Showing 30001 words to 33000 words out of 63585 words

Chapter 11 - FEERYAL Part 2 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.txt

laifin ta bane ita kanta kwalliya ce, bata bukatar karin kwalliya.
ta saka ashoben ya zauna a jikin ta kamar dan ita aka halittasa
ta d'aura mata d'ankwalin, tare da rataya mata wani d'an siririn gyale.
kana ta bi jikin ta da turare.
Miemie da mai yin kwalliyar duk tsayuwa sukayi suna karewa Feeryal kallo
"Ya ilahi ya lillahi, zan iya rantsuwa tun da nake harkar yiwa mutane kwalliya ban tab'a yiwa wata kwalliya a 1time ta haska tamkar wacce na d'au Three hour ana mata kwalliyar ba,
ba wani fenti nayi miki ba paudar ma sama-sama na goga, ba kwalliyar ce tayi miki kyauba ke ce kikayi wa kwalliyar kyau,
sai kace ke ce amaryar."

Miemie da ta bud'e baki sai yanzu ta rufe
"Idan da amaryar ta sami kyanta ai da ta gode da bamusan in da rawan kanta zai tsaya ba,
yanzu ma yaya,
muje Feeryal nasan yanzu kam kowa ya watse ma saura mu."

Direban Ammah da Miemie ta hanashi d'aukar kowa tace ya jira su ya kaisu, shi ya d'auke su zuwa filin taron........!



Babu editing

14
Tun da suka doso gurun baka jin ko mai sai sautin tashin kid'a.
motarsu na fakawa Miemie ta fito da sauri tana fad'in
"Feeryal yi sauri ana kan yi ban da mu."
ta zaga ta gefen da take ta ruko hannunta suka nufi cikin Hall d'in.
Feeryal ta rike hannun Miemie gam ganin jama'ar gurin maza da mata gabad'aya ya tada mata hankali.
"Miemie ni kam zan zauna a moto na jira ki idan an tashi ki zo mu tafi, ga mutane fa."
"Dalla muje mutanen cinyeki zasuyi, illa iyaka ki zame musu abin kallo kamar dai yanzu da ido ya bar kan amarya ya dawo kan mu,
ke ki natsu da'alla ki d'aga mana aji, saura ace azo ayi rawa kiki zuwa,
zo muje ta can ga gurin zama."

Da sauri ta d'ago ta hangi ango da amarya Kuraiba sai washe baki take,
angon nata kuwa na zaune fuskarnan tafi ta kullum murtukewa da rashin annuri.
"Ido ta waro ganin in da Miemie take nuna mata,
sai sun tsaga ta sakiyar filin kafin suje gurin.
"Miemie mu zauna ata can mana."
"Ke tacan zamuje so nake a tantance kasa da sakuwa, sakanin kwalliyar mu danasu Ameerah,
duba kika yadda suke kallon mu,
kirika murmushin nan naki abin zai fi bada show,
ki had'a da juya wannan idanun naki, kinayi kina irin wannan tafiyar naki kamar na yanga."
Miemie ta karasa maganar da dariya..
itama dariyar tayi tana zame hannunta daga rukon da ta mata, ta zille tayi d'aya gefen.
dole Miemie ta biyo ta.

Biki ya yi biki mawaka ana ta gwangwaje basira kowa da kalar baje basirar sa da yake,
anyi manni an zubda daloli.
Feeryal sai zuba murmushi take abun ya burge ta ba kad'an ba.

MC ya gayyaci ango da amarya da su fito fili.
tun MC bai rufa baki ba Kuraiba ta mike,
tana yi masa alama da ya taso.
shiko fuska yadad'a had'ewa.
da sauri Mommy ta mike daga gurin zamanta ta je ta ruko hannunsa, bakin ta yakasa rufuwa
"Taso mana Abdurrahim yau fa ranar farinciki ne, taso ka rike amaryar ka ku shiga fili."
badun kar ya dizga Mommy gaban kawayen ta ba, da babu abin da zai sa ya tashi,
karfa-karfan da akayi masa ma na zuwa gurin ya ishe sa.
ya mike ta kamo hannun amaryar ta had'a da nashi, ya zame hannunsa ya rike iya yatsarta d'aya.
a haka suka shiga filin.
wata sassanyar waka aka sakar musu, amarya ta takarkare ta rika tikar rawa,
shiko yana tsaye abin ma haushi ya bashi ganin yadda ta dage take tikar rawa,
sai kuma wani mammannewa take a jikin shi.

