Showing 30001 words to 33000 words out of 94393 words

Chapter 11 - TASWIRAR KADDARA BOOK COMPLETE PDF .txt

Mrs A.M   

03 Aug 2024

16909

ki mayar dasu na ki ne ai ko so kike na dinga sawa ne ina yawo, haka kika bar min kayan kazantar ki a toilet ynxu da wani ya gani fa"


Da sauri na sunkuyar da kaina kasa cikin kunyar maganar sa, cikin lallashi nace "sir toh gashi na dawo dasu"


Daga kafada yai yace "baxan karba ba in nayi kyauta bana karba ragowar kayan naki ma suna jaka ta," juyawa yau ya bude jakar ya fito da pant da pad din tsirara ya miko min


Kallon hannun sa nai ganin abinda yake miko min yasa ni juya masa baya da sauri nace "na shiga uku"


Wani murmushi ne ya subuce masa da bai shirya masa ba.


Su Xuby da dukkan du suka hangame baki suna kallon ikon Allah da sauri Nana ta tabo Zuby ganin hawaye na zubo Mata, ajiye papers din Tai kawai na nufi kofa tana fashewa da kuka, suna su Nanan baya suka mara Mata da sauri.


Suna fita na juyo kamar zanyi kuka nace "sir ynxu me zasuyi tunani kace na bar kayana a toilet kuma Ka dakko wannan abun"


Kankance ido yai yace "ke me kike tunani badai kina tunanin vawulence ba kwaila da ke har kin iya wannan tunanin"


Zaro ido nai ina kama baki na nace "sir" sai kuma na ajiye masa ledar na juya cikin sauri na fita.


Shima idonsa ya zaro ganin yadda mazaunai suke rawa sbd sassarfar datai, cikin mamaki yace badai yarinyar nan ciko take ba, Tabe baki yai yana fadin kai kuma meye naka Azlan.


Komawa yai ya zauna amma sai ya kasa aikin masa kawai tunanin yadda take yawo a school ba Hijab yake Maza suna kallon ta.






************


Uku saura na karasa gida a gajiye nai wanka naci abinci Sannan na shirya cikin riga da skirt simple style na yada babban mayafi na rufe jikina, Aisha ma data sa irn kayana itama mayafin ta yafa.


Mimi nake sawa takalmi data dage akan sai ta rakani hadda birguma a akasa dole na shirya ta itama.


Mikewa bai bayan na gama samata takalmin na kalli Umma da take cewa kar mu manta mu tsaya mu siya mata fruits na dubiya daga Kai nai nace "Insha Allah Umma baxa mu manta ba"


Muna fitowa daga gidan mukai kicibus da cilla a daidaita zai wuce, tsayawa yai ya sakko yace "uwar dakina barka da wannan lokacin"


Murmushi nai don Allah ya sani kwana biyu nayi missing cilla don ma kusan kullum sai munyi magana ta WhatsApp, daga kai nai ina kallon sa yana ma Mimi magana suna dariya.


Kallon adaidaitar nai nace "ina Ka sami adaidaita cilla"


Dariya yai yace "ta saminu ce ta ban nadan yawata Nima a ciki ynxu xan fita ma mu gwada sa'ar mu"


Murmushi nai cilla yana burgeni sam bashi da matacciyar zuciya yana da zuciyar nema sosai, cikin Raha nace "toh muje mu zaka fara dauka asibiti muka nufa duba maman Asma'u"


Adaidaitar ya shiga yace "Bismillah uwar dakina shigo muje Allah sarki Nima na samu na duba ta"


Ciki muka shiga muna hira har muka isa asibitun bayan mun tsaya na sai musu kayan fruits na 1k din da Abba ya bayar.


Cikin asibitin muka nufa cilla na rike da laidar ni kuma ina rike da hannun Mimi, kasancewar Asma'u ta fada min number din dakin yasa bamu sha wuya ba gurin Nemo dakin.


Knocking mukai aka bamu izinin shiga muka shiga cilla kuma ya tsaya a waje tukun, ba mutane da yawa a dakin daga mamn tasu dake zaune akan gado sai Asma'u sai wani namiji da kallo daya zaka mai kasan yayan Asma'u ne.


