Showing 45001 words to 48000 words out of 94393 words

Chapter 16 - TASWIRAR KADDARA BOOK COMPLETE PDF .txt

Advertisement

Mrs A.M   

03 Aug 2024

17025

abinda ya faru a gidan baffa, Sawa Abba yai aka Kira masa Batul sannan yafada musu komai har ma da auren da suke so a basu na Batul


Da sauri Batul ta kalli Abba tana hawaye tace "Abba aure na kuma?"


Daga kai Abba yai yace "hakan shine rufin asirin mu da na Mimi, zata tashi tare da mahaifin ta kema baki da fargabar komai akan dangin mijin ki wata ran zasu iya miki gori"


Kuka na fashe dashi nace Abba "don Allah kayi hakuri wallahi na tsane sa"


Shiru Abba yai yana tunani kafin ya kalli Umma data ke kallon Batul kamar ta make ta murmushi kawai yai yace "tunda baxa ki iya ba Batul, Aisha ke zaki aure sa?"


Da wani irin sauri Batul ta dago ta kalli Abba kirjin ta na wani irin bugawa tace "Aisha kuma Abba sai ta auri Mr Wicked?"


Gyada kai Abba yai yace "tunda ke baxa ki iya auren sa ba Batul ina jin kunyar nace ma tsohon baxan iya basa jinina ba sai na bawa Aisha kawai"


Mikewa nai ina kuma fashewa da kuka na shige daki, dukkan su da kallo suka bini sannan Abba ya kalli Umma, ciro wayar sa yai yace ma Yusuf yana son ganin sa, mikewa yai yace ina zuwa ku jira ni anan Zan dawo na muku bayani.


Yusuf bai dau lokaci ba ya iso, tare da Abba suka tafi babban gida sun dade suna tattauna wa kafin Abba yace "zan fada ma lokacin da za'a tsayar da ranar bikin sai Ka fadawa magaba tan Ka, tunda so nake a hade bikin gaba daya kuma Aisha bata gama secondary school ba wannan shekarar dai zata gama"


Sunkuyar da kai Yusuf yai cikin kunya yace "ngd sosai Allah ya kara girman"


Mikewa yai ya fita fuskar sa dauke da murmushi, sai da suka kara tattauna wa sannan Kawu Nasir ya Kira ya fada ma Baffa sun yadda sai dai kuma ga abinda Batul din tace shima dai sun dade suna magana kafin ya kashe.


Ajiyar zuciya Abba ya sauke yace "Alhamdulillah"


Da ya koma gida har lokacin Umma da Aisha suna zaune sai maida maganar suke, Zama yai ya musu bayani gwari gwari sannan ya umarci Umma ta same sa a daki da kwai maganar da zasu karasa.


Ran Umma fess ta bi bayan Abba Jin ta take cikin farin ciki auren Yaya Mata biyu lokaci daya ba tare data kawo ba, gasu tana aurar dasu ba wata a gabanta ai abin a mata murna ne.


Ina kwance sai dai na daina kukan sai tunanin wai Abba zai bawa Mr Wicked Aisha ne kawai yake damuna a raina.


Dagowa nai jin shigowar Aisha, kallon ta nai naga sai murmushi take da sauri na mike nace Aisha wallahi kar ki yadda mutumin nan ba na kirki bane mai zaki yi da shi Allah kar ki soma yadda


Zama Aisha tai ta juya idonta tace "Ya Batul me yasa, yana kama da Mimi fah sosai baki gansa ba mai kyau in na same sa matsayin miji ai na haye wallahi."


Tsaki nai nace "baki da hankali ke ana maganar hankali kina wani hauka meye kyau kuma, dallah ki nutsu ki gane mana bashi da hali mai kyau Dan iska ne"


Da Sauri Aisha tace "nidai Ya Batul ki daina iskanta min shi, kuma Abba har sun Kira Baffa sun fada masa cewa ke kince a'a amma ni sun bashi ni"


Da sauri nace "Mai Baffan yace"


Murmushi tai tana janyo dankwalin ta tace "murna sukai sukai godia, Abba ya fada musu dai kema dama da wanda kike so sai a hada bikin lokaci daya"


Zaro ido nai nace "ni kuma waye Wanda nake so din?"