Mommy da uwar amarya Hajiya Luba da Hajiyan Dubai da kawayen su suka taso,
suka shiga b'arin kud'i a jikin su.
sai kace ganye suke wasa musu.
sai kirari ake musu, iyayen ango iyayen amarya.
Farida ma ta taso ta bud'e bakin jakanta.

Bayan su Mommy sun koma gurin zaman su, su Amerrah ma suka taso suka shiga wasa 'yan kud'ad'en da suka zo da su a jakarsu.
Miemie ta mike tana fad'in
ai na mance Daddy ya raba mana 50-50k ga naki ma a jakata."
ta ciro d'aurin 'yan d'ari biyar-biyar sabbi tar mika mata d'aya.
"Taso muje muyi masa liki."
tayi maganar tana kokarin roko hannunta.
da sauri yati baya da hannun ta tana cewa
"Aa kyale ni je kiyi masa likin ga nawa ma duk ki had'a kiyi masa likin kawai."
"Ai baki isa ba kowa ya je ya yi masa liki ke ce bazaki je ba,
ai dai zaki je ki taya shi farinciki, Allah sai kin je taso muje."
"Dan Miemie ni ki rabu da ni kije kiyi masa kawai ni bazani ba."

Hannunta ta figa ta janyo ta tana tirjewa Miemie tana cewa fa sai ta je.
d'an karamin bakin ta ta cuno tana bubbuga kafafunta a kasa tare da yarfe hannunta tana cewa
"Ni dai Miemie ki barni ni dai bazan jeba."
a haka ta janyo ta suka shige filin.
wani irin tafi gurin ya kaure da shi ji kake
rap-rap-rap.
da sauri ta tsaida buga kafa da yarfe hannun da take ta d'ago kai da sauri.
taga mawakin yana takowa in da suke ya yin da yake ci gaba da rera salon baitin sa,
Camera ya dawo kan su.
yana zuwa in da suke ya shiga ciro kud'i a aljuhun sa yana lika mata.
aka kuma kaurewa da tafi had'e da hele..
kai ta sunkuyar a hankali ta soma yiwa ango da amarya liki kamar yanda taga Miemie take musu,
amma kanta a sunkuye.
sai shigowa filin ake madadin a yi wa amarya da ango liki sai mata liki ake.
ita dai kanta a sunkuye bata yadda ta d'ago ba, tana ta lika musu kud'in hanun ta.

"Kamar ke ce amaryar sai kike fi dacewa da angon."
da sauri ta waiga bayan ta, wata babbar mace ce tsaye tana mata liki ta baya.
murmushi matar ta sakar mata, itama tayi mata gajeren murmushi.
tana juyo wa idanunta ya yi karaf da nashi.
wani mugun kallo ya wurga mata,
da sauri ta zame jiki ta fice a filin ta koma gurin zaman su.

Amarya Kuraiba ta bita da ido.
wace ce ita daga fitowar ta ta cinye taron ko ita amaryar ba a yi ihun fitowar ta haka ba.
ta had'iye abu mai d'aci a wuyan ta, ta aje tambayar ta cikin ranta sai bayan biki zata bibiyi wace ce ita,
da zata fito filin da aka tanadar domin ta har ta janyo hankalin mutane kanta.
daga an ga 'yar wata kasa sai duk a rud'e.
tayi kwafa a kasan ranta.
ta maida hankalin ta kan angon nata,
ta cigaba da shishigewa jikin sa.

Daga in da Mommy ke zaune take ta aikawa Feeryal harara, wan da ita batama san tayi ba.

Feeryal na zama ta sauke numfashi Allah ya gani ba son shi cikin irin wannan taron take ba.

Bayan ango da amarya sun zauna aka gayyaci kannen ango.
duk yadda Miemie taso ta tashi su shiga fili fir take, haka ta kyale ta ta je suka tika rawar su..



Duk da cikin taro ne bai hanashi busa sigarin sa ba, yana yi yana karkata baki irin na 'yan iska.
cikin muryar 'yan kwaya ya ce
"Kai dubi wata had'ad'd'iya zazzafan kayan dad'i."
"Ai tun d'azu na lura da irin had'iye yawon da kake akanta, kai fa Jazu ba karamin maye bane amma na mata."
wani dariyar rashin mutunci ya ke ce da shi
"Ke Zuly mata abin so ne, wancan yarinyar ta tara kayan dad'i a guraren nan."
dariya tayi tana kallon in da take
"Ba karya kam ta aje komai zam-zam amma nan gani nan bari, sakanin ka da shi kallo daga nesa."
"In dai zaki taimaka min me zai hana bazan samu ba."
"Nawa zaka biya?."
"500k."
"Seriously yanzu nake son jin su a banki na."
"Idan kika gama aikin ki zaki jisu, kin san dai bama haka da ke."
"Baka da matsala."
ta fad'a tana mike wa, ta nufi in da su Feeryal suke zaune.

