Showing 21001 words to 24000 words out of 94393 words
Chapter 8 - TASWIRAR KADDARA BOOK COMPLETE PDF .txt
wallahi baxa ta Jira umma ba zuwa zatai taga baby"
Dariya nai nace "Allah ya raya sa, amma ALLAH ya shirya min Mimi wallahi ko meye na zumudin"
Dariya ita ma tai tace "Ai ya Batul Baki sani ba rige rige suke ita da Hidaya wai duk Wanda ya fara daukar babyn toh babyn sane kin san su ai da son girma"
Girgiza kai kawai nai nace "mai aka dafa ne don ina Jin yunwa"
Sai da tayi dariya tace "jallof din taliya ce tana kitchen"
Mikewa nai naje na zubo na zauna ina ci muna hira da Aisha har na gama, ina bata labarin Asma'u yau nayi kawa dai finally.
Sai wajen magrib Umma ta dawo ita kadai, kallon bayanta nai bayan na gaishe ta nace "Mimi fah Umma"
Tabe baki tai tace "taki dawowa wai bata gama ganin babyn ba ni kuwa na kyale ta tunda zaku shiga sai ku dawo tare"
Daga kai nai nace "dama mu jiran ku muke amma mun shirya bara mu shiga kafin Abba ya dawo"
Hijab dina na gyara muka fita nida Aisha zuwa gidan Maman hidaya, acan muka sami Mimi kuwa ta kankame ita da Hidiya sun kafa sun tsare duk wanda ya dau babyn sai sunje sun makale shi suna leka babyn.
Zama mukai bayan mun gaisa ina wa Maman Hidaya sannu, karbar babyn nai ina kallon sa Allah ya zuba min son Yara sosai a zuciya ta, murmushi na saki na dago na kalli Mimi data zubawa yaron ido itama.
Dagowa tai ta kalle ni tace "Maa Nima ki siyo min baby irin wannan"
Kallon ta nai gabana yana faduwa ynxu kullum zan kalli Mimi sai fuskar Mr Wicked ta fado min a rai, dan murmushi nai nace "ba ga shi ba Mamn Hidaya ta siyo muku"
Make kafada tai tace "Maa wannan brother dn Hidaya ne kinga maman tace ta siyo mata kuma a gidan su yake, nima ki siyo min nawa sai ya ringa kwana a gidan mu kina goya min Shi"
Aisha dake sauraran mu tayi dariya tace "Ya batul sai ki shirya siyo na shalelen ki baby don tunda ta fara wannan maganar nasan kullum sai ta ishe mu akan zancen baby"
Banxa nai musu na maida hankali na gurin maman hidaya muna hira, muda muka ce zamu tafi da wuri dai gamu har 9, sallama mukai Mata bayan munyi maganar ni zan Mata snacks da drinks na suna.
Koda muka koma gida Mimi cika ma Abba kunne tai da labarin sabon baby, marairaice wa tai ta kalli Umma tace "Umma nace Maa ta siyo min baby tace baxa ta siyo ba toh ke ki siyo min kawai"
Dafe kirji Umma tai tace "ni kuma Mimi da tsufana"
Daga kai Mimi tai tana mar mar da ido tace "Uhm Umma kawai ke ki siyo min zan dinga ma babyn wasa"
Kallona Umma tai tace "tab wannan aikin sai dai Maa din taki amma bani ba ita dai zaki sa gaba ko zata maida hankali ma ta fara kula manai manta"
Hade rai nai na kalli Abba nace "Abba kaji Umma zata fara koh"
Murmushi Abba yai yace "gaskia take fada miki Batul, ni kaina maganar da mukayi da Yakumbo knn yau tace ya kamata ki maida hankali a kan masu zuwa neman auren ki, kullum girma kike sake yi"
Kokarin maida hawayen nake nace "Abba ni baxan yi aure ba, baxan rabu da Mimi ba kuma bana son tai agolanci azo ana mata gori"
Salati Umma ta saki tace "kice so kike ki tsufa a gida muna goga kafada, in an shigo a rasa wace matar gidan wace yar gidan koh Batul, wai yaushe xakiyi hankali ne maganar Mimi dama wani yace zai raba kune"
Abba ne ya karba da fadin kuma baga Yusuf ba yaron nan ya yadda da Kaddara yace Shi ahaka yake sonki kuma zai rike Miki Mimi kamar Shi ya haife ta amma kinki sauraran sama gaba daya"
Cikin rawar Murya nace Abba taya zan saurari Yusuf shin kun manta waye Yusuf Abba, saurayin..... Sai kuma na fashe da kuka ina rungume Mimi a jikina, sosai nake kukan wanda hakan yasa Mimi fashewa da kuka itama tana rungume ni sosai......
