Showing 174001 words to 177000 words out of 205258 words

Chapter 59 - AL'AMARIN MARYAM BOOK COMPLETE PDF END .txt

mumy da mamane kawai a gurin sai Faty daketa zirga zirga.






Suna gaisawa ya Bature ya dawo daga sallah, yayi fici fici dashi. Ya tashi yaje gurinsa suka gaisa yana masa yame jiki bejiba ya koma mazauninsa wato kan gadon Mimi ya riqe hannunta.










Mama ke masa bayanin tun safe yake haka riqe da ita, anyi anyi dashi yaje gida ya yi wanka yaqi. Yace "mama ke da mumy kuxo muje gida ku kintsa sai ku dawo tunda gani ga ya Bature ga Faty, in yaso inkun dawo saimu koma ku kuma ku kwana da ita. Suka yarda da shawararsa dan suma din tun safe suke tsaye yakamata suyi wanka suci abinci.






Ya debesu ya fara kai mama sannan ya kawo mumy gida ya wuce gidansa, yasmin na tambayarsa jikin Mimi yace da sauki kawai. Ya debi kayansa qanana Set 2 ya fice. Sai daje eatry yayi siyayyar snack dasu ice cream kana ya sayi fura. Ya koma store ya sayi soso dasu brush da kayan tea kana ya koma asibitin.








Yasamu ya Bature yadda ya bashshi Faty kuma ta fita. Ya rufe dakin yaje toilet ya hada masa ruwan wanka yakai masa komai sannan ya fito yace "ya Bature dan shiga ka watsa ruwa" baiyi gardama ba Don shima yana buqatar hakan.










Ya jima a toilet din, yayi komai har brush, ya fito ya shafa mai da perfumes ya saka kayan da Audu ya kawo masa. Yaji dadin jikinsa sosai, sai alokacin yaji gajiya bacci da yunwa sun rufeshi. Audu ne ya bashi tarkacen kayan da ya siyo, yana hillatarsa da hira yaci sosai ya kuma shanye furar tas. Faty ta shigo tana musu sannu, itama sai a lokacin ta samu xama taci abunda Audu ya siyo. Ta karbi Babynta a hannun me raino wanda yayi kuka har ya gaji ta bashi nono. Sunata hira ko ince jimami har 10:17 lokacin mumy da mama suka dawo, mumy dauke da tea flask mama kuma food warmer.










Suka qara jimantawa juna, mumy tace Faty ta tafi ita da Audu da Bature su kuma su kwana da Mimi. Bature qiri qiri yace "nifa babu inda xanje wlh" mumy ta haushi da xagi tana cewa "Dan ubanka kasan kana santa ka bari ciwo ya ragargajeta haka?" mama ta shiga tsakaninsu don ita Bature tausayi yake bata.








Likita da Faty suka kuma shigowa ya qara duba Mimi yace "bacci take kuma xata iya farkowa koda yaushe, sannan sunyi magana da wani likitan qashi a Dala zaizo gobe ya dubata shi da wani likitan kwakwalwa inma da yiwuwar a canja mata asibiti xuwa na Dala xa a canja" sukai godia ya fita. Audu ya dau Faty suka tafi ya kaita gida shima ya wuce nasa gidan.