Kujerar da ke fuskantar Feeryal ta ja ta zauna da murmushi kan fuskarta tana fad'in
"Sannun ku dai sister's to ya bikin?."
"Gashi ana kan yi."
cewar Miemie."
zama budurwar mai suna Zuly ta gyara idanunta a kan Feeryal ta ce
"Tun daga can na ke ta hango ki, na ce yau daren nan tawa ce nayi samuwar kawa,
sunana Zuly."
ta karashe maganar da miko mata hannu.
ido Feeryal ta bita da shi batare da ta miko nata hanun ba, sai murmushin da tayi mata.
Zuly ta dubi Miemie ta marairaice murya.
"Kawar tamu bata magana ne dan Allah kice ta ce min wani abu mana."
Miemie ta tab'e baki
"Da alama dai yanzu ta kurmance."
"Hahaha amma anyi kyakkyar kurma anan to a haka nake son ki da kawa,
kin ga ke ma kin zama kawata tun da ke kawar kawata ce,
ni suna na Zuly ke fa."
maganar ta bawa Feeryal dariya.
tad'an dare.

Hannu Miemie ta mika mata kamar yadda itama ta mata tana cewa
"Ni kuma Miemie ita kuma Feeryal."
"Wow nice names, amma ku kannen ango ne ko naganku da ankon kannen ango?."
Miemie ta ce
"Eh mu kannen sa ne."
sosai ta dage tayi ta zuba musu hira, Miemie uwar 'yan surutu tana taya ta.
har Feeryal tad'an saki jiki tana d'an sa baki cikin hirar.

Karfe 12 dai-dai aka tashi, motoci suka soma jidar mutane suna maida su gida.
tuni ango ya shige nashi motar ya yi gida batare da yajira komai ba,
dan dama ya yi yinkurin tafiya har sau biyu Mommy ce ke hanashi.
aka kwashi amarya da kawayen ta aka tafi da su A.A FIYA STREET.

Su Miemie sukayi waje gurin nasu motar.
har gurin motar Zuly ta biyo su,
suna kokarin shiga mota,
ta ce
"Dan Allah ku d'an jira ni na duba na gani ko motar da nazo ciki ta tafi,
dama kai amarya zanyi sai na biku kawai."
ta juya da sauri suna tsaye suna jiran ta jikin mota.

Can ta nufa in da mutane suke tsastsaye da ala ma jiran mota suke.
da sauri ta karaso gurin ta ce
"Sannun ku mota kuke jira?."
suka ce Eh.
ta ce "Ga mota can babu kowa cikin ta, ku karasa mana ku shiga."
ai ko da sauri suka nufi in da ta nuna musu, ita kuma ta yi saurin isa gurin
abokin harkallar ta sukayi magana kana ta juyo da sauri, gurin su Miemie.
mutanen da ta ce misu ga mota can suna zuwa kuwa suka kama d'uruwa cikin mota.
Miemie ta ce
"Aa ya ya haka ya da shiga mana mota?."
suka ce gidan amarya zasu kuma ance musu wannan motar gidan amarya ce.
Feeryal ta ce
"Miemie rabu da su su shiga kamar zai d'au ke mu ai motar."
tun kan ta rufa baki suka shige.
Miemie ta shiga gaba tana cewa
"To ai sai ki zo ki shiga nan mu had'u mu makuru."
tayi maganar tana hura hanci.
murmushi Feeryal tayi ta shiga ta zauna gefen ta tana kokarin rufe murfin motar,
Zuly ta karaso gurin tayi saurin rike murfin
"Ah me zan gani haka wariyar launin fata za'a gwada min, mota ta cika ni ina kasa,
to ai kuwa sai dai ke ki fito, mu nima wata motar,
yauwa gama mota can sauko dan Allah muje mu shiga can, ba girman ku bane zama a matse alhalin daga gidan A.A FIYA kuka fito, yaho muje can motar."
ta janyo hannun Feeryal ta fito ta maida marfin ta rufa tana fad'in
"Allah ya tsare gamu a bayan ku muma sai mun iso."
direba ya ja motar suka fice daga harabar Hall d'in.