Kallona tai da mamaki tace "Ya Yusuf mana, Abba ma ya fada masa shima ya shirya ina gama secondary school za'a yi biki ynxu dai zasu tsayar da rana kinga saura wata 5 mu fara WAEC lokacin kema kin gama second semester dinki kawai sai musha biki"


Kasa magana nai sai binta da kallo kawai nake sai iyayi take tana yafa mayafi a kafada irin matan auren nan..








********
Kallon Azlan Mami tai da kansa yake kasa, gaba daya ta kasa yarda cewar Azlan ne zai aikata wannan abun sai dai kuma hujjojun da suka bayyana da kuma yadda ya amsa da kansa yasa bata da yadda zatai.


Mama kuwa ba karamin farin ciki tai ba ko bakomai wano tabo ya shafi Mami jikarta ta farko shegia ce.


Cikin nutsuwa Uncle Mustapha yace "har aure Baffa ya karbo masa na maman yarinyar, duk da an samu matsala amma sun mana bayani yace duk lokacin da muka shirya asa rana."


Cikin fushi Mummy da tunda aka fara maganar take tunanin halin da yar ta zata shiga tace "amma kawai sai a nema masa auren ta, bayan bama ita ce ta haifi yarinyar ba"


Baffa dake kallon ta yace ko "banyi daidai bane uwata"


Da sauri Mummy tace "ba haka nake nufi ba Baffa amma a duba, shi baya ra'ayin auren yarinya kuma tun tuni ake binsa da zancen Xainab yana botsarewa ynxu ya zata ji Baffa don Allah" ta karashe cikin rawar murya.


Shiru Baffa yai yayinda Abie yace "Baffa a duba lamarin gaskia kodan sbd Zainab din kowa yasan tana son Azlan"


Da sauri Azlan yace "Abie don Allah kuyi hakuri wallahi horon ya min yawa taya za'a bani mitsilar yarinya kuma azo ace za'a hada ni da Zainab wallahi hauka zan fara inaga, gurin wa zanje na sauke budurcina....."


Make masa baki Abie yai yace "kar na sake jin Ka ambaci budurci ko ranka ya baci"


Murmushi Baffa yai ya kalli Azlan ya ce "Allah ya baka ikon yin adalci a tsakanin matan naka da Xainab za'a hada ayi auren rana daya zaka angwance da Mata biyu Insha Allah nan da Wata bakwai"














Comments Nd share plz












Mrs A.M🥰


[03/09, 18:26] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️


*TASWIRAR KADDARA*


♠️♠️♠️♠️♠️




Written by
Mrs A.M🥰


Page 25


*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃




*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*




*LOCATION KANO*


08062073990


BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM





Sunkuyar da kai kawai Azlan ya kasa dago kansa ya kalli, kowa.


Kallon sa Baffa yai yana son yai magana don shirun sa tabbas ya bashi tsoro, a yadda yasan Azlan tabbas bai tsammanin zai yi shiru ba.


Abie ma kansa shirun Azlan ya a ynxu ba shi tsoro a yadda yasan danshi ba irin sune ake ma dole ba akan abinda basu da ra'ayi ba amma gashi an bashi mata biyu a rana daya kuma dukkan su ba ra'ayin sa ba har ansa rana amma baiyi magana ba.


Ajiyar zuciya Baffa ya sauke yace "zaki baka ce komai ba"


Sai da yadan dau seconds sannan ya dago idonsa da suka yi wani irin jaa sbd bacin rai, murmushin gefen baki yai yace "mai zance tsoho kun gama yanke hukunci Allah ya kaimu"


Mikewa yai kawai ya fita daga gidan gaba daya...


Shiru palourn yai kafin Baffa ya sallami kowa, bayan ya fadawa Abie ya Kira Abba ya fada masa sun sa nan da 7 months tym din Aisha ta gama secondary.