Bature kuma ya miqe kan doguwar kujerar dakin ya fara bacci, yayin da mama da mumy sai lokacin suka zauna kan centre carpet din da sukaxo dashi suna cin abinci tare da jimanta ciwon Mimi. Mama kecewa "nikam Adda da anhaqura da surkudawa Mimi allurai mun koma gida anyi na musulunci don yadda Taheer yayi bayanin ciwonta kamar dasa hannu aciki" mumy tace "nayi wannan tunani fadima amma a bari xuwa goben muga farkowarta" Bature dake kwance yana sauraransu gabansa yayi wata irin faduwa, wannan shine abunda yake gudu ace xa aiwa Mimi maganin gida su riqe mai mata da sunan magani. Wlh kuwa baxai yadda ba ko sama da qasa xata hade, qafarsa qafar Mimi. Dan haka ya fara motsa kwanjinsa tun yanxu da cewa "mama maryam fa laulayin ciki ne ke damunta kawai, kuma tun a can munyi magani ta warke yaune abun ya dawo, munyi magana da wani abokinmu likita acan Germany ishaq na nema mana Visa ana samu xan wuce da ita can ayi duk abunda ya dace inta haihu ma dawo ki..... " mumy ta katseshi da cewa "Dan ubanka munsa da kai cikin maganarmu? Inka kuma saka mana baki saina zabga maka mari, karka nayi shiru akan abunda kayi kaxaci na haqura ka cuci banxa wlh saina maka hukunci, maryam kuma mu da kai naga wanda yafi iko da ita. Taqamarka daya dai matarkace ko? To ni kuma nina haifa na aura maka kuma innaga dama ina iya tsinka igiyar auren in aura mata wani tunda bakai kadai na haifa ba" jin haka yayi tsit, mama kuma haquri take bata.










Sun kwanta suna baccin suna farkawa sabida ko Mimi xata tashi. Qarfe uku dare nayi mama ta tashi ta shiga toilet ta dauro alwala da duqufa kan abun sallah tana nemarwa diyarta sauqi gurin Allah. Har akai kiran sallar farko shima Bature ya miqe yayo tasa alwalar ya fara nafilfili. A lokacin ne kuma Mimi ta tashi, tanata jijjiga gadon abunda ya farkar da mumy ta isa gurinta tana kiranta. Bature yayi gaggawar sallame sallar a xuciyarsa yace tabbas abunda mutum ya sabayi ko mutuwa xaiyi yana mutuwa akansa, tashin qarfe hudun dare yabi jikin Mimi ko a halin ciwo saita tashi.










Ya isa gurin Mimi wacce take kiran sunansa bakinta tar tana cewa "ya Bature xai kamani ka ceceni" abun dariya mumy ta hanashi qarasa kusa da Mimi ta shiga tsakaninsu tana cewa "kinga maryam bude idonki ki ganni mumyn ki ce a gida kike cikin kulawarmu babu wanda xai kamaki" itadai Mimi tunda ta hangi ya Bature ta bayan mumy take miqa masa hannu yaxo gurinta. Mama dake watching komai ta taso ta kamashi takaishi kusa da Mimi kana mimin tayi shiru tana qara damqe hannunsa kamar bata lura da wanxuwar su mumy a gurinba ko bata ganesu ba.








Yana shafa kanta dayi mata magana a hankali aka samu ta koma bacci.








Qarfe bakwai da rabi na safe ta kuma farkawa, lokacin dakin ya cika da yan dubiya kuma hayaniyarsu ce ta tasheta. Ta kwallah qarar kiran ya Bature, hankalinsu ya dawo kanta. Baffa da Dady suka matsa suna mata sannu, bata amsa ba ta fara sambatun a cire mata qafarta ta isheta da ciwo. Ta fincike qarafan da suka saka mata a qafar tana ihu, Faty tai saurin matsawa tana riqeta tare zare mata drip din karta jiwa kanta ciwo. Shigowar Bature tare da Dr yasa tai shiru.








Ya qaraso ya riqeta ya tadata zaune tanata sambatun ciwo, likitan ya fara aune aunensa tana dukansa da cewa ita ya kyaleta ya Bature ya cire mata qafar tunda yace ko babu qafa zai zauna da ita. Dr. Yace yana ganin afara kiran likitan kwakwalwa don matsalar brain dinta tafi tsamari yanxu don wannan abun da take shine matakin hauka na farko.










Kukan mama ya katse musu maganar da suke, inda take kuka tana cewa "wanene haka yayimun wannan aiki? Wanene ya jefemun yar da ciki a jikinta? Me maryam ta aikatawa wanda yayi mata wannan abu so ake ta shiga duniya da ciki kome?" Baffa ya taso ya riqeta yana bata haquri, Mimi sai lokacin ta lura da mama.