Kuyi hakuri da wannan na fita ne kawai na muku typing nema😊
Comments Nd share plz
Mrs A.M🥰
[18/08, 02:50] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 13
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Shiru su Abba sukai kawai suna binta da kallo ganin kukan da take, ni kuwa sai da naga Mimi tana kara volume dn kukan ta sannan nayi shiru na goge hawayena ina rarrashin ta cikin lokaci kankani tai bacci.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke yace "Batul bawai muna son takura ki bane ko mun gaji dake, a'a kawai muna son ki samu farin ciki ne kema Yusuf ya yadda da dukka abinda ya Faru yace zai aureki kuma zai rike Mimi, ba dama shine damuwar ki ba?"
Shesshekar kuka kawai nake na kasa magana taya Abba suke tunanin ma wai Zan iya auren Yusuf, ai baxan taba wannan cin amanar ba.
Tsaki Umma tai tace "kai ne kake lallaba ta Abba, ai ita ba yarinya bace shekara 19 zata shiga sa'annin ta sun fara aure suna zaune dakunan mazajen su, amma ita tana nan tana shirmen baxa tai aure ba, nidai a matsayina na Mahaifiyarki ina baki shawara daki zauna kiyi tunani da kyau, har yaushe zaki cigaba da zama da tabon dake cikin zuciyar ki?"
Lumshe ido nai kawai ban yi magana ba, Dan murmushi Abba yai yace "baxan Miki dole ba Batul, amma ta bakin mahaifiyar kine ki zauna kiyi tunani Allah ya zaba Miki abinda yafi alkhairi, zan bawa shi Yusuf din numbern ki kuna gaisawa"
Daga haka ya kalli Umma yace suje su kwanta, na dade a zaune a gurin kafin na mike na dau Mimi na shiga dakin mu, kwantar da ita nai na Mata addu'a na zubawa Aisha ido dake bacci.
Nima kwanciya nai na lumshe idona ina tunanin shin su Abba basa jin kamar cin amana zanyi in na auri Yusuf?
Shiru nai na dade ina tunani ganin kwakwalwata tana daukar zafi yasa ni mikewa naje nayi alwala nazo na tayar da sallah ina neman zabin Allah akan wannan al'amarin daya danno kai cikin rayuwata.
**********
Shan fruit dinsa yake hankali kwance yana kallo, dagowa yai a karo na uku ya kalli Zainab data ke kaiwa da komawa tunda ta gansa a Palourn tana sanye da English wear riga da skirt da suka kamata, sai turo kirji take tana wani karairaya kamar zata karye.
Maida dubansa gurin Mami yai ta dago itama ta kalle sa, murmushi yai yace "Maa wai ni ake son a yaudara ake wani ciko ana turo kirji"
Kama baki Mami tai ta dan saci kallon Zainab data fito daga kitchen hannun ta rike da cup, maida dubanta gurin Azlan tai tace "ban gane ba"
Murmushin gefen baki yai ya dan sosa bayan kunnen sa yace "turo ta uwar tai tazo tana ciko tana karairaya sbd nace mata kwaila ce ta min yarinya bata san ina gane ciko bane hala"
Girgiza kai Mami tai tace "wai yaushe zaka nutsu Ka rage rashin kunya ne Azlan"
Waro idonsa yai sosai yace "Maa wani abun nai kawai fa gaskia na fada"
Girgiza kai Mami tai tana masa addu'ar shirya a zuciyar ta.
