Showing 9001 words to 12000 words out of 94393 words
kirani da baka ba kuma bana cikin jerin farare, kuma bankai Mimi manyan ido ba don idona madaidaita ne, hanci ne kawai za'a dan iya kamanta mu shima don dukkan mu muna da dogayen hanci ne amma ni nawa hancin yafi na Mimi siriri, sai lips inda na Mimi suke sirara kuma kananu nawa kuma madaidaita ne kuma suna da dan tudu kadan sannan a zagaye suke, ko gashin kai nawa da nata ya banbanta ni nawa kana gani zaka ga gashin mune na hausawa dai dai misali, nata kuwa yawansa da tsantsin sa yafi kama dana larabawa.
Maganar kyau kam nasan Mimi ta fini kyau nesa ba kusa ba kuma ba inda ta dakko ni, Murmushi nai kawai ina ja mata hular ta data zame sai kuma na hade rai ina jawa kowa ye mahaifin Mimi Allah ya isa don haka ya zamar min jiki in har zan kalli Mimi sai na tsinewa Babanta, ina wadannan tunanin har bacci ya dauke ni....
Asuba ta gari Batul🥱
Comments Nd share plz
Mrs A.M🥰
[09/08, 17:45] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 6
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Washe gari tare muka fita nida Mimi sai da na fara rakata har makaranta sannan na fito don karasawa tawa school din kasancewar 9 ina da paper, a hanya na hadu da cilla yana gani na na tsaya yana sosa keya.
Harara na maka masa kafin nai gaba don haushin sa nake ji shekaran jiya nai ta kiransa yaki daga wayata, kuma bai kirani back ba har ynxu(Hajia Batul yada karfin hali haka)
Dan sauri yasa ya dawo gefen ta amma dan nesa da ita yadda kusancin su bazai yawa ba, cikin muryar katuwar muryar da yace "haba Uwar dakina kiyi hakuri wallahi wayar tawa bata hannu na kika kira kuma dana karbi wayar zare sim dina nai naje na siyar da ita ynxu dai wata sabuwar nake son siya"
Wani kallo na watsa masa da idanuna masu matukar kalli da sheki kafin na tabe bakina nace "toh ynxu daka min wannan tambayar na tambaye kane"
Murmushi yai yana kallon ta daga dukkan alamu yau Yan miskilan cin ne a kusa da mutuniyar tashi gwara ya lallaba ta su rabu lafia, cikin kwantar da murya yace "ina so na kiraki tun jiya inji nawa kika samu a Jamb din ki naji an saki result"
Sai lokacin nadan saki fuskata ne nace naci "Alhamdulillah 228 na samu"
Murmushi yai yace "barka uwar dakina nida ma nasan insha Allah zaki kwashe ta ai kedin ta daban ce"
Girgiza kai nai nace "kai nawa Ka samu"
Shafa kansa yai dayai masa askin samarin zamani yace "184 na samu"
Dan tsayawa nai da tafiyar da nake na juyo na kalle sa nace "don Allah fah"
Dariya yai yace "wallahi da gaske nake Nima nayi mamaki na dauka fa irin 40 dinnan zan samu AI da aka duba min a cafe da farko kin yadda nai sai da mutane da yawa suka duba aka tabbatar nawa ne sannan na yadda"
Dariya nai nace "Alhamdulillah baka ji yadda naji ba tun jiya dama nake tunanin Kai nawa Ka samu don ina fatan mu shiga school dinnan tare muyi komai tare bana son shiga shirgin mutane kar ma a raina Ka"
Dariya cilla yai yana gyada kai yace "Allah ya taimaki Uwar dakina"
Nidai banyi magana ba har muka karaso bakin titi, kallon sa nai nace "Ka gaida Baba kace mata zan shigo Insha Allah anjima in na dawo"
Daga min kai yai yace "kamar kinsan kuwa jiya ta gama min maganar kwana biyu bata ganin ki nasan zata ji dadi sosai in na fada mata"
Sallama nai masa na karasa makaranta, binta da ido Cilla yai yana matukar ganin girman Batul kaf layinsu ita ta fara masa kallon mutum mai mutunci kowa a matsayin Dan iska ya dauke sa sbd yanayin shigar da yake da kuma irin maganar sa don da ya taba dabanci har taba yana sha, fara shirinsu da batul ya rabu da dabancin da yake ya kuma daina shan taba, da taimakon Abbanta ya sama masa aiki a wani garagi, shiyasa har Mamansa take mutunta lamarin Batul din.
