushi,
tayi kyau sosai cikin hijab d'in tamkar balarabiyar asali.

Ido ta lumshe jin iskar waje ya bigeta.
tun ranar da ya citota ya dawo da ita gida, bata kuma sa kafa cikin gidan ba sai ya.
koda Miemie ta zo sunyi hira iyakar rakiyan ta da ita bakin kofar parlour.
hango get d'in su Miemie tayi tana lissafin taje ta kirata ta rakata ta kaimasa.
"Ko zai karb'a ma oho to amma ai jini bai tab'a masa rigaba ranar."
tayi maganar ita kad'ai.
ta sa kai tana shirin tafiya sashin su Miemie taji karar mota a bayan ta.
da sauri ta waigo tare da matsawa gefe.
motar tawuce.
batasan wa ke ciki ba dan gilashin motar mai duhu ce.
sai da ya wuce tasoma takawa a hankali.
a gaban side d'in su Ajmal motar ta tsaya.
Ajmal ya fito daga side d'in su ya zo jikin motar.
tazo daf da motar ganin Ajmal a gurin ta juyo tana shirin gaida shi, idanunta ya sauka kan nacikin motar.
idanunsa kan wasu files yana dubawa sannan ya mika wa Ajmal d'in.
shi kuma ya karb'a yana yiwa Feeryal murmushi.
itama ta maida masa a gajarce ya juya da sauri ya nufi parking lot yana gyara rikon files d'in.

Ganin shine a motar tashiga takowa a hankali zuciyarta na tsalle, a sannu ta karaso jikin motar kanta a sunkuye.
ta d'ago ta kalleshi,
idanunsa na kan wayar da yake dannawa,
tun ranar da ya taimake ta taji girmansa ya shinfid'u a ido da zuciyarta.
a hankali ta miko masa rigar cikin siririyar muryarta ta ce
"Nagode Sahab ga rigar."
yakai 1min kafin ya d'ago idanunsa ya sauka cikin nata.
"Sahab."
sunan da ta kira shi da shi ya nanata a ransa.
da sauri tayi kasa da kanta.
shiko ya yi wa motar key ganin haka yasa ta d'an matsa gefe yaja motarsa ya wuce sashinsa.

Kallon rigar tayi kana ta kalli bayan motar nashi, sai kuma ta juya.
dan dama ta sammaci haka daga gareshi,
tasan ba lallai ne ya karb'i rigar ba dama,
ko ya yi sammanin da jini a jikin wannan rigar ne shima.
rau-rau tayi da ido ta juya.....!




20
Tana daf da shiga side d'in Aunty tajiyo muryar Miemie tana kiranta.
ta juyo ta tsaya tanata murmushi.
Miemie ta karaso rike da yarinya a hannunta.
"Ina kika fito ne Feeryal, shine kin fito ko nimata bakiyi ba ko."
tab'e fuska tayi ta ce
"Wannan Sahab d'in ne na kai masa rigarsa da ranar ya bani, yauma yaki amsa."
"Ranar d'in ma jinin ya tab'a ne?."
kai ta girgiza.
"To ki ajiye idan kika kuma bashi bai karb'arb'a ba, sai ki bawa wani,
um ga motar Ya Faruoq can mijin Aunty Farida, yazo zasu tafi bari na kai mata 'yarta, ko zaki rakani?."
"Aa jike ina jiran ki anan."
"Dalla zo muje ke zaman guri d'ayan ma ko damin ki baya yi, kullum kina nanike a ciki, ni ina zan iya ai sai dai in ciwo nake, shima ina jin dama-dama bazan zauna ba zanyi waje na mike kafa,
d'an rike min ita na gyara."
Feeryal na karb'ar ta ta ce
"To muje."
Miemie tayi sauri tayi gaba.
Feeryal ta biyo ta tana fad'in
"Miemie ki karb'e ta dan Allah."
Miemie ta dad'a sauri tana dariya har suka karaso gurin motar Faruoq daya fito yana tsaye jikin motar.
"Ya Farouq ina yini."
cewar Miemie tana waigen Feeryal tana mata dariya.
ya amsa idanunsa akan Feeryal data kwab'e fuska kamar zatayi kuka.
hannu ya mika mata alamun ta miko masa 'yarsa da take ta tsallen ganin uban nata a hannunta.
ta miko masa ita tare da gaishe shi.
ya amsa idanunsa a kanta kana ya dubi Miemie ya ce
"Miemie dariyar zolaya ko, me kikayi mata take b'ata rai."
ta ce "Ni ban mata ko mai ba kwad'ayin kuka take ji, yanzu zakaga tana yi."
tayi maganar cike da zolaya tana kallon ta.
dariya ya yi yana cewa
"Au haka take da saurin kuka, to gaskiya ya kamata a sami mai rarrashi, meye sunan kyakkyar?."
Miemie ta ce
"Feeryal sunan ta."
kai ya jinjina yana cewa
"Sunan dai-dai da yanayi."
zai kuma magana Farida ta fito.
wani irin daramm taji ganin Feeryal a gaban mijinta idanunsa tarr a kanta yana ta mata dariya.
Miemie ta ce
"Aunty Farida ai Neezrah ko kuka batayi ba tana ta wasan ta, zan zo har gida na d'auke ta muzo mu wuni."
wani irin abu ta had'iye tamkar kayoyi a makoshinta, kai kawai ta iya gyad'awa Miemie ta bud'e mota ta shiga.
Farouq ya ce
"Anya kuwa Miemie ni dai a hannun Feeryal naga baby Neezrah ya tabbata dai ta iya raino ba ke ba."
ya yi maganar yana bud'e gefen direba har lau yana yiwa Feeryal murmushi.
Miemie ta bigi kafad'ar ta ganin tayi murmushi tace
"Hum wai har taji dad'i sai kace ita tayi rainon."
tafiya ta soma tana fad'in
"Ai nima nayi daga can zuwa nan."