Cikin fushi zainab data gama Jin komai ta shige dakin da aka sauke a Palourn ta rufe kofa, gaban mudubi taje ta zubawa kanta ido tasha heavy makeup sosai duk sbd ta birge sa gashi yau bra har 3 tasa Ashe ya gane ciko tai.
Cikin bakin ciki ta fashe da kuka, tunda tazo gidan basu hadu ba sai yau kamar yasan tana nan baya shigowa sai ya daidaici bata nan, gashi ita gaba daya zaman gidan ya gundureta bata wani sakewa, da sassafe take fita gidan kawayen ta suyi ta yawo joint joint suna chilling sai ta kwana ta yini ma basu hadu da Mami ba.
Wayar ta ta janyo dan kiran Mummy sbd ta gaji so take ta koma gida gaskia, asan kuma yadda za'a yi tunda wannan hanyar da suka dauka tun ba'a je ko ina ba ya gane.
A Palourn kuwa Azlan ajiye bowl din da yake shan fruit dn yai ya kalli Mami yace "Maa in tambaye ki don Allah"
Maida hankalin ta Mami tai gunsa Jin yai magana cikin nutsuwa sosai kamar ba Azlan ba, ajiyar zuciya ta sauke tace "ina Jin Ka"
Sai da ya dan yi shiru na kamar 2 minutes sannan yace "mai yasa wasu suke sa hijab kullum ne wai Mami basa jin zafi suna yawo da hijab dogo har kasa kullum a cikin rana"
Bin sa da kallon mamaki Mami tai tunda take da Azlan bai taba mata maganar abinda ya shafi Mata ba ko kuma yanayin shigar su ba, ganin kallon da take masa yasa shi fadin "shiknn ma"
Murmushi Mami tai tace "Hijab mutunci ne ai Azlan, kuma musulunci ma ya umarci mace data rufe jikinta kawai ba'a amfani da koyarwar musulunci ne amma duk wadda kaga tana sa hijab tana yi ne dn rufe jikinta da kuma killace jikinta, abinda matan ynxu basa ganewa ita mace Mai DARAJA ce ZAKI bai kamata komai nata a same sa a arha ba"
Ruwa tasha tana kallon yadda ya mai da hankalin sa sosai kanta yana sauraran ta hakan yasa ta cigaba da fadin "dukda ynxu wasu suna amfani da hijab dn gurin fitsara sai kaga yarinya tasha dogon Hijab har kasa amma da zaka bude hijab dn tsirara take amma ba duka aka xama daya ba, Shi Hijab rigar mutumci ne kuma ana ma duk Wanda take yawan sa shi tana rufe jikinta kallon Kamila."
Gyada kai yai ya juya, murmushi mami tai tace "amma dai mai yasa Ka tambaya Zaki"
Dan tabe bakinsa yai yace "wata fitsararriyar yarinya ce take sashi kullum na ganta dashi nake ganin ta, amma abinda yake ban mamaki meyasa mara kunyar yarinya zata dinga sa hijab a university kullum, kowa dai yasan bata da kunya tunda bata ma yawo da Mata sai Maza kullum zaka ganta ita da wani gardi a gefen ta sun jera suna tafiya," sai kuma yai tsaki ya kalli Mami yace "wai uwar dakina gardin yake ce Mata fa katon saurayi yana fadawa karamar kanwar sa uwar dakina ita kuma amsawa"
Murmushi kawai Mami take zatai magana Junaid da tunda Azlan ya fara magana ya shigo ya tsaya yana ji yace "Wace mai sa'ar ce wannan datai tsaye a xuciyar mazage har yake maganar ta yau, Mami da gaske ne abinda kunne na ya jiyo min yau Azlan ne yake maganar wata mace gaskia yau ranar ta musamman ce har sadaka zanyi Ashe dai aljanar da muke xargin ta aure Ka ta sake Ka"
Kallon Junaid yake yana kankance idonsa yace "Junaidu yaushe na fara wasan banxa dakai?"
Kama baki Junaid yai yace "wai Azlan nida kai waye babba ne?"
Mitsi mitsi yai da idonsa har ya bude baki zai magana kawai kuma sai yai shiru ya janyo lip dinsa na kasa yana tsotsa ahankali.