Cikin girmamawa muka tsugunna har kasa muka gaishe da maman Asma'u da tambayar ta ya jiki, cikin sakin fuska ta amsa mana.


Kallon Asma'u nai wacce tun shigowar mu ta kafe Mimi da ido cike da al'ajabi murmushi na sakar mata nace "Asma'u ya mai jikin ALLAH ya Kara sauki"


Ajiyar zuciya ta sauke tace "da sauki Batul jikin Alhamdulillah anjima ma za'a sallame mu"


Masha Allah na fada ina gyara zamana don duk a takure nake sbd kallon da Yayan Asma'u yake min, Mimi ce dake Kan cinyata tace "Maa mun bar uncle a waje fah"


Dan bude baki nai na kalli Asma'u da kanta ya Kara daurewa Jin sunan da Mimi ta cemin nace "Asma'u tare muke da cilla shima yace zai duba jikin mama yana waje"


Ita ta shigo dashi shima yai mata ya jiki sannan muka muke bayan na ajiye mata ledar kayan Fruits din, sallama mukai wa Maman tasu ita kuma ta rako mu waje.


Rike hannun Mimi tai tace "wannan ma kanwar kice amma bakwa kama sam ni wallahi da Mr Azlan ma take min kama sosai kamar an tsaga Kara"


Duk da gabana ya fadi Jin sunan Wanda ta ambata amma hakan daure nace "Yata ce fa ni na haife ta"


Wani ja tai ta tsaya tana kallona sau kuma ta kalli Mimi tace "yar kice bana son wasa don Allah"


Murmushi nai ina cigaba da tafiya nace "wallahi yata ce kinji ma na rantse"


Da mamaki sosai tace "dama kin taba aure"


Shiru nai kawai ban mata magana ba ina kokarin controling mood dina har muka karasa gurin adaidaitan, shiga mukai nayi Mata sallama mukai gaba.


Har kofar gida cilla ya maida mu sannan na basa kudin motar, dakyar ya karba da yace baxai karba ba sai da na bata rai sannan ya Karba yana dariya.




Washe gari da wur na tashi don karfe 9 muke da lecture, amma sai Mimi ta tashi da rigima itama akan sai ta bini tunda an musu hutun boko da islamiyya duk yadda na rarrashe ta kin yadda tai hadda birgima akasa tana ihun wayyo Maaa ta daina sonta.


Kamar zanyi kuka na kalli Umma da tai kamar bata San muna yi ba, dole na shirya ta cikin doguwar rigar atampa na sa Mata baby hijab ba karamin kyau tai ba kamar ka saceta bama baby hijab din daya kasance dark blue sai ya haska fatar ta sosai.


Kudin kashewa na kara tunda da Mimi zanje ai nasan dole na tafu da kudi don Mimi bata shiri da yunwa.


Sallama mukai wa Umma da take dariya a ranta kuma tausayin Batul ne fal, murmushi tai tana binsu da addu'a.




A adaidaita sai da na gama ja Mata kunne akan Banda suruta kuma ban yarda ta yiwa kowa magana ba ba ruwan ta da mutane ita dai daga min kai kawai take bakin ta kamar zai tsage sbd murnar zan tafi da ita school dinmu itama.




Lokacin da muka isa har 9 ta kusa hakan yasa ni sauri ina rike hannun Mimi, sakin hannu na tai tana dariya tai gaba tana fadin "Nima zan iya MAA mu tafi toh"


Mun kusa zuwa hall dinmu sbd lecture din Mr Wicked ne shiyasa nake saurin zuwa don kar ya rigani shiga, da sauri na juyi Jin Mimi ta saki Kara a razane na kalli wanda ta bangaja din ina baya kamar zan fadi gabana yana tsanan ta bugawa.


Sir Azlan da yake tahowa hankali sa na kan wayar sa sbd wani sako da yake dubawa yasa bai San da mutum a gaban sa ba kawai sai ihun yarinya yai, da sauri ya sa wayar a aljihun sa yana sa hannu ya dago Yarinyar data sunkuya tana duba hannun ta data bige san da shi, wani irin bugawa kirjin sa yai da karfi sanadin arba da fuskar yarinyar da yai............
