Har suka fice a gidan Farida bata iya cewa komai ba tana zaune zuciyarta na tukuki.
tun a hanya Farouq ya ke ta kawo mata maganarta ya na cewa
yarinyar she is so cute completely.
hirarsa d'aya biyu sai ya sakota, har duka isa gida
bai fasa ba.
suna shiga parlour'n su ta kwab'e mayafinta tana haki da yadda take jin zuciyarta kamar zai yi bindiga.
Neezrah ya aje kan kujera yana fad'in
"Zauna 'yar rainon Feeryal ko gobe zakije gidan su ne, dan naga ke ma sai murna kike a gidan su."
cikin masifa da tafasar zuci ta ce
"Badai gidan su ba sai dai gidan mu dan ba gidan uban Feeryal bane can."
ta juya fuu ta shige d'aki.
murmushi ya yi dan bai kawo komai a ransa ba ya cigaba da yiwa 'yar sa wasa.

Da daddare har ya yi nisa a bacci ta tashe shi, dan ita takasa baccin, sabar masifar kishi.
ta bubbugashi tana fad'in
"Faruoq ta shi ka gaya min mene ne dalilin dayasa kake ta kawo min maganar mayyar aljanar yarinyar nan, tun a mota har a cikin gidan nan, wace munafurci kake kullawa cikin ranka."
ido ya bud'e cike da bacci ya ce
"Haba Farida a tsohon daren nan zaki tada ni da wani magana mara kan gado, babu ko Abba'n Neezrah ma yau to me zan gaya miki, me kuma zan b'oye miki cikin raina,
dan nayi maganar kanwarki shine wani abun tashin hankali."
"Dakata Faruoq ba kanwata ba karka sake had'a ni da ita, dan babu abun da ya had'ani da 'yar da ba'asan asalinta ba,
tsintacciyar cikin ruwa,
daga yau karka sake kawo min batun ta cikin gida har in kana son zaman lafiya a gidan nan."
janyo ta ya yi jikin sa ya ce
"To naji shike nan Sleep please bazan kara ba."
Farida bata iya bacci ba sabar yadda take
jin zuciyarta, kamar ana mata luguden tab'are.