Tace "mama ki yafemun mutuwa xanyi, qafata da kaina ciwo sukemun. In na haihu a hayyacina koba a hayyacina ba na bar miki abunda na haifa duniya da lahira nasan xaki soshi ki masa tarbiyya yadda kikaimun" mumy da Faty suka saka kuka a tare. Likitan yace da Dady a ragu a dakin xaiwa Mimi allurar bacci. Amma Mimi tace "kar wanda ya fita akyaleta tai sallama da yan uwanta ta nemi yafiyarsu." lamarin daya saka kowa kuka a dakin.








Ta kama hannun Bature da Faty ta riqe gam tana hawaye, Faty ma kukan take, shi kuma Bature idonsa jajur. Mama ta matso tanawa Mimi adduoi tana tofa mata. Nan take Mimi ta rikice tana ihu ita batason wannan tofin tana qoqarin dukan mama. Bature ya tashi ya kama mama yakaita bakin kofa yana cewa "Dan Allah ku kyaleta tunda bataso, ya yarinya bata da lfy xa a xo a kama yimata tofi aka?" su mumy kallonsa suke sororo da alamu ya manta matsayin mama a gurinsa. Mumy cikin lallashi tace "Bature wannan ya nuna cewa ciwon Mimi iskace tunda batason a tofa mata ayar qur ani" ta kalli Dady tace "inaga Dady mu nemi sallama aje ayi na gida kawai" Baffa yace "haka ne dai dai Halima" take anan Bature ya hausu da fada cikin fita hayyaci yace shi babu inda xa akai masa maryam dan visarsu ta kusa fitowa zasuje Germany.








Dady daya lura dansa baya cikin hayyacinsa sai ya fara lallabashi da cewar ba rabashi xa a yi da Mimi ba just xa a riqetane na wani lokaci tanajin sauki xa a dawo masa da ita.








Ya fincike hannunsa daga riqon Dady yace "baxan baku itaba, meyasa kuke hakane? Kai rabaka da kai da taka matar? Sama da shekaru arba in kuna tare, sai ni dan mugunta xaku rabamu" ganin abun nasa ya wuce hankali mumy taxo ta zabga masa mari, Mimi ta saki wata ajiyar xuciya me kamada shaquwa. Mumy ta qara kifa masa mari, a wannan lokacin Mimi watsi tayi da duk wata na urar dake jikinta ta taso ta nufo mumy da nufin hanata dukan Bature. Sai dai kafin ta qaraso ta fadi qasa.






Ya riga kowa isa inda take ya dagata ya maidata kan gadon ya kwantar, tana kuka yana kuka tana shafa kuncinsa inda hannun mumy ya fito rada rada.








Tana kuka tana cewa "ya Bature karka tafi ka barni gurinsu, zasu dunga yimun wannan tofin ni banaso xan bika ka kaini asibiti."






Be daddara ba ya kuma komawa gurin Dady yace "Dady na tuba karku rabani da Mimi yanxu, she is my wife nd my best friend, nafi kowa iko da ita ku bani abata kota warke ko bata warkeba ina sonta a haka kuma xan kula da ita."






Dady yana hawayen tausayinsu yace "SULAIMAN haqurin dai xakai, gata ake muku kaida ita." yana jin haka ya juya ya nufi qofar fita. Ganin haka Mimi ta fara ihu na fitar hankali tana kiran "ya Bature karka tafi ka barni, ya Bature ina sonka Don Allah karkaimun haka, bazan iya rayuwa babu kaiba" tana yunqurun tashi Faty da Audu na riqeta. Shima Bature yana kuka sharban kamar mace ya bar dakin ko juyowa baiba.






Babu wanda be xubar musu da hawaye ba, da kyar Audu ya danneta Faty tai mata allurar bacci.










Cikin minti bakwai bacci ya fara daukarta, suka cikata Faty ta gyara mata kwanciya. Ta qaraso gurinsu mama tace "mumy anya bamuyi kuskuren raba ya Bature da Mimi ba a wannan gaba? Shi ya tafi yana kuka kamar mace, ita kuma tana ihun kiransa cikin fita hayyaci."








