Showing 18001 words to 21000 words out of 94393 words
Chapter 7 - TASWIRAR KADDARA BOOK COMPLETE PDF .txt
ya faru cilla ina wannan mutumin mai kama da Mimi Wanda ya kusa kade min kafa na masa rashin kunya"
Gyada kai cilla yai yace "ai baxan manta Saba uwar dakina kodan yadda yake kama da shashalelen ki"
Sai da nayi murmushi kafin na girgiza kai nace "shine lecturer dinmu na physics wallahi ni nasan da kyar in baxai ban carry over ba ya rama abinda nai masa"
Zaro ido cilla yai yace "kice min wannan maganar ba haka bane uwar dakina"
Dan cizar lip dina na kasa nai nace "Hmm cilla ina ruwa gashi daga gani bashi da kirki har ya bada assignment fah kuma wai ayi submitting gobe in ya wuce 8 baxai karba ba ai assignment din na tsaya nai shiyasa ban fito da wuri ba".
Tagumi cilla yai yana ajiye meat pie dinsa a gefe yace "da damuwa uwar dakina Allah yasa dai bai gane kiba"
Girgiza kai nai nace "ya gane ni don Saida muka hada ido da shi sannan ya janye idon sa ni bansan ya zanba har wani zazzabi ma nake ji"
Nan mukai zugun zugun nida Cilla har lokacin sallah yai duk sona da abinci kasa cin komai nai, sallah naje nai na koma hall din da xamuyi next lecturen mu, ana tashi mun fito nida cilla muna tafiya kamar ance na daga idona suka sauka akan sa Yana tsaye tare da wani suna magana shima dago idonsa yai ya zuba a fuska ta kuma yaki dauke wa ganin haka yasa ni balla masa harara na murguda masa baki, sai kuma na zare idona ina dafe bakin, ganin ya ware min manyan idon sa irin ni dinnan, da sauri na juya na kalli cilla Naga hankalin sa Yana gurin nema mana abin hawa, sai nai Shiru kawai gabana yana faduwa
Shi kuwa Azlan da mamaki yabi bayanta da kallo, gyada kai yai yace "uhm lallai"
Ranar haka na wuni a gida suku suku, Umma ta tambaye ni har ta gaji daga karshe sai ce Mata nai malamin physics din da nace mata bai shigo bane ya shigo kuma har ya bamu assignment yace muyi submitting gobe ai ko Karen hauka ne ya cije ni baxan ce Mata wanda ya kusa bige ni bane sabon lecturer dinmu karshe sai dai tace Allah ya kara maganin mai tsiwa.
Washe gari da wuri na fita sai dai na kasa samun abin hawa da wuri sai wajen 7:45 na samu adaidaita kamar zanyi fitsari a wando haka nake ji, ban shiga school ba sai 8:15 cikin sanyin jiki na nufi hall din da za muke da lecture tuni lecturer ya shiga amma ganin baya hana wadanda suka zo a makare yasa na shiga cikin sanyin jiki, yau a baya na zauna don ba waje a gaba.
Sai 9 ya fita yana fita na mike na nufi gurin class rep din mu, cikin damuwa nace "Hamza har anyi submitting assignment din jiya koh"
Daga mun kai yai yace "nima nayi mamaki dana ga baki zo da wuri ba ya akai haka"
Kamar zanyi kuka nace "wallahi abin hawa na rasa shiyasa, ynxu don Allah ba yadda za'a yi Ka kaimin nawa tun jiya na gama wallahi"
Zare ido yai yace "wa ai saidai kije ki Kai masa ko zai karba don nikam ba ruwana, da na kai masa saida yace na Kara fada in 8 ya wuce duk Wanda yakai masa baxai karba ba"
Shiru nai cikin damuwa nidai banason nayi missing wannan assignment din don yace zai iya Zama first test dinmu, ajiyar zuciya na sauke nace "toh don Allah ina ne office din nasa"
Kwatance yai min na fita don bamu da lecture sai 11, sai da na fara biyawa na taho da cilla Wanda bai shigo ba sai 9 tunda 11 yake da lecture, tare muka nufi office din nasa gaba na Yana faduwa.
