Showing 171001 words to 174000 words out of 205258 words

Chapter 58 - AL'AMARIN MARYAM BOOK COMPLETE PDF END .txt

yayarta uwa daya uba daya.






Farida da su safna, anty Rabi kusan Kullum nan suke wuni kuma suna yabawa da kulawar Aisha ga Mimi.








Dake Qur'ani warakane sai gashi a hankali Mimi ta fara samun sauqi, ta dena digar da jini ta kunne kuma qafar kumburin ya Sabe sosai kadan ya rage sai dai bata takawa. Rashin maganar nan dai shine matsalar da kuma shirmen cewar mama na kiranta.








Bature yafi kowa murnar samun wannan sauki, ya kuma dagewa da kaita asibitin a zatonsa maganin asibitine yasa hakan. Kudi kuwa baisan abunda ya kashe ba Kullum cikin sadaka yake da sakawa ayi sauka Allah ya kawo sauqi. Kuma a hankali sauqin yana samuwa shima kuma ya fara maida hankali kan aikinsa.








Ya Taheer Kullum da safe saiya shigo duba Mimi kafin ya fita aiki, kuma ya yaba da saukin da ake cewa ta samu har yaga gaskiyar Bature daya hanasu fadar bata da lfy wa yan kano, ashe da sun fada da sunyi gaggawa tunda gashi sauqi Kullum samuwa yake.








Su Farida da safna sun dan rage shigowa kowacce ta samu xama a gidan mijinta a dalilin ganin sauqi ya samu. Farida sai a lokacin ta fara awon ciki don da bata faraba tunda babu nutsuwa.








Yammacin asabar liqis tana falo tana kallo da Aisha shi kuma yana cikin dakin batasan me yake ciki ba amma dai ya dade. Ta miqe tsaye tace da Aisha bara in gwada inga xan iya tafiya?






Aisha tace "a a madam bari inxo in riqeki karki fadi" tayi dan murmushi tace 'barni dai in gwada Aisha komai saida gwaji" ta fara takawa a hankali Aisha na binta a baya karta fadi, har qofar shiga bedroom din kana Aisha ta dawo tunda tasan yana ciki.








Ta shiga ciki a hankali take takawa tana dingishi, yana cikin bathroom yaji shigowar mutum yace "waye?" tunda yasan bamai shigowa ciki sai Aisha, a iya saninsa kuma Mimi bata tafiya sai an turata a kujera. Yacigaba da kiran waye? Amma shiru.






Kamar a mafarki yaga Mimi a bakin bathroom din yana cewa "maryam kece ko mafarki nake?" ya tsame hannunsa daga cikin kumfar da yake mata wankin undis dinta (pants da bra) ya dauraye ya matso jikinta yace "maryam ke kadai kika shigo? Lallai sauqi ya samu godia ta tabbata ga Allah." ya kamota ta xauna kan kujerar daya ajiye mata suna dan hira yana wankinsa.










Ta kalleshi xuciyarta cike da tausayinsa da sonsa tace "ya Bature kai kakemun wankin undis?" ta fada tana kwallah. Yace "common meye aciki Mimi luv dan nayi miki? Ada aike kikemun ko? Yanxu Allah ya kawomu lokaci nima ina miki aiba wani abu bane" ta share hawayenta, yana aikin suna jifan juna da murmushin luv har yagama sukai alwalar magrib suka fito.








Sosai sauki ya samu, kowa ya saki jiki don abunda ya rage kawai dawowar walwalarta.






Ranar monday da wuri ya fita aiki sabida suna da meeting, kuma Mimi tayo masa rakiya har bakin mota da dingishinta sai dayaga ta koma sannan ya shiga suka tafi.