Murmushi Junaid yai ya zauna a kasa kusa da kafar Mami suna gaisawa, juyawa yai ya kalli Azlan daya hade rai yana kallo yace "Zakin Baffa yaushe zaka zo gidana ne wai kaci abinci, kullum sai Samira tamin korafi akan baka zuwa Ka daure kazo don Allah ko weekend ne"
Juyowa yai ya zubawa Junaid idonsa daya sha kwalli sai sheki suke kafin yai tsaki yace "Allah ya kiyaye naje gidan kanwata cin abinci sai kace wani mayunwaci zaka ce nazo gidan Ka cin abinci"
Girgiza kai Junaid yai yace "koma meye ai ta zama yayarka tunda tana auren yayanka ko?"
Mikewa Azlan yai ya kalli Mami yace "Maa bara naje gurin Abie ina son magana da shi, sannan ki dinga ma min addu'a sosai MAA plz ana kawowa budurcina hare hare sosai"
Daga haka ya sa kai ya fita daga palourn, yana takunsa cikin jarumta, binsa da kallo dukansu sukai kafin Junaid ya kalli mami a tare suka saki dariya...
Part din Abie ya nufa don yasan ynxu haka yana gida, sai da ya tsaya yai knocking kofar aka basa ikon shiga sannan ya shiga, Abie ne kawai a Palourn sai Mama a gefensa tana hada masa tea.
Karasowa yai ya zauna a kan kujerar dake kallon ta Abie yace "Ina wuni"
Binsa da kallo Abie yake yana karantar sa yace "lafia qalau ya aikin"
Gyada kai kawai yai ya kalli Mama da tun shigowar sa ta maida hankalin ta kan abinda take yace "Evening Hajia"
Dan dagowa tai ta daga masa kai kurum ta mikawa Abie tea dinsa tana gyara zaman ta don ba inda zata je zama zatai duk abinda zasu tattauna itama ayi agaban ta taji.
Jin yaki magana yasa Abie fadin "Ina sauraren ka"
Dagowa yai ya kalli Abba yace "so nake nabar lecturing din da nake don bana jin zan iya Abie"
Jinjina kai Abie yai shidama yasan ba'a banza ba Azlan zai shigo gurinsa saidai in wani abun ne, ya dan Jima yana nazarin sa saidai ba alamar ko da Wasa yake dukda dama yasan in har zaiyi magana toh da baya fada da Wasa iya gaskiar sa yake fada.
Gyada kai Abie yai yace "ko Zan iya sanin dalilin dayasa kake son barin lecturing din?"
Kai tsaye yace "fyade ake son min yau saura kadan wata ta rabani da budurcina da kyar na sha"
Sunkuyar da kai Abie yai yana shan tea din sa yayinda Mama ta shiga girmama lamarin rashin kunyar Azlan wai fyade aka kusa masa.
Dagowa Abie yai yace "dama ana yiwa namiji fyade ne Azlan"
Gyara zaman sa yai yadan lashi jajayen lips dinsa yace "sosai ma tunda naje makarantar nan Mata suke kawo min hari, sai suna shiga ta banxa suna zuwar min office da sunan wai Zan koya musu abu basu gane ba ko kuma kai tsaye su aiko min da letter wai suna Sona"
Shiru yai ya kalli Abie ganin Shi din Abie yake kalla yasa shi fadin "yau wata shigo min tai cikin masassun Kaya ya bude Rabin kirjin ta haka ta janye mayafi kuma ta sunkuyo yadda in na dago dole idona zai fada cikin rigar ta, ina dalili ina da lafia fa Abie don banyi aure ba bawai hakan na nufin ina da nakasu bane lafiyayyan namiji ne ni toh shiyasa tun kan wataran sufi karfina su hadu su lalata ni na shiga uku nace xan yi resigning"
Murmushi Abie yai yace "mai yasa kai baxa Ka dau mataki ba da kanka"
Shiru yai don ya fuskanci Abie bawai xai goya masa baya bane gashi yai wa Baffa alkawarin baxai yi resigning ba sai da izinin Abie.