Shi kadai ne wanda Batul take gani a matsayin Aboki don ko lokacin da KADDARA ta fada mata bai taba gazawa gun tausar taba shiyasa shima bashi da aminiya irin ta komai nasa ta sani, ynxu haka tare suka rubuta Jamb din wanda Saida batul tai masa karamin hauka sannan ya yadda ya rubuta dama yana da waec dinsa tare suke son shiga university sai dai kowa da course din da yake son karanta.
Koda ya fadawa Mamansa ra'ayin sa na son komawa makaranta ba karamin murna tai ba don ba yadda batai da shi ba amma fafur yace shi baxai wani karatu ba don kwakwalwar sa bata daukan komai sai gashi shima ya samu jamb din, bashi da matsalar kudin Makaranta tunda yana tarawa a banki kuma mahaifiyar sama tana Sana'a sosai Alhamdulillah suna da rufin asiri daidai gwargwado.
Murmushi yai yana mamakin son girma irin na Batul a kalla ya bata shekara 7 don shi shekarun sa 25 amma ta maida Shi kamar kanin ta, girgiza kai yau yace "Allah ya nuna min ranar da wani da wani zaiyi wuf da zuciyar ki in aurar dake don ranar hadda ni a masu Kai amarya ai ba Zama aminiya guda tana aure"
**********
Cikin takunsa na cikakken namiji ya fito daga dakinsa yana gyara neck tie dinsa, kusan karo suka kusa ci da Abie da sauri yai baya yana Dan kau da kansa.
Da mamaki Abie yake Kallonsa ganin sa sanye da suit ash colour da tai matukar amsar jikinsa, kallon agogon sa Abie yai kafin ya maida dubansa gurin Azlan yace "lafia kuwa naganka cikin shigar nan kuma zaka fita da sassafe"
Da dan mamaki Azlan ya bi jikinsa da kallo sai kuma ya saki wani munafikin murmushi yace "Lau Abie office zani"
Ware ido Abie yai yace "office kuma dama kana zuwa office har ynxu neh"
Wannan karan sai da ya dan gyara tsayuwar sa yana zuwa hannunsa cikin aljihun sa yace "ina zuwa mana Abie sai dai ba kullum ba sai ta zama dole ynxun ma wani zane ake so nayi na wata makaranta shiyasa zanje Amma ina gamawa zan fece"
Gyada kai Abie yai sai kuma ya kalli idon Azlan daya sha kwalli rambadadau yace "toh shi kwallin zaka office ma sai Ka sashi wai ni ban gane maba meye amfanin wannan kwallin ne"
Cike da shakiyanci ya kankance idonsa ya janyo lip dinsa na kasa ya kasa sannan yace "na farin jini ne Abie kasan na gaji da rungumar pillow shine nake sawa ko zanyi budurwa Nima Ka aurar dani na danka mata budurcina don naga magauta sun fara kawowa budurcina Hari"
Sakin baki Abie yai kafin ya girgiza kai yace "ynxu duk yan matan da suke sonka ko acikin yan uwa ne basu ishe Kaba sai Ka wani sa kwalli ga yar uwar Ka Zainab kowa yasan irin son da take ma amma kayi banxa kamar baka san me take nufi ba"
Shafa kirjin sa yai yace "Abie basu min ba duk kwailaye ne ita kuma Zainab din inaji kirgan dangi ta fara ne ko yaya ne gata a tsaye kamar sanda ba gaba ba baya ynxu fisabilillah Abie in na aure ta a wani kirjin zan dinga kwanciya maimakon na kwanta naji laushi saidai naji kasusuwa."