Washegari da safe bayan ya fita office ta shirya ta d'au mota sai AA FIYA STREET.
tana isa b'angaren Mommy ta shige.
Mommy na ganin ta ta ce
"Ya akayi Farida ko jiya kinyi mantuwa ne?."
ta ce "Nazo cin uwar mayyar yarinyar nan ne, jiya kwana Faruoq ya yi yana ambaton sunan ta,
zo muje Sumayya ko Ameerah ku kira min ita."
Ameerah tayi kus kamar bataji ba.
Mommy ta ce
"Ke Sumayya tashi kije ki kira mata ita, ai kiyi mata tatas in da gobe bazata kuma bin kurwar sa cikin dare ba."
Farida ta juya ta fita Sumayya ta bita tana fad'in
"Aunty Farida da kin rabu da ita."
hararar ta tayi
bata tsaya ba sai da tafito waje ta ce
"Wuce kije ki kira min ita."
Sumayya ta wuce sashin Aunty.
a parlour ta tadda Aunty ta ce wai Farida tana kiran Feeryal.
Aunty ta d'anyi jim sannan ta ce
"Me ya faru ta ke niman ta?."
ta ce "Ni ma ban sani ba tadai ce na kira ta."
kai ta jinjina ta ce
"Shiga tana ciki."
Sumayya ta shiga ta sameta tana bacci ta tasota ta d'au hijabi suka fito.
har sun kai kofa zasu fita
Aunty ta ce
"Tafad'i abin da zata fad'a ki dawo bance ki amsa ta ba."
Feeryal ta gyad'a kai kana suka fita.
Aunty ta koma ta zauna bataji ko d'arr ba dan tasan ba shegiyar da ta isa tasa mata hanu yanzu ta share, sai dai taji wa jikinta.

Farida na ganin su tasoma tahowa tana fad'in
"Yau nazo naci uwar ki har gida naga wanda ya tsaya miki."
ta na isowa in da take ta shako wuyan hijabin ta.
"Meye had'aki da mijina da zakisa ya koma gida yana kawo min zancen ki,
maitar taki takai har kin fara bibiyar mijina,
me za'ayi dake da ba a san asalinki ba,
to wlh gargad'i na farko na karshe idan na sake ganin ki a inda mijina yake sai nayi miki d'anbanzan duka na b'ata fuskar da yake rud'in ki yake kaiki ga mazajen mutane,
shegiya mayyar banza aljanar ruwa,
nafi karfin ki wlh ba dai miji na ba."

Ajmal dake tahowa ta bayansu ya ce
"Meye haka Farida wani irin abu ne wannan meye amfanin hakan."
cikin masifa fa ce
"Karabu dani Ajmal naci uban yarinayr nan, dan wlh bata isa ba mijina yafi karfin ta."
"Kaji wani shirme dan Allah ita cewa tayi tana son mijin naki."
"Idan ta fad'a ma basai na kasheta ba, wlh mijina ya girmi ajinta 'yar da ba a san asalinta ba ma,
idan bata fita sabgar miji na ba, wlh sai na halakata."
kai Feeryal ta sunkuyar Ajmal na kokarin jan hannun Farida da ke rike da wuyan hijabin ta wayarsa tayi kara.
ya zaro wayar a aljuhu ya kai sa kunne
daga cikin wayar ya ce
"Bawa Farida wayar."
ya zaro a kunnen sa yamika mata yana cewa
"Wai gashi."
sai da ta harare sa kamar ita ce gaba da shi kafin ta ce
"Inji wa nifa baza'a mareni a hanani kuka ba."
ta fizge wayar ta kai kunnenta.
Ajmal yashiga waige-waige yana son ganin daga ina yake har yasan abin da yake faruwa, yana d'aga kai ya hango sa can saman upstairs na side d'in sa yana tsaye rike da Mug a hannunsa ya yin da d'aya hannunsa ke kare da waya a kunnensa.
daga cikin wayar Farida tajiyo muryar sa

"Saketa! baki da hankali ne zaki rika d'agawa mutane murya a cikin gida, oya fita ki bar gidan nan ki koma gidan ki, kar ki kawo wa mutane haukar banza,
kisa ta tarawa mutane jama'a."
Farida ta tura baki ta mikawa Ajmal wayarsa.
ta sake ta tana cewa
"Allah ya taimake ki wlh da sai kin gane cewa mijina ba saranki bane,
mayyar aljana kawai."
ta juya fuu ta yi gurin motarta tashige tabar gidan.