Mumy ta share kwallar idonta tace "Faty inbamuyi hakan ba ya xamuyi? Bature da Mimi basusan komai ba sai soyayyar junansu, kuma indai ba haka mukai masa ba baxai bari ayi mata magani ba" Faty tace "to Allah ya bata lfy. "








Abun mamaki Mimi ko rabin awa bataiba tana bacci ta kuma farkawa cikin ihu, duk kuwa da qarfin allurar da akai mata. Kiran sunan mijinta take tana cewa yazo ya dauketa.








Mumy da Faty suka matso suna mata magana, mama kuwa tana gefe tana kuka. Ta kalli Faty tace "ya Faty kiramun ya Bature indai kina qaunata" mumy tace "maryam yi haquri yaje ya karbo maganin da aka rubuta miki." ta kau dakai daga barin da mumy take tace "ya Faty nace ki kiramun ya Bature inban ganshi ba mutuwa xanyi" Faty tace "Mimi mumy na miki magana" tace "ba ruwana da ita, baxan qara kulata ba tunda ta daki ya Bature" tana fada tana kuka.








Faty tai murmushi tace "mumy kinji lefinki shiyasa akaqi kulaki" mumy jiki a sanyaye tace "yi haquri maryam, bansan xakiji haushiba da ban dakar miki shiba"










Suna haka har yamma tayi, qarfe shida lokacin yan dubiya ya wuce. Likita yaxo Dady ya nemi sallama, babu dogon bincike ya sallamesu dalili kuwa shine suma likitocin yau sha biyun dare dai dai xasu shiga yajin aiki.










Aka dorata kan kujera sukai gida da ita, a lokacin magrib tayi Mimi har tagaji da ihun a kira mata ya Bature ta haqura. Amma tayi jigum babu ci, babu sha babu magana.








Bature kuwa yana fita asibiti anan tashar gyadi gyadi yaji ana ambaton motar Abuja, ya shiga ya zauna take qaramace tana cika suka tafi.










Xuwa laasar yana Abuja cikin gidansa har yayi wanka, bai fitaba har bayan isha ko sallah a daki yake.








Ishaq ya shigo har bedroom din ya sameshi, shima Baqo ne ya kaimasa tsegumin sulaiman ya dawo ya qulle kansa a daki. Ya dafa sulaiman din yana tambayarsa jikin Mimi, bai bashi amsa ba sai kuka ya saka masa kana ya dora da cewa "sun kwaceta ishaq, sun kwacemun maryam kuma mumy ce ta jagoranci kwacemun ita, abunda nake nufi shiya faru wai maganin gida xasuyi mata. Abunda ya gagari likita shi xa a xauna ace xa ayi a gida?" ishaq ya jinjina wannan lamari, kuma shima yana bayan sulaiman don be yarda wai iska ke damun Mimi ba, shi yafi ganin malรกria ce ta haddasa mata wannan ciwon.








Ya danne nasa damuwan ya lallabi sulaiman din da cewar ya bari a kwana biyu suje suyiwa Dady bayani da nuna masa takaddun asibitin sai su taho da maryam din. Dakyar ishaq yasashi yaci abinci ya bashi maganin bacci yasha ya kwanta.










Mrs Hajia ๐Ÿ˜Š
[9/30, 1:05 PM] โ€ช+234 706 296 6299โ€ฌ: ๐Ÿ™†๐Ÿผ๐Ÿ™†๐Ÿผ๐Ÿ™†๐ŸผAL 'AMARIN MARYAM ๐Ÿ™†๐Ÿผ๐Ÿ™†๐Ÿผ๐Ÿ™†๐Ÿผ



Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)




๐Ÿ“FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 6โƒฃ1โƒฃ






Saqon masoya na iso mani ta hanyoyi daban daban, ina godia sosai.






Matan Baffa suka fito suna kallon maryam dake zaune kan kujera babu magana, aka shigar da ita har dakin mama. Baffa ya nemi ganinsu gaba daya suka hallara dakin mama harda Rashida wacce ke zaune a gida yanxu.