A kofar office din muka tsaya na daga kai na kalli inda aka rubuta sunansa *AZLAN MUHAMMAD ABDULLAH* knocking nai sau daya Jin shiru yasa na Kara wani, ciki ciki naji ance come in.
A hankali na tura kofar muka shigo nida Cilla, sai da na sauke ajiyar zuciya jin office din yana wani sassanyan kamshi ga sanyin AC dake tashi, dago kaina da zan suka fada cikin nasa yana zaune akan doguwar kujera ya mike kafafun sa yana sanye da kananun kaya kafarsa ba takalmi sai sheki take.
Zuba min ido yai shima tun daga Sama ya kalle ta tana sanye da hijab brown colour dogo har kasa, sai jakarta data rataya shidai kullum da hijab yake ganin ta, maida dubansa kan cilla yai dake bayanta kansa a kasa yana mamakin meye alakar ta da wannan namijin da kullum zaka gansu tare suna tafiya kuma da dukkan alamu ba gida daya suke ba.
Maida duban sa kanta yai hakan yasa ni bude baki a hankali nace GOOD MORNING SIR.............
Comments Nd share plz
Mrs A.M🥰
[15/08, 15:42] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 11
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Maida dubansa kanta yai haka yasa ni bude baki a hankali nace "Good Morning Sir"
Tabe karamin bakin sa yai ya zuba mata ido yana mamakin rashin kunyar yarinyar Ashe ma level 1 take lallai bata gama balaga ba.
Dan dago idona nai caraf idonmu suka hadu, yamutsa fuska yai cikin husky voice dinsa yace "me ya kawo ki office dina"
Cikin dauriya nace "sir assignment din da Ka bamu jiya ne, tun jiyan na gama sir yau ban samu abin hawa da wuri ba kuma da nazo already lecturer ya shiga sir"
Dage gira daya yai yace "so"
Hadiye wani yawu nai nace "shine shine nazoo nayi submitting sir"
Kallon Cilla yai cikin hade rai yace "kai mai kazo yi kuma"
Da sauri cilla ya dan zaro ido sannan yace sir "rakota nai"
Sai da ya dan saci kallon ta sannan ya maida dubansa kan cilla yace "fyn zaka iya fita tunda ba abinda ya kawo Ka"
Da sauri na kalli cilla daya juya zai fita cikin saurin magana nace "Sir Abba ya hana fa yace kar na dinga zuwa office dn lecturer ni kadai"
Kankance ido Azlan yai yana bin ta da wani mugun kallo cikin zuciyar sa yace lallai yarinyar nan bata da man kai ni Azlan take fadawa haka, bata san yadda nake tattalin budurwarcina ba ai ni ya kamata naji tsoron kebewa da ita ko dan yadda ake kawowa budurcina Hari ta kowanne bangare.
Tabe baki yai cikin husky voice yace "ki koma class ki bawa class rep dinku, duk Wanda bai submitting ba yayi kafin 1 yazo ya min submitting and ki fada masa this should be the last da zan bada assignment Ince Amin submitting aki yi akan tym", daga haka ya maida kansa jikin kujerar ya lumshe idonsa.
Sai da na maka masa harara sannan nace "thank you sir"
Muna fitowa daga office din nida Cilla a tare muka saki ajiyar zuciya sai kuma muka sa dariya, muna tafiya muna gulmar sa har muka isa hall din.
Assignment din na bawa class rep din sannan nai masa bayanin abinda ya fada min muka juya nida Cilla don yunwa nake ji ko breakfast ban yiba.
Cikin lokaci kankani karatu ya fara daukar zafi sam bana wasa don sosai abubuwa sun dau zafi har Dan ramewa nai, har lokacin banyi wata kawa ba don bana son shiririta, duk inda zani tare muke zuwa nida cilla kuma shine yake rakani.