Salati Abie yasa kafin ya juya da sauri kamar zai kifa ya nufi part dinsa yana salati wallahi Azlan ya fi karfin sa ynxu har shi zai tara yana ce masa kwailaye waye da waye..
Shi kuwa Azlan murmushi ya saki yace daidai nake da ku Allah baxan auri kwaila inzo ina taga taga ba na fison naji komai dumi dumi abina haba.
Part din Mama ya nufa don zai karbi wayar sa da Mufeeda ta karba jiya wai xatai hoto Shi yama manta bai karba ba, yana zuwa ya tura kansa cikin dakin yana sallama kasa kasa, Mama ce kawai zaune tana Shan tea tana ganin sa ta gyara zamanta tana dan hade rai.
Dafa kujera yai ya dan daidaita tsayuwar sa yace "Hi Morning Hajia"
Kallonsa tai takaici kamar zai kashe ta ta rasa me yasa Sam Azlan ya raina ta wai Hi Morning Hajia, gyada kai tai tace "lafia"
Shiru yai ya zuba mata lumsassun idonsa yana kallon ta shidai baxai ce komai ba saita tambaye sa, dagowa yai caraf suka hada ido ya zuba mata idon nan nasa da suke matukar tsorata ta, sanin baxai magana ba tunda yai hakan yasa ta fadin "wa kake nema ne"
Agogon sa ya kalla ganin tym na gudu yace "Mufeeda"
Yana tsaye Mama ta kwalawa mai aikin ta Kira tana zuwa tace taje ta cewa Mufeeda tazo inji Azlan, basu dade ba suka dawo Mufeeda na baya tana sanye da kayan bacci hannunta rike da wayar sa.
Cikin girmamawa tace "Ya Azlan Good Morning kayi hakuri wallahi jiyan bayan na gama sai kuma battery din yai kasa shine na Sama charging kuma na manta ban kawo maba"
Karbar wayar yai yace "bana hanaki yawan rantsuwa ba"
Marairaice wa tai tace "kayi hakuri baxan sake ba na manta ne"
Bai ce komai ba sai kallon Mama da yai ya daga mata hannu alamun bye ya fita yana takun sa cike da jarumta, yana fita gurin motar sa ya nufa ya shiga da wani mugun guda yaja ta yabar gidan don ana jiransa a jiya aka basu contract din ginin makarantar da gwamnati zata gina kuma shi ake son ya zana..
Tafiyar minti 10 ta kaisa companyn sbd gudun daya keyi, yana zuwa bai ko tsaya amsa gaisuwar mutane ba ya nufi office dinsa dake hawa na 2, katon office ne mai dauke da doguwar kujera ta hutawa sai kujera da table dinsa a gaban table din kujeru biyu ne da baki suke zama akai ga kofar toilet dinsa a gefe shima gefe daya fridge ne dan madaidaici office din ba abinda yake sai kamshi.
Gurin wani katon shelf ya nufa dake dauke da manyan littafai, tura shi yai sai yai baya daki ya bayyana, shiga ciki yai yana bin ko ina da kallo dakin zanen sane anan yake Zane in yana office cikin nutsuwa ya dauko duk abinda zai bukata na zanen makarantar da zaiyi so yake kafin ya bar office yau ya kasance ya gama zanen, remote din AC ya dauka ya kure ta sannan ya sassauta neck tie din sa ya zauna, janyo wayar sa yai ya kunna suratul Bakara cikin kira'ar Sheik sudais cikin nutsuwar da ban taba ganin sa da shi ba ya shiga bin karatun cikin kwarewa da bawa ko wane harafi hakkin sa a hankali ya dauki Pencil yai bismillah ya dora akan paper ya fara xaneeee.......
**********
Cikin Amincin Allah mun gama waec Lafia sai fatan result yai kyau, tunda muka gama na maida hankali kan sana'ata sosai don ynxu har doughnut nake yi a fitar min da shi, ga kuma kunun Aya da zobo na.