Ajmal ya dubi Feeryal da jikin ta ya yi sanyi yace
"Yi hakuri Feeryal kije abin ki."
a hankali ta juya.
tana shiga Aunty ta bita da kallo ganin jikin ta a sanyaye ta ce
"Me yasa Farida'r take niman ki?."
murya a sanyaye ta ce
"Wai nafita sabgar mijinta wai ya koma gida yana zance na."
Aunty tayi murmushi tare da girgiza kai
ta ce "Je kiyi wanka kizo kiyi breakfast."
ta juya ta shige bedroom d'in ta.


Ji ya yi an rungume shi ta baya, Kuraiba ta manna kanta a bayan shi tana shafa kirjinshi.
cikin narke murya ta ce
"Mijin Kuraiba ba ko zuwa duba ya na kwana ba, kasan da ya nayi bacci kuwa,
gurin nan sai zafi yake min sai da nayita gasashi da ruwan zafi,
ka duba min zafi yake min har yanzu."
hannunta ya b'anb'are a kirjin sa ya juyo tare da wasa mata wani kallo kana ya juya ya bar gurin.
wani uban mika ta sake tana tuna kasantuwarsu har yanzu zakinsa yaki gogewa a kwakwalwar ta,
tana ji ina ma ace ta kasance cikin hakan yanzu..

Umma Karima ce tsaye cikin d'akin ta, rike da waya a kunnenta.
daga cikin wayar ake fad'in
"Hajiya sai yau Allah ya yi aka samo wani da kyar,
in zaki biya million 2 idan guri ya rufa zan kawo miki."
Umma Karima ta sauke wani nannauyar ajiyar zuciya tana fad'in
"Allah na gode maka wahalata tazo karshe, million 3 zan baka shima ka rike ne dai-dai komai ya dai-dai ta zan biyaka kud'in aikin ka mai soka."
"Hahaha Hajiya to na gode anjima zaki ganni."
Umma Karima ta sauke wayar tashiga tika rawa.
tana fad'in
"Sai ni Hajiya Karima bani Dubai London bani England."
tawani shekewa da dariya
"Hahaha yanzu wasan zai soma.......!




21
Guri na rufawa kamar yadda mutumin da sukayi waya da Umma Karima yace zaizo kuwa sai gashi yazo.
a parking lot d'in ta ya tsaya tafito ta sameshi.
ya mika mata wata bakar laida yana fad'in
"Ga sakon ki Hajiya na d'auki kasada sosai amma na shafe duk wata shaida."
har hannunta na b'ari ta karb'i laidar tana cewa
"Kai sannun ka da aiki kayi namijin kokari da kai za'aci arziki saboda kayi rawar gani wajen ganin an samo arzikin,
yanzu ga wannan miliyan ukun ne, kaje ka sha shayi da su kayi murna lokacin arzikin ka yayi."
ta mika masa jaka mai d'auke da kud'ad'en da ta shirya ciki.
ya karb'a da murna yana fad'in
"Lallai kuwa godiya nake Hajiya, ai muna fadarki muci arziki mu barta a inda take."
har ya shiga motar sa bai fasa zuba mata godiya ba, yana fita tashiga kwad'awa Liti direban ta kira.
ya shigo cikin hanzari yana amsa kiran nata.
ta ce
"D'auko makullin mota da sauri fita zamuyi yanzu."
"Ina kuma zamuje Hajiya da magriban nan?."
"D'auko da'alla a hanya kayi min wannan tambayar."
ta shige mota da sauri tana rungume laidar da kyau a jiikinta.
sai da suka haura titi kafin ya dubeta yana cewa
"Hajiya ina muka dosa ko tafiya zamuyi ta yi kawai?."
ta ce "Dajin Mali zamuje kara gudun motar yi sauri hanzarta."
"Hajiya ba dai kud'i kika d'auka a laidar nan zaki kai masa ba, ni fa dama ina da bukatar wasu kud'ad'e sabo da na kwan biyu ban yi aike gida ba."
"Ni matsala ta da kai ke nan, kullum baka da damuwa sai na kud'i, ko an baka sai ka kuma niman su, ka aje bukatar kud'in nan naka yanzu sai an gama komai tukun,
Allah na tuba idan aiki ya kammala meye kud'i kuma ai sai dai ka bawa wasu,
kai dai yi sauri mu isa."
Liti ya kara gudun motar yana cewa
"Wai gara in fad'a miki da wuri ne kar ki kwashi kud'ad'en duka ki kai masa mu mu rasa."