Yau ma kamar ko yaushe na nutsu fiye da yadda bake nake nutsuwa sbd physics din da muke da shi ynxu Wanda Mr Wicked yake mana kamar yadda nasa masa suna, ina cikin duba joter dina sbd yace yau zai mana test shiyasa duk a rikice nake don malamin mugu ne baya mana Wasa ko kadan, sallama naji a kaina hakan yasa na dan dago don ganin wace, murmushi nai ganin Asma'u Hamza course mate dita ce kuma mun dan fi shiri a cikin class din don itama da dukkan alamu karatu ne ya kawota ba shirme ba.
Zama tai a gefena tace sannu "Batul sarkin karatu"
Dan dariya nai nace "sannu Malama Asma'u kinga laifina ynxu karatun ya dau zafi sai kana yi kullum kana dubawa in ba haka ba kazo karatun exam kanka yai bombing"
Dariya tai tace "kuma hake ne, ke ba ruwan ki baki shiga cikin mutane"
Dan murmushi nai nace "toh in shiga in batawa kaina lokaci, tym din da bamu da lecture nafi gane wa in zanci abinci naci, in kuma bana Jin yunwa na duba papers dina in na koma gida ba lallai na duba ba sbd gajiya"
Murmushi tai tace "haka ne shiyasa Nima nace bara dai na dawo gurinki na dinga Zama naga serious student ce keh in ba damuwa"
Dan murmushi nai nace "laa ba komai Allah mu dinga zaman tare nima wani tym dn zama haka yana damuna"
Zatai magana knn Mr Wicked ya shigo hakan yasa ta yin Shiru, Nima bakina naja nai Shiru duk muka nutsu muka zuba masa ido......
************
Cikin shesshekar kuka tace "ynxu Mummy me na rasa da Ya Azlan zai bude baki yace baya sona, ina da kyau na Mummy kuma yadda Maza suke bibiyata shi Mai yasa baya min haka"
Kwafa Mummy tai tace "goge hawayen ki Zainab in ina raye sai kin auri Azlan, shegen yaro ya kalli tsabar idona yace baya son ki ni bansan dalilin Baffa na goya masa baya ba wallahi"
Hawayen zainab ta goge cikin shagwaba tace 'Mummy ai kema kinsan Baffa yafi sonsa akan kowa nidai ki taimake ni Mummy ki shawo kan Baffan ya amince In ban aure Saba mutuwa zan yi Allah"
Da sauri Mummy ta rufe Mata baki tace kiyi min shiru kedai kawai ki hada kayan ki kamar yadda na tsara Miki, kije gidan Ya Muhammad din ai gidan babanki ne, kuma in kinje bangaren Hajia Maryam zaki sauka, ina Kara fada Miki kiyi duk abinda zakiyi don jawo hankalin sa gare ki sannan ki daina sa bra guda 1 ki dinga sa biyu kuma masu push sosai badai kwaila yake ce Miki ba in kika koma sa biyu ai sai ya dawo miki kallon mai abubuwan arziki, sannan kije kasuwa ki siyo abin cikin duwawu haka ni dai Wallahi bani kuka gado ba da ace ni kika gada AI karyar Azlan ya kiraki da kwaila.
Dafe kumatu Zainab tai tace "Mummy ai yasan bani da boobs din in nayi ciko baxai gane ba kuwa"
Tsaki Mummy tai tace "ke dallah rabu da shi bai wani san yadda kike ba kawai yafada ne shi Azlan din har wani ganin ki yake da zai San yadda kike, kedai kiyi abinda nace sannan in kinga Yana guri kidinga dan karairaya kina turo kirji"
Dariya suka saki suka tafa kamar kawaye Saida Mummy ta gama fada mata duk yadda zatai sannan ta mike ta bar dakin tana jaddada Mata tai hanzarin shiryawa don yau take son ta tafi gidan Abie.
Bin bayan Mummy da kallo tai sannan ta mike ta nufi gaban Mirror tana karewa kanta kallo, tana da kyau sosai don fara ce tass kuma kasancewar ta yar gayu Mai gyara fatar ta da lura da ita yasa skin din nata Kara wani haske, sai dai kawa katon bakin dayai ma fuskar ta cikas, don tubarkalla tana da babban baki amma ba'a cika ganewa ba sbd yadda take kullum cikin makeup hakan yake taimakawa gurin boye girman bakin nata.