Comments Nd share plz












Mrs A.M🥰
[24/08, 15:22] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️


*TASWIRAR KADDARA*


♠️♠️♠️♠️♠️




Written by
Mrs A.M🥰


Page 18




*BABY BEAUTY LOUNGE*


*INA YAN GAYUN SUKE MASU BUKATAR GYARAN JIKI, HENNA BLACK AND RED, PEDICURE AND MANICURE, MAKEUP, SALON KU GARZAYO ZUWA BABY BEAUTY LOUNGE DOMIN SAMUN DUKKAN WANNAN ABUBUWAN, HAKIKA GYARA SHINE MACE KUMA KO WACCE MACE YAR ADO DA KWALLIYA CE*


*INA MASU BUKATAR KOYAR MAKEUP DA SALON DUK MUNA YI A BABY BEAUTY LOUNGE CIKIN FARASHI MAI RAHUSA ZAKU SAME MU A TUDUN MALIKI TITIN ALASURE NO.995*


PHONE NUMBER 08183462148 OR 07058457638


*MUNA SIYAR DA MAGUNGUNAN MATA DANA MALLAKA DUK A BABY BEAUTY LOUNGE*


BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM






Cikin tsananin bugawar zuciya ya sunkuya kasa ya Kara riko fuskar yarinyar cikin rudani, itama Mimi manyan idonta irin nasa sak ta sake ware wa tana budewa kamar yadda yake da nasa a duk lokacin da wani Abu ya basa mamaki, "Subhanallah" ya fada yana shafa fuskar ta.


Cikin sauri na matso gurin gabana yana faduwa na finciko Mimi nace "zo mu tafi"


Cikin shagwaba tace "Maaa to ai uncle din nan ne ya bige ni kamar ya karyan kafa ma"


Na bude baki xanyi magana naji muryar sa data fara shakewa yace "zo beauty muga kafar ko na karya din"


Ganin ya biye mata yasa ta cire hannun ta daga cikin nawa ta tafi gunsa tana turo baki, murmushi ya saki Wanda ya bayyana hakoran sa farare ya riko hannun ta.


Kara sunkuyar da kansa yai gun kafar sa cikin faduwar gaba yake kallon kafar ta shape din kafar sa ce sak banbancin kawai wannan ta Yara ce, lumshe idon sa yai yana ambaton sunan Allah a zuciyar sa.


Hannu Mimi ta dora a kansa cike da shagwaba tace "Uncle baka duba kafar ba har ynxu na gaji"


Saita kansa yai kafin ya duba kafar Tata duk da yasan ba wani abinda ya Sami kafar kawai ragonci take, dagowa yai yace "uhm beauty ashe raguwa ce keh haka ba kiji ciwo ba"


Washe baki tai tace "toh Masha Allah, Uncle kaima a school din nan kake MAA dita ma anan take da kyar ta yadda tazo dani sai da na dinga birgima a kasa ina ihu"


Gajeriyar dariya Azlan yai yace "ni teacher dinsu ne, mai yasa bata so tazo dake"


Daga kafada Mimi tai tana ware hannu alamun itama bata sani ba


Jan kumatun ta yai yana rike Mata hannu yace "muje toh class din ynxu su Maa din taki zan koyar"


Da sauri ta tari gabansu cikin tsiwa nace "Sir ka sakar min yarinya ta zan shiga da ita"


Bin ta da kallo yai tundaga Sama har kasa wai yarinyar ta lallai yarinyar nan ta raina Sama tabe baki kawai yai ya zagaye ta ya nufi hall din


Kamar zan kuka na bi bayan su GA Mimi ina hango ta sai zuba take masa.


Muna shiga Hall dn gaba daya ido ya dawo kanmu bama Mimi dake rike da Azlan, ganin idon mutane yasa nayi gurin Asma'u wacce itama idon ta zuba mana na Kai tsakiya knn Mimi ta daga murya tace "Maa ki tsaya ni toh"


Ido na lumshe ina dana sanin zuwa da Mimi da nai, banza nai mata kawai don haushin ta nake ji na zauna gefen Asma'u.