Karfe 7 da rabi suka isa saboda gudun da motar take.
Umma Karima ta sauko a motar guri ya rufa yayi duhu, babu tsoron Allah bare tsoron dukun dajin bare tsoron wani mugun dabba mai cutarwa.
zuciyarta ya kekashe muradin ta kawai take hangowa a gabanta.
ta kunna hasken wayarta ga kuma hasken fitilar mota.
jiki na rawa na son cikan muradinta, sai kakabe laidar take a jikinta.
ta cire mayafi ta kunce d'ankwali ta cire takalmi, ta d'uru cikin duhuwar kogonnan, zuciya a kekashe babu d'igon tsoro bare imani.

"Gafara dai boka yau gani tafe da babban guzuri, nasamo cikon na uku."
wani irin hargitsastsen dariya kogon ya kaure da shi
"Hahahaha kinyi nazari da lissafi mai kyau, saura kiris laya ta gama narkewa jeki sanya shi cikin tukunya."
da sauri ta isa gaban tukunyar kaskon tajefa laidar ciki.
wani irin hargitsewa gurin ya yi da wani irin sauti mai ban tsoro,
tukunyar ta kama tafasa tana dafuwa tamkar wutar zuga,
wani kumfa ya taso fuuu yana bin jikin tukunyar yana gangara zuwa cikin wani rami mai zurfin gaske da ba'a iya hango karshen sa.
jikin Umma Karima na rawa, idanunta a kan tukunyar, har kumfar tagama sauka tas tukunyar ta shafe kamar babu abinda ya tab'a zama cikin ta.
kazamtacciyar dariyar nan ya kuma kecewa da shi yana fad'in
"Aiki ya kammala ikon ki ya soma."
zubewa gaban shi tayi tashiga karanto mishi ayoyin godiya.
ya ce "Tashi kije gaki ga duniya kin samu."
jiki na kyarma ta mike tafito daga kogon ta kwashi kayakin ta, tashige mota bakin ta yaki rufuwa.
Liti ya kunna motar su ka soma fita daga dajin.
ganin yanda yau ta fito cikin mashahuriyar farinci daga gurin bokan nata ya ce
"Hajjaju an samo wata nasarar kenan."
baki ta dad'a washewa ta ce
"Nasara mai girman gaske ma kuwa, kai dai yi sauri mu isa gida kawai."
karfe tara ya kawo su gida, Umma Karima ta shige gida tana jin kanta da girma.

Da misalin karfe goma na dare Daddy na zaune yana dube-dube cikin computer.
Mommy na zaune a gegen sa dan yau ita ce da shi.
da sauri ya kai hannu ya dafe kansa tare da fad'in
"Innalillahi wa innailaihirraji'un."
ya rike kansa da karfe
yana jin wani irin sarawa da kan sa keyi had'e da jiri da gilmawar bakin duhu.
addu'a yarika karantowa duk wacce tazo masa baki.
Mommy ta mike tana masa fifita da fad'in
"Alhaji me ya faru?."
yakai tsawon minti goma a haka da taimakon Allah da addu'a yarikajin sassaucin abin da yake ji.
har ya iya janye hannunsa a kan da yake ji kamar an d'aura masa wani katon abu mai matukar nauyi.
kallon Mommy ya yi dake tsaye tana masa fifita, numfashi ya ja da kyar yana tuna da Fad'imatu'n sa ce da da addu'a zata taimaka masa ba fifita ba.
ido ya rumtse yana jin girman ta cikin zuciyarsa, lallai mace mai ilimi garkuwa ce cikin gida.

Da kyar ya iya mikewa ya dawo bakin gado ya zauna, yana cigaba da ambaton sunan Allah.
har yakai bayan sa ga katifa bai fasa ambaton Allah ba,
yana ji kamar ana kafa masa kusosi cikin sassar jiki musan kansa da yake jin sa kamar zai rabe gida biyu sabar nauyi.
yakai awa guda idanunsa a rumtse bawai ko dun ya yi bacci ba.
Mommy kuwa ganin ya yi suru da addu'o'in da yake a fili, tuni ta d'ale gado tashiga sauke minshari.
sai wajen karfe biyu kafin ya samu bacci marad dad'i ya d'auke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login