Kallon kirjin ta tai da yake kamar lemon tsami don bata da kirji sosai kamar wacce ta fara kirgan dangi sai duwawun ta da yake shafe, a takaice dai bata da body structure a tsaye take number 1, ajiyar zuciya tai tana tunanin yadda zata dinga ciko tana masa karairaya, wani tsallen dadi tai tana jin kamar ta aure ta gama ne donfa ita tayi alkawarin auren Azlan ko ana ha Maza ha Mata........
*********
Cikin aji ta waina manyan idonta ta kalli kawayen ta tace "Nana kinsan Allah gayen ya mugun tafiya dani, tun ranar dana fara ganin sa na kamu da mugun sonsa" sai ta sauke ajiyar zuciya tana dafe saitin zuciyar ta tace "kinsan ya hadu ne koh"
Murmushi Nana tai tace "Ai ni Zuby mamaki kike bani ashe zaki fada soyayya ta gaskia"
Hararar nana tai tace"gashi kuwa ni har na fadawa Dad na samu mijin aure"
Zaro ido Hafsa tai da tunda suka fara maganar bata ce komai ba tace "Zuby are u serious? Mutumin nan fa ko sanin zaman ki baiba amma har kin fadawa dad kin samu miji"
Dan bata fuska tai tace kina tunanin baxai soni ba kome, mikewa tsaye tai tana dan gyara budaddaiyar abayar jikinta Wanda ya fallasa Riga da wandon dake jikin ta da suka kamata sai mayafi data yafa a kanta, juya jikin ta tai tace "meye baiji ba anan"
Bin ta da kallo sukai tana da diri dai dai gwargwado kuma tana da boobs madaidaita sannan tana da kyaun fuska don fara ce duk da dai farin hadda na bleaching, gyada kai Hafsa tai tace "komai yaji kawata"
Wani Murmushi tai tace "toh kunga ai kawai nasan zaima fada tarkon Sona don wallahi sai na aure sa haba wannan daga gani ba karamin haukata mace zaiyi a bed ba" ta wani lumshe ido tana lasar Baki
Wani ihu suka saki har saida mutanen dake gefen su suka juyo suka kalle su, dariya Nana tai tace "Zuby me ya kamata mu farayi ynxu toh da zai sa yasan da zaman ki"
Hafsa ce tai caraf tace "abu Mai sauki ai gurin sa zaki je kina karairaya kice kinzo ya koya miki abin da yai mana dazu baki gane ba AI kin gane
koh"
Tafawa sukai suna shewa inda ta mike tana kara fesa turare a jikin ta ta nufi Office din Mr Azlan Muhammad Abdullah.
*Wacece Zuby*
Ya daya tilo ce a gurin Alh Ahmad Muktar da kuma Hajia Badiyya, ita kadai Allah ya basu haka yasa suke nuna mata soyayya mai tsanani dukkan abinda take so Shi take yi hakan yasa ta taso sangartacciya ta riga ta saba duk abinda take so Shi zatayi ba Wanda zai kwabe ta, tana da girman kai sosai ynxu haka tana level 3 a BUK inda take karantar Architecture.
Tun suna level 1 suke tare da Nana da kuma Hafsat haka yasa suka zama aminai sosai, ba laifi tana da kokari kodan kasancewar ta mara son raini a gurin course mate dinta hakan ke sata dagewa tayi karatu don kar ta samu carry over...
Tana da tarin samari sosai wadanda kawai cin kudin su take sai kuma irin wadanda ake soyayyar shan minti ayi romance amma ba'a zarcewa.
******
Yana zaune yana shan drink aka yi knocking kofar sai da yai kamar baxai amsa ba sai kuma yace "yess come in"
A hankali ta turo kofar ta shigo tana yin sallama, a kasan baki ya amsa mata kallo daya yai mata ya kauda kansa sbd yadda jikinta yake bayyana.