A tsakanin lokacin nan na shiga tahfiz weekend da safe ina so kafin na samu admission na haddace izu 10 tar a kaina, sosai Allah ya Sama Sana'a ta albarka ina ciniki sosai, ganin wani lokacin da yamma ba abinda nake yasa nayi shawara dasu Abba na fara zuwa gidan Aunty Zainab maman shahida koyan dinki tunda tana dinki, AI kuwa dana tambaye ta akan ina son zuwa na fara koyan dinki ckin farin ciki ta amince.
Fara zuwana koyan dinki ya Kara maida ni busy sosai sam bani da ishashhen lokaci ga hadda ina yi, cikin haka result dinmu na waec ya fito, Alhamdulillah naci sosai don A har uku nake da shi.
Haka kuma na fara karatun post utme don Buk na cike ita nake son zuwa fatan dai na samu naci post utme din, tunda ynxu makarantar ma ko kaci wani lokacin danne wa yayan talakawa ake yi a bawa yayan masu dashi.
A hankali hannuna yake kwarewa a dinki na dinkawa Mimi riguna har biyu masu kyau irin na yara...
***********
A xaune yake a kasan carpet ya mike kafafunsa dake dauke da kwantaccen gashi, yana sanye da three quarter da kuma singlet data fito da kirar sa ta cikakken namiji, kallon Junaid yake daya kwantar da kansa akan cinyar Mami yana hawaye gefensa Samira ce tana sanye da abaya kanta a kasa itama kukan take kasa kasa..
Cikin muryar data shake sbd kuka Junaid yace "Mami sunce wai ba lallai naga dana a duniya ba wai wannan aikin da aka min basu da tabbas akan sa kawai sunyi ne sun Dora ni akan magani, ni in nayi hakuri Samira fah ita haka zata rayu baza taga danta a duniya ba knn anya xaman mu ba cutarwa"
Allah sarki Junaidu🥹
Comments Nd share plz
Mrs A.M🥰
[10/08, 19:56] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 7
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Da sauri Samira ta dago ta kalle sa cikin damuwa ta rarrafo ta iso gaban Mami itama, hannun ta ta dora akan na Junaid tace "baxan taba barin Kaba Hub duk halin daka shiga Nima shi na shiga ina kaunar Ka a haka ina sonka sosai"
Murmushi Mami tai tana kokarin mayar da hawayen ta cikin dakewa tace "ku kwantar da hankalin ku yarana Insha Allah za'a dace ma Junaid komai zai zo ya wuce"
Shidai Azlan yana zaune ya zuba tagumi yana kallon shidai har ga Allah baiga wani abun damuwa ba dududu auren Junaidu shekara biyar ne amma ya tayar da hankalin sa sbd ance baya haihuwa ai ya bari ya shekara 20 haka sai ya fara damuwa, Shi Sam yara basa gabansa ma sbd dakinsa suke Shi kuma baya son hayaniya.
Kallon sa Junaid yai yace "Azlan baka ce komai ba Ka zuba mana ido kawai"
Kankance idonsa yai yace "Junaidu mai xance ma toh addu'a kawai zan taya ka Allah ya kara lafia amma in kana bukatar maganin karfi ne kafada min zan nemo ma"
Da mamaki Junaid yake kallon sa Samira kuwa sunkuyar da kanta kasa tai tana mamakin rashin kunyar Azlan hatta Mami sai da taji kunya ta lullube ta.