**********
Wani irin ihu Zeey tai ta fada jikin Mummy tace "Mummy ynxu dai nan da 7 months zan zama matar Ya Azlan?"


Murmushi Mummy tai tace "insha Allah kuwa, matsalar kawai auren da Baffa yace zai masa da waccen shegiar duk da naji baban yarinyar ya Kira yana ma baffa wata magana amma banji ba Allah yasa ma suce baza su bashi auren ba"


Zama zeey tai tace "Mummy ai ni wannan auren da za'a masa sam baya gabana, nasan kowa za'a aura masa baxa ta kama kafata a komai ba don haka kar ma ki damu, kuma ina shiga ciki zamu San yadda zamuyi mu fita da ita."


Murmushi Mummy tai ta shafa kan Zeey tace "dama ai ke nake ji kar ki tada hankalin ki Amma tunda kin kwantar da hankalin ki ynxu kawai zamu shiga gyara kine yadda in ya shiga gonar ki sai ya raina kansa".


Wani juya ido zeey tai tace "yauwa Mummy na shiyasa nake sonki sosai".


Dariya sukai suna tafawa








*********
Tunda abin ya faru gaba daya ba Zama wata suku suku bama dana ji Umma tana gayawa Aunty Bilkisu data zo cewa ansa ranar biki wata 7, ga Aisha ynxu ta koyi wasu kalar hauka bata da aiki sai karatun littafan Hausa, da na mata magana sai cemin tai wai zaman aure take koya da yadda zata Kula da Mijin ta.


Yau sati daya da faruwar abin knn muna zaune a tsakar gida nida Aisha sai Umma, Mimi na daga kofar kitchen tana gera kayan wasan ta wai girki take yi.


Hira muke wanda yawanci Umma ke mana nasiha da yadda ake rike Miji da kuma Kula da jiki da tsafta.


Janyo wayar ta tai tace "bara na Kira Bilkisu ma na tuna mata kar ta manta tace zata je shagon Aunty Baby Mai baby beauty lounge ta karbo muku maganin sanyi, gwanda ku fara sha tun ynxu"(08183462148 or 07058457638 tana saida magungunan sanyi masu kyau da inganci sannan akwai Kayan da'a masu inganci Wanda zasu gigita oga🙈)


Nidai banyi magana ba sai Aisha ce take kallona tana wani murmushi, harara na maka Mata ina jan tsaki.


Shigowa kamal yai dauke da sallama, Zama yai akan tabarmar sannan ya kalli Mimi yace "Mimi Daddyn ki yazo yana waje"


Da gudu Mimi ta taho gun kamal dafa gwiwowin sa tai tace "da gaske Daddy na yazo Ya kamal"


Dariya Kamal yai yace "yana waje ma"


Da gudu ta kwasa tayi waje, ni kuwa da tunda kamal yace Mr Wicked yazo naji wani irin bugawa da kirji na yai sai kawai na saukar da kaina kasa ina duba wayata duk da kuwa ba abinda nake gane wa.


Kallon Aisha kamal yai yace Ya Aisha kije wai yana jiranki


Da sauri na dago na kalli Aisha don Jin wani amsa zata bawa Kamal, sai dai ga mamaki na sai Naga Ka kalli Umma, daga mata kai Umma tai hakan yasa ta mike da sauri ta shige daki, minti kadan ta fito sanye da hijab ta dan fesa turare ta gyara fuskar ta.


Raka ta nai da kallo har ta fice, juyawa nai naga Umma ta zuba min ido tana kallo na, juyar da kaina nai amma ji nake kamar na dora hannu a Ka na fashe da kuka.


Bata dade ba ta dawo fuskar ta a washe sosai, kallon Umma tai tana sosa kai tace "Umma yace wai in tambaye ki in kin yarda zamu rakasa super market nida su khalil da Mimi".


Murmushi Umma tai tace "Allah ya kiyaye in har da su Khalil ne ai baxan hana ba, ko ba komai yayi spending tym da Mimi."