Batare data xaunaba ta shiga bedroom ta koma bacci, Aisha tanata aikinta hadi da leqawa taga ko Mimi ta tashi ta kawo mata abinci amma taga bacci take. Har tagama komai Mimi na bacci, ta fitowa da mimin kayan da zata saka dan a tsarinta tana tashi take wanka kana ta yi break fast. Doguwar rigar atamfa mai laushi ta dakko mata, bataga Dan kwalin rigar ba so saita dakko mata kashka medium irin wanda ake dorawa saman doguwar rigar ta hada mata da atamfar ta ajiye a kusa da Mimi gefen gado. Kana ta fita gurin kitchen gurin moses inda suke haduwa gaba daya da ragowar ma'aikatan suna ganin yadda yake girki suna hira.






Dake hausawa sunce baya bata da kadan, Mimi cikin baccinta taji ya Bature na tashinta, ta farka a firgice ta kalleshi tace "harka dawo?" yace mata "eh" kawai ya zarce dayi mata wasannin soyayya. Ta xare jikinta don batason wannan harkar sam a halin yanxu tace masa bari nai wanka, ta dingisa ta wuce bathroom. Tana wanka tana tunanin meya dawo da ya Bature gida yanxu shi da yace mata yau meeting garesu? Da wannan tunani ta fito wankan, abun mamakin sai ta samu dakin wayam babu kowa, da sauke ajiyar xuciya a fili tace "dama nasan bazai dawo yanxu ba, May be mafarki nayi"










Ta shafa mai tana saka riga ta hangeshi kwance ta cikin madubi tsirara akan gado, gabanta yayi wata irin faduwa. Ta juyo taga gurin wayam, ta kuma kallon madubin ta hangoshi kwance. Hankalinta yayi wani irin tashi tayi yunqurin ihu amma ta kasa don bakinta ya sarqe.












Tana cikin wannan haline taga ya dunfarota, ta runtse ido tana so tayi ihu ko addua amma bakin ya rufe gam, dalilin ihunta kuwa ganin wannan mutumin mai nufota tsirara da nufin sex da ita al'aurarsa har qasa take wato takai gwiwarsa kuma wai sex xeyi da ita. A fuskarsa dai kamannin mijinta sak, amma tasan mijinta bashi da wannan mummunar Al aurar. Allah ya temaketa ta yunqura ta miqe tare da xarar mayafinta tai waje da gudu. Tafiya take tana waige amma ga mamakinta binta yake tsirara yana dariya.








Ta nufi gate dake brain din irinta yarace wai saita nufi office din su Bature a nufinta taje taga shine wanda ke binta koba shi bane. Me gadi ya bude mata gate yana cewa 'sannu madam jiki yayi kyau, gidan alh ishaq xaki leqa kenan?" ta fita ba tare data tankashiba sabida hankalinta yayi gaba.








Ta tari napep a layin ta fada masa yakaita Company din NNPC. Ya fara tafiya da sauri don yaga alamar sauri take don suna tafiya tana waige. Ita kuma anata bangaren ya Bature take gani har yanxu yana binta kuma tsirara yana dariya ga mamakinta kuma sauri yake har yana wuce ababen hawan dake gudu kan titin.








Yana ajiyeta ta shige cikin ma aikatar da gudu, yana cewa hajia kudin bata saurareshi ba ita kawai burinta ta gujewa wannan dake binta kuma taje office din ya Bature taga shine koba shiba.










Sai dai abunda yayi mata cikas bata San office din nasa ba tunda bata taba xuwa ba, dan haka ta nufi babbbab hall din da suke meeeting inda ta hango jamian tsaro jibge gurin suna gadi.








Ta nemi shiga suka hanata tare da tambayar wacece ita, ta dunga nuna musu mutumin dake binta tare da ce musu gurin mijinta xata. Sukace ta tafi tabasu guri su basuga kowa ba, daya daga ciki yace "su kyaleta da alamar mahaukaciya ce"








Suna ta dauki ba dadi tsakaninsu da ita, su sun hanata shiga, ita kuma ta kafe saita shiga sabida wanine ke binta.










Daga cikin dakin meeting din suka farajin hayaniya tayi yawa, mr Alex ya tura Hanifa taje taga meke faruwa. Ta miqe dan cika umarninsa










Duk da tanada masaniyar abunda ke going amma sai datayi mamakin ganin Mimi anan tana fada da sojojin. Direct tace "ku barta ta wuce matar Eng SULAIMAN A AZEEZ ce, tana da tabin hankali" ta bawa Mimi hanya ta wuce tana wani shu'umin murmushi na cikar buri.