A kufule Junaid yace "banson iskanci meye haka wai"
Jingina bayansa yai a jikin kujera yana rungume hannun sa a kirji yace "misali in so daya kake yi kaga sai Ka Kara kaimi kana yi kamar so uku haka koh shine kawai kaga in yi dayan ba'a dace ba kasani ko ana biyun a dace don't feel shy Ka fada min zan nemo ma"
Sakin baki Junaid yai fa takaici GA kunya data rufe sa, fahimtar hakan yasa Mami itama ajiye kunyar ta agefe tace "tashi ku tafi Junaid sai da safe Allah yai muku albarka"
A hankali suka amsa suka mike suka fita, da kallo Azlan ya raka su nai bai ce komai ba, maida dubansa ga Mami yai yaga ta zuba masa ido hakan yasa shi sosa keya ya saki wani munafikin murmushi yace "Mami ya kinsani Jin kunya kuma kar ki kawo tunanin komai a ranki Nima kawai nasan ana yi fiye da daya ne amma budurcina lau yake"
Girgiza kai Mami tai tace "Allah ya shirya min kai Azlan ya nuna min ranar da zaka yi aure Ka daina kiran wannan budurci"
Dan tsai yai da idonsa yana kallon ta sai kuma ya tsuke bakinsa yace *"MAA* ynxu in nayi aure shiknn kowa ya daina min kallon Mai budurci knn"
Mikewa Mami tai tana cewa "bara na tafi Azlan baza ka samin hawan jini ba, kuma kar ka manta da akwai taron Family karshen watan nn nasan halin Ka zaka iya kin zuwa"
Shidai rakata yai da ido kawai har ta shige dakin ta sai kuma ya mike ya nufi part dinsa, yana isa ya zauna akan lafiyayyan gadonsa, shifa su Abie sun kasa gane sane baya son mace tazo ta ce tana sonsa yana son mace Mai aji matuka, yana fatan ya ga ranar da wata mace zatai masa duba ba irin na soba, yana son ya kasance ko sonsa zai kashe mace ta ja ajinta taki fada masa har sai in shine ya fada mata cewa Yana sonta, Amma Allah na tuba Mai zaiyi da wata Xainab shekarar ta 24 amma kallon kwaila yake mata sbd duk ciko take.
Shi babbar samuwar Sama ynxu wannan family meeting din da zaka ayi sam baya sonsa sbd wasu dalilai nashi, karamin tsaki yai gashi tunda Mami tace yaje baxai iya musu ba zuwa ya zamar masa dole, kwanciya yai yana lumshe idonsa cikin wani yanayi da yakan shiga.......
********
Dawowa ta knn daga tahfiz a gajiye nake sosai duk jikina ciwo yake min ma, Zama nai a kasan carpet din palourn mu ina mike kafafuna, cikin gajiya na kalli Umma da take duba littafin Seera turo baki nai gaba cikin shagwaba nace "Umma kina kallo na shigo fah"
Banza tamin sai da ta dau mintuna sannan ta kalle ni tace "toh da kika shigo mai zan miki ne ehe in zaki Saba ma gwanda ki saba jami'a zaki shiga tohm"
Nidai ban kuma magana ba mikewa nai na shiga kitchen Dan wake na dora mana, ina cikin yi Mimi dasu Kamal suka shigo Suma saida na gama Dan waken na zuba mana a babban plate muka hadu gaba dayan mu muka ci har Umma, bayan mun gama su kamal ne sukayi wanke wanke ni kuma nai wa Mimi wanka, cikin rigunan dana dinka mata na dauki daya nasa mata sai murna take an sa Mata sabon kaya.
Kallona tai tace "Maa unguwa zamu je kin samin sabon kayan da kika dinka min"
Dariya nai ina taje mata dogon gashin ta nace "a'a babban gida zamu gurin yakumbo kinga mun dade bamu je ba ko Babyna"
Daga Kai tai tana murmushin dake kara wa fuskar ta kyau sosai, hula na samata na rufe Mata gashin ta ruf, kallon ta nai bayan na dafa kanta nai mata addu'a nace "Maza jeki gurin Umma ko su Ya Khalil kuyi hira bari Nima nayi wanka koh"
Da gudu ta fita na bita da kallo ina murmushi, kayana na cire na sa zanin wanka na na fita don wanka, ban dade ba na shigo dakin mu shiryawa nai cikin riga da skirt simple style ne amma sun kamani, a hankali na taka har gaban Mirrow dinmu na tsaya ina karewa kaina kallo.
Bana cikin jerin masu kiba kuma niba sirirya bace Allah yamin halitta Mai daukan hankali sosai, ina