Tsalle Aisha tai cike da murna tace "mun gode Umma bye," kallona tai tace "sai mun dawo Ya Batul."


Da harara na bita har ta fice daga gidan, juyowa nai na kalli Umma nace "ynxu Umma kika barsu suka fita tare da Mr Wicked bashi da hali mai kyau fa Umma kina kallo dai shine mahaifin Mimi"


Kure ni da ido Umma tai kafin tace "Batul ki shiga hankalin ki akan aibata wannan mutumin, ke ynxu in Mimi taji ki zata ji dadi ki sani duk lalacewar Uba, uba ne kuma kar na Kara ji kin fadi wata kalma mara dadi ko ba komai shine zai auri kanwar ki, yau da gobe kuma wataran zata ji haushin yadda kike masa."


Kwalla ce naji tana kokarin zubo min kawai na juyar da kaina ina wasa da wayata.


Ban san mai yasa ba amma tunda suka fita hankali na ya kasa kwanciya bini bini na kalli kofa ko na duba ogoga na.


Sai gab da magriba suka shigo hannun su dauke da manyan ledoji, sai walwala suke.


Nuna wa Umma sukai kayan kwadayi ne ya siyo musu sai kayan wasa dasu teddy daya siyo ma Mimi.


Ledar dake hannun Aisha ta mikawa Umma tace "Umma kinga mai ya siyo min" ta fada fuskar ta dauke da murmushi.


Karba umma tai ta bude iPhone x ce mai kyau golden colour, kallon ta Umma tai tace "ke kika ce ya siya Miki"


Da sauri ta daga hannun ta tace "ba ruwana Umma cemin yai ina da waya nace a'a shine yace amarya kamar ni banda waya ni banma san ya siyo ba sai da muka dawo ya ban yace har SIM ya samin"


Ajiye ledojin Umma tai tace "angode sosai ku ajiye a Palour sai Abba yadawo a nuna masa"


Nidai ko uffan ban ce ba, koda Abba ya dawo aka nuna masa godia yai yace ma Aisha ta Kula da yadda zatai amfani da wayar.


Tunda ga lokacin kullum Aisha tana manne da wayar ta bata da aiki sai chatting da waya, sai kuma zance don ba'a sati ba tare da tai zance ba wataran da Mimi take fita wata ran kuma ita kadai.


Nidai nawa ido amma Allah ya sani ba karamin azabtuwa nake ba, bama in tana waya tana kashe murya ji nake kamar na karbi wayar na rotsa a kasa, nidai bansan mai yasa nake haka ba amma na barshi a matsayin kawai don bana son Mr Wicked ne kuma na tsane sa sbd abinda yai ma Khadija.


Aunty Bilkisu har gida tazo ta kawo mana magungunan sanyi Wanda ta karbo mana a gurin Aunty baby, sosai Umma ta dage akan Kula da yadda muke amfani dashi, don ta hana mu tsarki ma da ruwan sanyi sai na dumi, kuma ta hana mu Shan abu mai sanyi.


Alhamdulillah kam maganin sanyin yana da kyau sosai don muna ganin amfanin sa, ganin kyaun sa yasa Umma itama ta fara sha don tace itama bata tsufa ba in dai gyara ne.


Cikin haka muka koma makaranta, result dinmu yai kyau sosai komawa ta makaranta shi yake dan rage min wani radadin, don tsaf na fita harkar Mr Wicked ko class dinmu ya shigo bana yarda mu hada ido, kuma abinda na Kula shima ya watsar da ni ba abinda ya shafe sa, in yazo abinda ya kawo Shi yake yi ya fita.


Sosai na maida hankali akan karatu na bana wasa, nida Asma'u mun Kara zama kawaye sosai har auren mu na fada mata date din amma ban ce mata Mr Wicked Aisha zata aura ba.


Itama ta dage sai fada min tips din rike miji take yi, sai dau kawai na zuba mata ido ina kallon ta don a ganina Mai zan dauka tunda har ga Allah nidai ba son Yusuf nake ba, ni ynxu ma sai muyi sati bamuyi magana ba dama dama a WhatsApp yana dan mun magana sama sama.