"Muje ko ga motar can."
suka jera zuwa gurin motar.
ta bud'e gidan baya,
maza biyu ne a zaune a ciki sai kuma d'aya a mazaunin direba, ta shiga ta masa can ta mannu da mazan sosai, ta ce
"Shigo mu lallab'a, ko kuma kai fita kar mu tseta sosai."
wan da yake jikin kofar ta can ya sauka ya koma gefen mai zaman banza.
kana Feeryal ta shiga jiki a d'an sanyaye dan bata tab'a shiga mota da maza irin haka ba.

Babu wan da ya yi magana a cikin su har suka fice.
sunyi tafiyar da baifi na mintuna biyar ba motar ta tsaya.
na mijin da ke gefen Zuly ya bud'e motar ya fita, itama ta sauka, shi ya dawo cikin motar ya rufe kofar.
ta zago ta gefen da Feeryal ta ke ta d'aga mata hannu
"Bye bye 'yanmata sai mun sake had'uwa."
da sauri Feeryal ta dube ta cikin rashin fahimta.
ita ko ta juya tana cigaba da d'aga mata hanu, ta shige wani motar da yanzu ya karaso gurin.
tana shiga aka figi motar da gudu.
wani irin juyowa tayi jin an......!




15
An wani rungumo ta, ido ta waro cike da matukar tsoro.
ya dad'a wani cacumo ta yana fa d'in
"Wayyo kai kaji jiki kamar auduga,
ja motar nan da sauri mu karasa ko mai zai iya faruwa a nan, nazo har wuya fa."
ya ja motar suka shari wata kwana, tuni cikin ta ya d'ura ruwa sai musu-musu take tana tutture shi.
ta fashe da kuka da ihun niman taimako.
a bakin get d'in wani hotel suka yi hon,
a ka bud'e suka shige ciki.
d'aya na mijin da ke zaune a gaban mota ya miko masa key dai-dai san da suka gyara parking.
ya ce
"Room 13 shine d'akin ku asha dad'i lafiya oga."
wani dariya ya sake hahaha. yana shafa fuskar Feeryal da yayi dama-dama da hawaye.
"Yi shiru mana zazzafa wannan irin kuka haka sai kace yanka ki zanyi, kayan dad'i kawai zan baki, kuma ke zake fad'i farashin ki da kanki, ba kyauta zan more kayan alatun nan ba,
muje ki fad'i nawa zan biya."
ya bud'e motar ya fito kana ya miko mata hannu ya ce
"Zo muje ko 'yammata."
da sauri ta matsa baya tana girgiza kai, hawaye na zuba.
ya mika hanu ya janyo ta ya fito da ita tana tirjewa, had'e da ihu.

Babu kowa harabar hotel d'in guri ya yi shiru, sai masu gadin hotel d'in su biyu.
ihu sosai take tana fad'in a taimake ta.
amma masu gadin sai dariya suke suna fad'in
"Kai Zazuu kabi a hankali fa sabuwar hannu ce wannan da gani."
ganin zata bashi matsal sai kawai ya ciccib'e ta ya yi ciki da ita.
a bakin kofar room 13 ya direta ya rike ta gam da d'aya hannun sa, d'ayan kuma ya zura key'n ya bud'e kofar kana ya tura ta ciki shima ya shige ya zare key'n ya maida shi ta ciki ya kulle kofar.

Sosai Feeryal ke kuka kamar zata shid'e,
ta shiga magiya da rokon sa
"Dan Allah kayi hakuri kar kayi min komai, wlh ni bana son kud'in ka bana so dan Allah dan Allah."
ta kuma rushewa da kuka sosai.

Shiko wani irin murmushi yake sakewa yana tako wa in da take,
baya ta shiga ja tana girgiza kai.
har ta garu da jikin gado,
hankad'a ta ya yi a kan gadon ya hayo kanta, yashiga shafa gefen fuskarta
"Oh zazzafa ki natsu mana, ni fa ba d'an yankan kai bane,
ni kawai mai bada gudumawa ne agaggauce;
baki tab'a sanin dad'in abin bane, ko kin hange sa a wando ne ya tsorata ki,
ki nutsu mu more juna gaskiya zan sha zaki kamar zuma,
ta ina zamu fara ko kin bani zab'i."
yana maganar yana tafiya da hannunsa jikin ta.