Kallon sa Mimi tai ta dago ta kalle ni harara na watsa mata sai ta juya gunsa tace Uncle Maa haushi na take ji zata min fada bara naje gun ta


Daga Mata kai kawai yai ta juya tana tafiya har ta iso gurina, a kan cinyata ta zauna tana murza idonta wai don kar na Mata magana, banza nai Mata na maida hankalina kansa.


Jikinsa duk wani iri yake jinsa sbd arba da wannan Yarinyar da yai kamar sa da ita har ta baci har yanayin dimple dinsa irn nata ne komai nata irin nasa ne bai wani tsawaita ba don baya cikin mood Mai dadi ko assignment bai bayar ba.


Gurin da muke zaune ya taho idonsa akaina, murguda baki nai na juyar da kaina gefe gabana yana faduwa, tsayawa yai a gaban sit dn da muke ya miko wa Mimi hannu, ban wani damu ba don nasan Mimi bata da saurin sakewa da mutane amma ga mamakina sai Naga cikin sauri ta Mika masa hannu ta sauka daga jikina.


Juyawa sukai zasu fita haka yasa na mike nima da sauri na mara musu baya, muna fita daga hall din na kalle sa nace "Sir ina zaka kaimin yarinya ta"


Kallona yai yace "siyar da ita zanyi"


Wata harara na watsa masa kafin na dauke kaina na maida shi gun Mimi da ta sake rike hannun sa sosai tana wasa da xoben sa.


Kamar zan kuka nace "sir don Allah Ka sakar min yarinya mu koma kaga muna da lecture ynxu Kar lecturen ya shiga"


Daga kafadar sa yai yana tabe baki yace "ina ruwana ki koma mana"


Da sauri nace "Mimin fa"


Kallona yai yana kankance idonsa yace "in kun gama komai zaki iya samun mu a office dina"


Zaro ido nai nace "da Mimi zaka tafi office din naka wallahi baxan yadda ba yadda duniya take ba gaski....." Ban karasa ba sbd yadda ya juyo a fuskace yana kallona idonsa har ya soma kadawa zuwa jaa


Da sauri na sa hannu na toshe bakina cikin tsananin tsoro don ni ban taba ganin sa cikin wannan yanayin ba, kuma Allah ya sani bansan na fadi abinda na fada ba


Juyawa yai kawai da Mimi suka tafi ina tsaye har suka wuce hawaye ke kokarin zubo min gashi ba halin binsu don test muke da shi ynxu dole na koma hall kamar na fashe da kuka ina mitar baxan sake zuwa da Mimi ba.




Mimi kuwa suna tafiya tana masa hira yana biye mata har suka karasa office dinsa duk inda suka wuce sai an bisu da kallo don yadda suka jeru dinnan haka ya Kara fito da kamannin su da juna sosai.


Suna shiga office din Mimi ta kalle sa tana sakin hannun sa tace "Uncle nan ne office dinka"


Murmushi yai yace "eh kina sonsa"


Dariya tai tace "sosai ma yayi kyau kuma da akwai AC ina son Ac amma bamu da shi a gida".


Murmushi Azlan yai yace "kice wa Daddyn ki ya siya miki".


Turo baki tai tace "Banda Dad ni Maa tace Dad dina ya mutu baxai dawo ba."


Dan maida hankalin sa yai gun ta yace "wace Maa din taki?"


Murmushi tai cikin farin ciki tace "ai kaganta Uncle itace Maa dita muna zaune a gidan mu da Abba da Umma da Maa da Ya Aisha da Ya Kamal da Ya Khalil sai ni."


Sam shi bai gane mai take fada ba tace bata da Daddy kuma tace Abba da Umma, cikin son fahimtar maganan ta yace "kin ce baki da Daddy kuma kince Abba da Umma?"


Dariya tai tace "Abba baban Maa ne Umma ma Maman Maa ce ni kuma granny tace Ya Aisha Aunty nace Ya Khalil da Ya Kamal uncles dina ne ta karashe tana washe baki."


Cikin Mamaki yace "ita MAA din taki wace ita?"


Turo baki tai tana Zama akan kujera tace "Maa ce fah Mamana toh Uncle".


Zaro ido yai yace "ita ce Maman ki?"


Daga masa kai tai tana juyi akan kujerar sa cikin nishadi, mamaki ne sosai ya rufe sa sai a lokacin ya tuna yadda take cewa ya ajiye mata yarta Ashe maman tace amma wannan Yarinyar har ya isa ta haifi kamar yarinyar nan.