Baffa yayi musu bayanin lalurar dake damun Mimi kuma ya nemi hadin kansu akan hakan karo na farko a rayuwarta. Duk iskancinsu wannan karon basu nuna ba suka dunga jimantawa suna mata sannu da fatan samun sauqi. Ya gabatar da Aisha a matsayin yar aikin Mimi wacce taxo xama da nufin temakawa Mimi.








Bayan fitarsu mama ta fadawa Baffa Mimi fa babu abunda taci tunda aka kawota kano, ada ana saka mata drip yanxu kuma da suka baro asibiti babu wannan maganar. Yace to tabari yaje sallar isha ya dawo zaisan abunyi.








Ya maza jikin kujerar Mimi yace "maryamu me kikeson ci?" tai masa shiru. Mama tace ai haka take tunda ta fuskanci mijinta baya kusa da koma kurmar qarfi da yaji.








Faty xata iya cewa taji dadin wannan yajin aikin domin ta samu damar jinyar Mimi, daga asibiti gida ta biyosu ya Ahmad ya biyota da akwatinta da ragowar kaya. Shima babu yadda beyi da Mimi ba tai magana taki, Faty tai mata alwala akai akai tai sallah taqi.








Baffa daga masallaci ya taho da wani malamin islamiyya maqocinsu, ya nuna masa Mimi. Yace suyi mata alwala, sukace da alwalarta. Ya fara karanto mata ayoyin korar shedanu amma shiru kakeji, sai da aka fara karanta ayoyin sihiri sannan ta fara ihu da kuka.










Yace a samo garwashi da sauri Rashida taje maqota ta samo, ya xuba turare aciki. Mimi da bata iya miqewa sai gata a tsaye tana neman hanyar gujewa wannan turaren hayaqin. Baffa da Huxaifa suka riqeta dakyar don abun ya girmi mata.








Xan iya cewa aranar babu wanda ya runtsa a gidan sabida ihunta, ko ince har maqota na kusa. Tun malamin nayin abu shi kadai har abun ya gagareshi aka kira wasu malaman. Sunkai 3:00 AM suna abu daya, sun jigata sosai sun gaji itama ta gaji duk jikinta yayi laushi ga ihu ga yunwa. Sai dab da asuba ta samu bacci aka huta.








Duk tajiwa kanta ciwo da wadanda ke riqe da ita. Malamin kewa su Baffa bayani cewa Mimi fa asiri akai mata wanda aka hadashi da aljanu marasa imani kuma haukatata akasoyi don haka wannan aiki sai annemi taimakon wasu malaman wadanda suka fishi sani don abun yafi qarfin mutum daya ko biyu.








Mama dajin haka ta dunga kuka tana cewa ita ba Mimi take tausayiba illah abunda ke cikinta shi da bashi da haqqqin kowa, hankalinta a tashe yake akan haka ganin yadda ake dambe da Mimi take burgima tana murje cikin.










Sassafe saiga mumy taxo da Dady harda wani malami, shima yaxo duba matsalar Mimi, lokacin bata tashi ba. Faty ta lallaba ta tasheta, cikin hukuncin Allah kuma ta tashi qalau sai dai babu magana.








Faty ta taimaka mata tai wanka, ta shirya ta kalleta tace "ya Faty nayi sallah?" tace "a a maryam ana binki salloli da yawa" Faty ta dunga gaya mata sallolin da xatayi da kuma adadin raka oin tanayi harta idar.








Aka kaita dakin Baffa gurinsu Dady, ta dunga kallonsu ba tare da magana ba, sai sune sukai mata sannu da jiki, shima bata amsa ba sai murmushi tayi.






Malamin yana kallonta yace "maryamu meke damunki?" tai shiru, ya kuma maimaitawa har karo 3 amma tai shiru. Ya guntsi ruwan dake hannunsa wanda yaxo dashi ya fesa mata. Ta yunqura da gudu tayo waje tana ihu, duk suka biyota ya bada umarnin a riqeta. Baffa ya riqeta tamau, shi kuma yacigaba da guntsar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login