Tana shiga gurin ta fara cewa "ya Bature! Ya Bature!! Kana ina? Kaxo xai kasheni, ko kaine ka turoshi ya tsoratani?" Bature kansa sunkuye yana rubutu ya tsinci muryar Mimi tana fadar haka.












Ya tashi da sauri ya nufeta, tuni ta fita hayyacinta sai maganganu take wanda rudi yasa baya gane abunda take fada. Duk gurin yayi shiru ita kawai ake sauraro, Hanifa na tsaye jikin qofa tana murnar Mimi fa lokaci yayi domin da alama hauka ya kankama.






Yaje ya riqeta yana girgixata da cewa "Mimi ki dawo cikin hankalinki plz, waye xai kaaheki? Meya kawoki nan?" ta dubeshi ta kuma dubi me kama dashi wanda har yanxu take ganinsa yana mata dariya tare da kiranta da "taho Mimi luv nine ya Baturenki" ta dunga kallonsu a tare, ta rasa waye na gaskiyar, take anan kwakwalwarta ta juye ta kwallah qara ta xube qasa sumammiya.










Wadanda ke gurin suka taso xasu tayashi daukarta, ya tsaidasu da cewa xai iya. Ya ciccibeta cikin rashin sa a mayafin dake rufe kanta ya xame ya fadi qasa, tsautsayi yasa ya takashi bai saniba aikuwa satsin tiles dana mayafin ya kwasheshi yayi qasa ya fadi Mimi dake hannunsa kuma ta fadi gefe wanwar kan cikinta.










Qarar faduwarta da kiran sunanta da yayi a tare suka fito, beyi ta nasa faduwanba ya nufeta a gigice yana girgixata da fadin "maryam ki tashi, maryam ki taimakeni ki bude ido" duk wanda ke gurin sai da ya tausaya masa ciki kuwa harda Hanifa da itace silar faruwar komai.










Akayo kansu gaba daya ana masa sannnu cikin sauri ya dakko wayarsa ya kira ya Taheer da ishaq a taqaice ya fada musu abunda ke faruwa.










Suna tsaye cirko cirko yayin da Bature ke tsugune gaban Mimi da bata motsi yana kuka haiqan ya Taheer ya iso. Ya dudduba Mimi shima take ya fara hawaye don gani yake Mimi ta mutu. Isowar ishaq yasa suka tsagaita da kukan, ya tsuguna ya dinga chaje Mimi, ya dago yace musu tana da rai tabbas. Ya Taheer cikin hanxari yace "to sulaiman inaga a sada yarinyar nan da iyayenta tunda har abun yakai haka ta fara fitowa." ishaq yace hakane yafi dacewa.










Bature badan yaso ba ya yadda, Taheer yace bari yaje ya samo tiket. Ishaq kuma ya fara bata taimakon gaggawa don numfashinta ya dawo.










Mr Alex ya matso cikin tausayawa yace "ya bada jet dinsa akaita" Bature yaji dadi sosai sukai godia, nan take ya kira pilot din yazo da jet din, Aka dora Mimi kan gadon marasa lfy ishaq ya juna mata drip da oxygen Taheer da Bature suka shiga jet din ya daga xuwa kano.










Meeting din daba a qarasa ba kenan, akaita jimamin halin da matar Eng sulaiman ke ciki.








Ishaq be koma asibiti ba gida ya nufa.






Hanifa kuma gwaggoriya ta kira ta fada mata abunda ya faru cikin farinciki amma bataji dadin tafiya da Mimi kano da akaiba. Gwaggoriya ta kwantar mata da hankali cewa ai a kano sai tafi nesa da sulaiman don tasan yana kaita zai juyo ya dawo Abuja sabida aikinsa ita kuma acan xata sulale ta gudu ta shiga dawa. Hankalin Hanifa ya kwanta da jawabin gwaggoriya ta bar damuwa data fita har sadaka tayi murnar aikinta yaci, kuji kwaba yan uwa wai layya da kare.










Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] β€ͺ+234 706 296 6299‬: πŸ™†πŸΌπŸ™†πŸΌπŸ™†πŸΌAL 'AMARIN MARYAM πŸ™†πŸΌπŸ™†πŸΌπŸ™†πŸΌ



Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)




πŸ“FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 6⃣0⃣








Ishaq yana isa gida ya samu Farida har bed room tana shirin wanka daure da towel. Babu sallama ya balbaleta da masifar cewa tana ina har Mimi ta fita taje office din sulaiman sabida tsabar shashanci da sakaci irin nata?






Farida ta tambayeshi cikin rudewa da neman maimaita mata abunda yace Mimi tayi. Cikin masifa kamar xai daketa ya fada mata duk yadda akai.






Ya dakata da fadan da yake dai dai lokacin da yaga Farida tayi xaman yan bori tana ihun kukan kiran sunan Mimi dan Allah a temaketa a dawo da mata da Mimi.






Ai tuni ya dena fadan ya dawo lallashin Farida da fada mata Mimi yanxu an wuce da ita kano kuma xata samu sauqi in shaa Allah. Shima dai a ranar aiki ya sameshi don farida taqici taqi sha sai kuka da kiran sunan Mimi da kuma cewa lallai saiya kaita kano itama dan gani take Mimi mutuwa tai suke boyewa. Haka ya yini lallashinta har bayan sallar asr.








Ya yiwa Baqo waya yace ya tattaro masa duk masu aikin gidan su sameshi anasa gidan.






Cikin qanqanin lokaci sukaxo suka sameshi, ya dunga binsu da kallo yana kada qafa, mugun haushinsu yakeji kamar ya tashi ya rufesu da duka.








Ya fara magana cikin qunar rai "abun takaici ne ace duk yawanku a cikin gida har maryam ta sulale ta fice baku sani ba, bayan kudin kunsan tana da lalura ba a rufe muku ba" suka rude da jimami da kalaman kare kansu na basusan fitar madam ba.








Ya daka musu tsawa da cewa suyi masa shiru, sukai tsit suna sauraransa yace "sakamakon abunda sakacinsu ya haifar antafi da maryam kano, dalilin haka ni kuma na koreku aiki gaba dayanku." falon ya cika da koke kokensu, farida tana zaune tana jinsu batasa baki ba idonta yayi jajur sabida kukan data yini yi.








Ya daka musu tsawar cewa su bace mai da gani, suka tashi jiki a sanyaye suka dunga fita Aisha ce kadai ta rage. Ishaq ya kalleta yace "ke xaman me kike?" ta matso kusa da qafafunsa cikin kuka tace "Dan Allah Alh kayi haquri, wlh lokacin dana bar madam bacci takeyi, sai yanxu da kaxo da lbrin abunda ya faru. Nidai kasani motar kano yanxu in bita can in tayasu jinyarta badon a bani kudi ba, sai don rama dinbin alkhairin da tayi yimun" ishaq yayi dan jim, Farida ta dafashi "ya ishaq ka kyaleta ita, amanace sosai tsakaninsu da Mimi" yace "to shikenan kije xuwa da safe sai inkaiki tasha ki tafi kano dan yanxu dare yayi."










KANO


Isarsu direct Aminu kano teaching hospital (AKTH) suka sauka. Dake abun na manya ne da gaggawa aka amshesu aka wuce da ita A&E. Likitocin emergency suka rufu kanta a qoqarin neman numfashinta.








Ya Taheer shi yayi waya ya sanar da gidajensu halin da ake ciki dan Bature bashi da nutsuwar haka, duk nacin likitocin da ya fita ya basu gurin suyi aikinsu amma dole suka kyaleshi domin yaqi fita qememe.










Faty wacce ta zama metro a halin yanxu ta riga kowa isowa don tana cikin asibiti wayar mama ta sameta tana kuka ta fada mata ankawo Mimi yanxu bata da lfy.