Kwanci tashi gamu yau mun gama exam din second semester Wanda yai saura wata daya bikin, Aisha ma tun wancan watan ta gama WAEC.


A gajiye na isa gida, a Palour na tarar da Aunty Bilkisu da Umma suna magana gyaran jikin sa Aunty baby zata mana gaishe su nai na shige daki.


Kallon Umma Aunty Bilkisu tai tace "munyi magana da ita tace sbd nice a gida zata musu na sati biyu, ga kayan da'a dai na karbo musu masu inganci wadanda za'a basu su tafi dashi gidan mijin."


Ajiye ledar kayan da'ar Umma tai tace "baxa a basu wani ynxu ba knn"


Murmushi Aunty Bilkisu tai tace "Aunty Sadiyya nidai ba ruwana wallahi haka kurin a dura ma Yara magunguna mata azo miji ya musu fata fata, tsumin tsassaken baure kawai xamu basu sai zumar mata sun isa gaskia, sai a musu kaza da Hadin kankana in satin bikin ya kama."


Dariya Umma tai tace "hakan yayi, Allah ya nuna mana lafia, munyi magana da Abba ma akan kayan kitchen, nima nawa Mama magana ina so na siyar da gona ta a hada kudin ayi komai tunda daga kansu na gama kuma, sai na mike kafa na cigaba da kula da mazan"


Sun dade suna tattauna wa kafin Aunty Bilkisu ta shigo dakinmu ta samu a gaba tana fada mana sirrin rike Miji, nidai kaina na kasa sbd kunya don Aunty Bilkisu bata rufe komai, fada mana take.


Wani Abu da Aunty Bilkisu ta fada sai da Aisha ta fashe da dariya, girgiza kai kawai nai ina murmushi duk da bana cikin dadin rai.


Kusan rana daya aka kawo mana lefe nida Aisha, ni akwatuna 12 Aisha 10 kayane masu kyau a ciki da tsada.


Su Uwani da suka zo ganin lefen kamar zasu yi hauka sai sakin magana suke akan aikin banxa abinda ma mazinaci wata zata aura, ba Wanda ya kula Su haka sukai suka tafi.


Ni Kam tun ynxu na fara missing gida da kuma cilla don nasan rabuwa dasu ba abu bane mai wuya.


Sosai hidima ake kusan kullum Aunty Bilkisu damu muna kasuwa gurin siyayyar kayan kitchen, gaba daya na kara ramewa sai boobs da hips tubarkalla.


Mama kuwa gudunmawar turaren wuta da Humra da kolacca ta siyo mana a gurin Maman Sudais (08062073990) lokacin da Mama ta kawo mana sai da Umma ta karbi numbern Maman Sudais din da farko so tai ta diba Mama ta hanata shine ta karbi numbern zata siyo itama don humrar data shafa ranar taji kamalai a bakin Abba😉.


Sati biyu kafin bikin muka fara zuwa gidan Aunty baby gyaran jiki, kwana uku da fara zuwa mu kadai munyi wani irin fresh ba karamin gyara mu take ba har gashin mu turara sa ake, cikin sati daya gaba daya mun chanja duk inda muka gifta sai mun bar kamshin jikin mu Mai sanyi da dadi, gashin mu kanshi kamshi yake.


Duk yadda nake cikin bacin rai da auren nan bama yadda Yusuf baya zuwa zance kuma ynxu bama waya kwata kwata, amma wannan gyaran jikin da aka fara mana ba karamin faranta min rai yai ba, kullum cikin taba jikina nake, munyi fresh sosai Aisha ma tayi kyau sai shakiyanci take wai saura sati daya akai ta gidan miji taji mai ake ji.






**********
Bangaren Zeey ma sosai take Shan gyara gurin Mummy da Mama sai banka mata magungunan mata suke ko maganin sanyi na sati daya suka bata aka shiga banka Mata magungunan mata, gashi ya siyo supplement na Kara kiba sbd ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login