Mikewa yai ya nufi gurin fridge dinsa, budewa yai ya dakko ice cream ya nufi gurin Mimi da shi, Zama yai shima akan kujera yace "zo musha Ice cream"


Washe baki tai ta matso kusa dashi ta zauna tace "Ina sonsa sosai Uncle"


Murmushi yai yace "what's ur name beauty?"


Debo ice cream dn tai a spoon tana kaiwa baki Saida ta shanye sannan tace "My name is Khadija B"


Kallon ta yai yace "meye ma'anar B din?"


Cikin rashin damuwa tace "sunan Maa ne Batul"


Cikin mamaki yace "me yasa baki sa sunan Daddy dinki ba?"


Tabe baki tai tana lasar lips dinta tace *Maa ce ta samin bansan sunan Daddy naba"


Shiru kawai yai don baya so ya takura yarinyar da tambaya ahakan ma yaga kokarin ta da alama tana da wayo sosai.


Shan ice cream din suka cigaba suna sha tana basa labarin school dinsu da friends dinta, biye mata yai sosai yake Jin kaunar yarinya tana ratsa shi, shi sam baya Wasa da yara ko zama a kusa da su bayayi a cewar sa ciwon kai suke sashi sai gashi ya zauna yana hira da yarinya.


Sosai ta sake dashi don ta gama basa labarin kowa na gidan su hadda yadda Maa dinta take da cin abinci sosai, har labarin Hidaya sai da ta fada masa da maman ta.


Kallon ta yai yace "ynxu Maa din taki baxa ta siya miki wani babyn ba ki dinga wasa"


Marairaice fuska tai tana kalar tace haka tace "Uncle wai baxa ta siyo min ba ai maman hidaya ta siyo mana, kuma ni na fison ita ta siyo min mu dinga kwana tare dukkan mu"


Rike haba yai yace "gaskia MAA bata kyauta ba zan lallashe ta amma ta siyo miki wani babyn koh?"


Tsalle tai tace "thank you uncle"


Jan kumatun ta yai yace "ki daina cemin uncle ni Daddy dinki ne tunda kince baki da Daddy"


Ware manyan idonta tai tace "da gaske Uncle Ka zama daddy na?"


Daga mata kai yai yana karantar farin cikin dake dauke a fuskar ta


Murmushi tai tana tsalle tace "toh Daddy kazo school dinmu nima na nunawa friends dina kai nace musu ga Daddy na su daina cewa banda Daddy."


Mikewa yai yace "zanzo har school din naku Beatty nace musu nine daddyn ki"


Rungume sa tai tana murna rike Mata hannu yai suka fita don yasan ynxu haka sun fito daga lecture din duk da baya jin zai iya bata Mimi ynxu sam baya son rabuwa da yarinyar haka kurin yake Jin son kasancewa da ita, hakan yana sashi tsintar kansa cikin farin ciki.


Cafeteria suka nufa duk inda suka wuce binsu ake da kallo kawai bama ynxu da mutane sosai suka fito, ko a jikin sa da yadda ake kallon su don shi baya son shirme.


Kaita yai ta zabi abinda take so bayan ya jido Mata ice cream da chocolate a leda, sosai ta ci abincin da aka kawo mata don tana ganin kaza tace masa ita take so, fried rice da kaza ya karbo mata sai ruwa, zuba mata ido yai yana kallon ta tana cin abincin ta cikin nutsuwa.


Daukar wayar sa yai kawai ya shiga mata hoto sai style take masa tana turo baki suna yi suna dariya, duk students din da suke gurin kallon su suke suna mamakin dama Mr Azlan yana Wasa da dariya haka.....








**********


Hawayena na goge na kalli Asma'u nace "kina gani har ynxu yaki dawo min da yarinya ta fa Asma'u"


Dafa ni Asma'u tai tace "ki taso muje office din nasa toh mu duba mu gani, amma dama ya san kune?"


Girgiza kai nai cikin nadamar zuwa da Mimi nace "ina fa ya san mu kawai kalan dangi ne ni ban taba ganin Saba ma Sai a school

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login