Ta tsaya akan Mimi tana taya likitocin aikinsu, suma sun qara bawa Mimi kulawa da suka gane sis din metro Faty ce. Aka bawa Bature takaddar biyan kudin gado da sauran charges din yaje ya biya. Amma qememe yaqi fita sai ya Taheer ne yaje ya biya aka bata gado.








Likitocin suka fito dan ansamu komai ya dawo normal amma tana bacci. Lokacin mumy, mama Dady da Baffa sun iso hankalinsu tashe. Faty ke musu bayanin Mimi ta samu bacci yanxu.








Suka dunguma dakin hankalinsu tashe yake har yanxu, mumy keta tambayar Taheer wane ciwone wannan farat daya Mimi tai wannan uwar rama kuma har aka kawota gida?








Sun sami Bature a dakin yana zaune gefen gadon hannunsa riqe hannun Mimi. Sai da suka xauna suka nutsu kana ya Taheer ya bude musu komai tun farkon ciwon har kawo yau.








Sukai jugum jugum suna sauraransa, mumy ta kalli ya Taheer tace "amma Taheer kaci amanarmu a matsayinka na babba a tsakaninsu, don sulaiman bashi da hankalu kaima baka dashi kenan? Marainiyar Allah bata da lfy kusan 3wks ku hada baki ku rufe mana? Nagode kwarai Taheer wlh in maryam ta mutu saina daureku kaida sulaiman"








Taheer ya gigice yana bawa mumy haquri, bai zaci xata dau abun da zafi haka ba.








Ta dunga watsawa Bature harara cike da tsanarsa tace "nagode sulaiman kamar nasan abunda xai faru naji hankalina bai kwanta ka tafi da ita ba" ta daka masa tsawa "tashi ka bacemun a gurin" Bature dai bayajin abunda suke cewa balle yaji tsawar mumy, yacigaba da riqon hannun matarsa.








Mumy a ganinta rainin hankaline yana jinta, ta tunkareshi Faty tai saurin tsaida ita tana kuka tace "mumy yanxu duk ba wannan ne abunyi ba lfyar Mimi itace agaba, abunda xai faru ya riga ya faru" dole mumy ta tsaya.








Mama dai babu baki sai ido takebinsu dashi tana share hawaye. Dady kuma yanata kiran consultants daya sani a asibitin ta cikin wayarsa, yayin da Baffa ke kallon Mimi cikin jimamin jin wai maryam din yanxu ko tafiya batayi.












Xaman jigum jigum ya biyo baya har xuwa yamma, Mimi bata farko ba gadai oxgyen an saka mata da wasu manyan ingina. Sabida alfarmar Dady da Faty manyan likitoci keta zarya akan Mimi, tuni suka nemi asibitin Abuja aka turo musu duk record din ciwon on-line.








An turata xuwa dakin xray akai mata brain CT scan (photon kwakwalwa) photon da yakanyi 1wk kafin ya fito ita sabida gata a cikin 1 hour ya fito consultant a bangaren ya duba yace brain dinta normal take babu komai akanta.






Adai cikin wunin aka kaita physiotheraphy (bangaren likitan qashi) suma xray din sukai aka tabbatar babu matsala kamar yadda result din ya nuna a Abuja.






Duk wannan abun da ake Mimi bata sani ba don bata farko ba, a qarshe aka maidata Female medical ward, aka bata aminity (wato daki ita kadai) aka qara mata wasu inginan akanta da hanci sai qafar da suka daddaura wasu manyan qarafuna sukayi hanging din qafar da qarfen saman gadon.






Dukkansu sun rame a wuni guda kawai, anyi anyi Bature yaje gida yaci abinci yayi wanka tunda ance Mimi bacci take amma yaqi. Dady ne ke faman dashi mumy kam babu abunda tace masa tsakaninsu harara in sun hada ido dan mugun haushinsa takeji.








Magrib tanayi bayan idar da sallah Audu yazo, shidin ma dawowarsa aiki kenan lbr ya sameshi a gurguje ya kimtsa yaci abinci ya taho. Ya samu Baffa da Dady sun tafi gida,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login