Mikewa kawai yai ya tura hannun sa cikin aljihu yace "sai da safe"
Binsa da kallo Abie yai yace "Allah ya cigaba da tsare min kai"
Tabe baki Mama tai ta juya keya tana kallo, itafa iskanci Azlan yana isar ta komai budurci ta rasa gidan uban waye yake da budurcin, bayan kowa sheda ne akan rashin jinsa da yadda yake zuwa club duk dare..
********
Washe gari da ciwon kai na tashi hakan yasa Abba cemin na kwanta basai naje makaranta ba, Asma'u na Kira nace don Allah tamin attendance baxan samu zuwa ba banda lafia, sosai ta nuna damuwar ta har tace da zata biyo in an tashi nace mata da sauki ai ciwon kan kafin muyi sallama.
Ina kwance a daki ina kallon Aisha dake shirya Mimi don bana Jin zan iya shirya ta da kaina sbd yadda kaina yake min ciwo, tun ina kallon su har bacci ya dauke ni bansan yaushe suka tafi ba.
Ban tashi ba sai karfe 11 saura, a hankali na mike ina mika duk jikina ciwo yake min kodan sbd baccin da bana yi ne na safe yau kuma na samu nai.
Fitowa waje nai banga Umma ba nasan tana dakin ta, wanka nai ma shirya cikin simple riga na dauki breakfast dina ina cikin ci naji wayata tana ringing, banxa nai da ita ganin sabuwar number sai dai kirin da aka sake yi ne yasa ni daga wayar.
Ciki ciki na yi sallama muryar data amsa nice tasa gabana faduwa, daure wa nai nace "waye yake magana"
Daga dayan bangaren aka ce "Yusuf ne........"
Wai shin waye wannan Yusuf din ne🤔🤔
Mai yasa Batul bata son ta aure sa shin amanar waye zata ci da take cewa in ta aure sa taci amana🤔🤔🤔
Comments Nd share plz
Mrs A.M🥰
[18/08, 18:39] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 14
Dedicated to Mufeeda🥰
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Sai da gabana ya buga da karfi amma na tattaro nutsuwa ta nace "ina kwana Ya Yusuf"
Ina Jin sautin murmushin Shi cikin nutsuwa yace "Lafia qalau ya jikin Baba yace min baki da lafia"
Ajiyar zuciya na sauke nace "da sauki Alhamdulillah"
"Masha Allah, Allah ya kara sauki yasa kaffara ne"
A hankali nace "Ameen"
Shiru mukai dukan mu, shine ya ce "sai anjima tohm Allah ya kara sauki kiyi saving number ta kinji zan Kira anjima Insha Allah"
"Toh" kawai nace na kashe wayar dagowa nai idona suka fada cikin na Umma da ke tsaye a kofar dakin su tana kallona, marairaice fuska nai amma tai banxa dani ta wuce kitchen.
Kwana na biyu bana zuwa makaranta sbd ciwon kan dake damuna, saukin tama duk abinda kai Asma'u tana turo min kuma tana min attendance, a kwana biyun nan kuwa Yusuf ya taso ni gaba da Kira, don jiya ma sai da yazo dubani nidai ban fita ba kwanciya nai nayi lambon bacci sai Aisha ce taje ita da su Kamal suka gaisa ya basu leda Mai dauke da kayan kwalam su bani.
Yau da wuri na shiga makaranta kasancewar jikin nawa da sauki sosai, a hankali nake tafiya ina sanye da hijab dina kamar kullum dark blue ba rataya jaka a kafada ta, cikin sanyin jiki nake tafiya nayi nisa a tunani kawai naji na bangaji mutum, da sauri na dago ganin waye na bangaja a tare kirjin mu ya buga.
Zuba mata ido yake yana kallon ta kwana biyu knn baya ganin ta, tun shekaran jiya daya shiga musu lecture har yai ya fita bata zoba kuma jiya ma yana lura da abokin ta Shi kadai yake yawo a school Banda ita hakan ya tabbatar masa da cewa bata zoba knn don da tazo da zai gansu tare.
Nima zuba mishi ido nai ina kallon sa sai kuma na turo baki na kauda kaina gefe, ciki ciki nace "Good Morning Sir"
Maimakon ya bani amsa