Ido ta rumtse da karfi tana bige-bige da shure-shure, had'i da kururuwa, jikin ta na kyarma.
"Ki dai na wannan ihun babu wan da zai jiki a nan, ko an ji ma babu mai zuwa taimakon ki,
ke dai ki baje kawai mu more."
ya mike a jikin ta tare da rungumota ya matseta a jikin sa ya zuge zip d'in rigarta yana kokarin yin kasa da rigar.
kara ta kwalla ta yanka masa cizo a kafad'a.
da sauri ya sake ta yana murza gurin.
ta mike da gudu ta duro a gadon, ta isa bakin kofa tana kokarin murza ki, ya bita ya ruko ta.
ya janyo ta ya kuma tura ta a kan gadon.
ya bita yana kokuwan tub'e rigar jikin ta.
jikin ta na b'ari tarika ture shi tana kuka kamar zata shid'e.
ganin yana daf da cire mata riga, takuma takarkarewa ta yanka masa cizo a kunne.
yana sakin ta ta mike aguje ta shige toilet ta danna kofa ta murza key tana haki.
ta sulale kasa tare da kuma fashewa da kuka, tana toshe bakin ta...


A b'angaren su Miemie kuwa, har sun d'au hanyar A.A FIYA STREET.
d'aya daga cikin matan da suke cikin motar, ta ce da 'yan uwan ta
"Gaskiya fa dare ya yi karfe 12 da wani abu, yaushe har muje gidan amarya mu kuma juyawa gida, dare zai mana sosai,
gaskiya muwuce gida kawai in yaso gobe sai muje,
dan Allah direba ka sauke mu ko a kan titin,
Area-rod ne mu karasa kaga babu masu abin hawan ma."
Miemie ta juya ta kalle ta ta ce
"To ai muma dare zai mana yaushe har muje can."
"Dan Allah kiyi hakuri baiwar Allah tun da motar gida ce zaku koma ai, yanzu mu idan aka sauke mu a nan babu abin hawan da zata kwashe mu,
ki tai maka a sauke mu a can d'in.
Miemie ta yi shiru tana jan kwafa a kasan ranta.
direba ya juya akalar tafiyar ta su izuwa Area-rod.
a bakin titi suka sauke su kafin su suka juyo gida.

Ko da suka iso gida, duk motoci sun dawo har kowa ya shige b'angaren su.
amarya tana side d'in angon ta a b'angare d'aya na cikin side d'in.
a babban parking lot ya gyara fakin ta fito.
ta nufi sashin su.
tun daga nesa ta hango Abdurrahim tsaye cikin lambon gefen sashin hajiya.
yana sanye da wando 3qtr da singilet, hannunsa d'aya ya zura cikin aljuhun wandon d'aya hannun nasa kuma yana rike da mug, yana d'an kurb'ar Coffee.
a hankali ta karaso batayi sammanin zai tare ta ya tambaye ta ina ta fito ba dan yasan daga gun bikin sa suke,
sai kuma ta ji akasin haka.
"Ina kika tsaya sai yanzu kika dawo, ina sauran suke."
da sauri ta ce
"Wasu 'yan uwan amarya ne suka bi motar mu muka sauke su a unguwar su,
su Ameerah kuma sun riga mu dawowa ma."
"Kowa ya dawo ke kad'ai ce a waje?."
kai ta gyad'a ta ce "Eh."
kai ya jinjina tare da kai mug d'in bakin sa yad'an kurb'a.
sannan ya juya a hankali.


Har itama zata juya ta jiyo maganar Aunty.

"Miemie har kun bani tsoro ina kuka tsaya ne, har sai yanzu kuka dawo, ina Feeryal d'in take?, kowa ya dawo gida ku kuna waje."
Miemie ta ce
"Feeryal kuma ai tun d'azu ta dawo motar su ma ya riga namu dawowa, dan mu sai da muka biya muka sauke mutane kafin muka juyo gida."
"To ina ta shiga ke nan ban ganta ba, dan tun d'azu nake zaune a parlour ina zaman jiran dawowar ku, a wata motar ce ta dawo?."
Miemie ta ce
"A motar 'yan'uwan amarya, motar mu data cika ne wata 'yar'uwar amarya ta ce tazo su shiga motar,
mun rigasu tashi kam amma nasan dole zasu rigamu isowa dan mu sai da mukaje Area-rod kafin muka juyo gida."
da sauri Aunty ta juya tana fad'in
"To

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login