Karasowa tai ta tsaya daga dan nesa da shi cikin kissa tace "Good Afternoon sir"
Gyada kai kawai yai yana cigaba da duban system dinsa, cikin kwarewa da iya seducing namiji ta dan janye mayafin ta saman kirjin ta da ya taso yadan bayyana, sai da ta daidaita kanta sannan ta matso kusa da table dinsa ta sunkuyo yadda kirjin ta zai bayyana tace "Sir dama abinda Ka mana dazu ne ban gane ba shine nazo ka min bayani plz in ba damuwa"
Dagowa yai zai Mata magana caraf idonsa suka fada kan kirjin ta da suka dan bayyana ta sama...........
****
Da Mamaki na kalli Asma'u nace "da gaske wai Matar aure ce keh"
Dariya tai tace "wallahi Amma auren wata 2 knn"
Ajiyar zuciya nai nace "tab amma baku more amarcin ku ba"
Dan bude ido tai sai kuma tai dariya tace "Ashe kina magana haka nifa da kallon da nake miki san baki magana"
Murmushi nai nace "ina yi mana saidai bada kowa nake na gaskia"
Murmushin tai itama tace "kinga Baby yana kira nasan yazo dauka ta ko zaki zo muje ku gaisa daga nan sai mu rage Miki hanya"
Hararar ta nai nace "wallahi ki shiga hankalin ki kawai baki san halina ba kina cewa nazo muje mu gaisa da mijin ki tab, lallai da sauran ki ai kuwa in haka kike ki chanja don ynxu yaudara tayi yawa a duniya"
Murmushi tai tace "duk da bansan halin kiba Batul amma na yadda dake ai shiyasa nace Miki kizo ku gaisa din amma Nima ina kiyaye wa fah"
Gyada kai nai nace "better dai"
Dariya tai tace "tab kice haka kike da kishi wannan za'a sha kallo"
Nidai ban mata magana ba sai hannu dana daga mata kawai, murmushi nai don naji dadin yau din sosai ko dan sbd hirar da mukai da Asma'u ne, Nima fta nai na samu abin hawa don Cilla bai zo na yau...
Toh fans ga Zainab nan fah ta danno da karfin ta zata gidan Abie farauto zuciyar Azlan🤞 koya zata kasance zatayi nasara ko kuwa🤔
Ga kuma zuby fa itama tace bata yadda ba sai ta aure sa Don ita ta gama fadawa Dad dinta ma ta samu miji aure kawai za'a daura🏌️♀️🏌️♀️🏌️♀️
Ku kawo dauki za'a yiwa Oga Azlan fyaddd*****
Comments Nd share plz
Mrs A.M🥰
[16/08, 20:08] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 12
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Dagowa yai ya kalli fuskar ta yaga ta wani zuba masa ido tana masa wani kallo, hade rai yai ya mike tsaye ya dafa table din yace "karatu kika zo ko kuma tallan jikin ki kika zo min"
Da sauri ta dago ta kalle sa ganin yadda ya hade fuska yasa ta cikin inda inda tace "uhm uhmm sirr"
Tsaki yai ya nuna mata kofa yace "get out"
Zata sake magana ya daka Mata tsawar da bata son lokacin data kwasa a guje ba tafita.
Zama yai yana sauke ajiyar zuciya yana tunanin mafitar da zai dauka don gaskia baxai iya daukar wannan Risk dinba....
*********
Ina shiga gida da sallama na shiga palourn mu ganin Umma bata nan yasa na kalli Aisha dake assignment nace "Aisha ina Umma"
Dagowa tai d a fara'a tace "Maman hidaya ce ta haihu Ya batul shine Umma ta shiga itada Mimi, Nima da zan bisu sai Umma tace na zauna in kin dawo ma shiga tare"
Cikin murna nace "Kai don Allah Maman Hidaya ta haihu mai aka samu"
Murmushi tai tace "Namiji aka samu, kar kiso kiga Mimi da aka fada mata kamar zata yi hauka da kyar ta Jira Umma don da tace ita