Showing 39001 words to 42000 words out of 94393 words

Chapter 14 - TASWIRAR KADDARA BOOK COMPLETE PDF .txt

Mrs A.M   

03 Aug 2024

16912

Ka da shi ba"


Dagowa yai ya kalli Junaid sai ya kalli Abie baisan mai zai ce ba hakan yasa shi fadin "barayi ne suka sace", jiri na soma gani da sauri nayi baya ina fadin Innanillahi wa innanillaihir raji'un a hankali idona ya soma rufewa kawai sai gani sukai na zube a gun.


Aisha da Mimi kusan a tare suka taho gurina da gudu suna kuka, girgiza ni Mimi take tana fadin "Maaa kiyi hakuri baxan sake ba ki tashi"


Mami da Aunty sarah ne suka zo suka dago ni akan kujera suka kwantar dani, kallon Junaid Mami tai tace "zo ka duba min yarinyar nan Junaid mai ya same ta"


Da sauri Azlan ya janyo Junaid baya ganin yana nufar inda take, kallon Mami yai yace "Maa a Kira likita mace tazo ta duba ta mana ba dole sai Shi ba"


Tsaki Mami tai tace "Azlan bana son shirme don Allah ceto rayuwar yarinyar nan za'a yi har sai an wani tsaya jiran likita mace bayan ga doctor muna tare dashi"


Girgiza kai yai yace "Mami baxa ki fahimta ba kawai ya fada min abinda za'a yi a ceto ta ki sai na mata amma gaskia shi baxai taba ta ba maman Yarinya tace fah"


Kallon sa Baffa yai yace "zaki bana son gardama, kai Junaid jeka duba ta"


Kallon Baffa yake idonsa na sheki sbd tsabar bacin rai, sai hadiyar zuciya yake ji yake kamar ana Kwara masa ruwan zafi a kirji.


Kallon Junaid yai yace "Junaidu, Junaidu, Junaidu kaga so uku na kira Ka koh wallahi ko hannun ta Ka rike sai na karya ma shi don iskanci taya zaka taba mamar yarinya ta........."










Comments Nd share plz














Mrs A.M🥰
[30/08, 18:52] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️


*TASWIRAR KADDARA*


♠️♠️♠️♠️♠️




Written by
Mrs A.M🥰


Page 22


Dedicated to TASWIRAR KADDARA Fans group ina Jin dadin comments dinku Allah ya bar mu tare🤝🥰


*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃




*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*




*LOCATION KANO*


08062073990


BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM




Tsayawa Junaid yai cak ya juyo ya kalli Azlan yana mamakin abinda yake nufi da in ya taba ta sai ya karya sa, ya bude baki zai magana Baffa ya daga masa hannu dole yai shiru kawai yana kallon Azlan.


Ruwa Baffa ya umarci Mami data shafa mata a fuska, da sauri Aunty Sarah ta mika ma Mami ruwan shafa mata mami tai amma bata motsa ba cike da tsoro mami ta Kara shafa mata ruwan.


Wani ajiyar zuciya na sauke mai karfi ina jan numfashi na, a hankali na soma bude ido na hawaye ne Mai zafi ya sauko min, in har abinda na gani kuma naji ne gaskia knn Mr Wicked ne baban Mimi.


Lumshe idona nai ina fadin Innanillahi wa innanillaihir raji'un, Mami data zuba mata ido tana kallon ta a hankali ta dora hannun ta akaina tana shafawa, hakan dana ji kawai na fashe da kuka.


Zaro ido Azlan yai yana kallon ta, ta tabbata knn tana da aljanu yarinyar nn kallon baffa yai yace "tsoho ko Malam Sule za'a kirawo ne da alama kanta na motsi."


Harara Baffa ya jefa masa yace "Ka shiga hankalin kafa zaki"


Tabe baki yai yana daga kafadar sa yace "gani nai tana abun masu motsi a ka shine kawai na bada shawarar"


Girgiza kai Baffa yai kallon Aisha yai yace "ina ne gidan ku"


A hankali tace "Hausawa ne Baffa"


Gyada kai yai yace "bara na sa a maida ku gida kinji"


Abie da yake ta juya bracelet din yace "Aisha a ina kuka samu wannan abin hannun."


A tsorace ta dago ta kalle sa sai kuma ta juya ta kalli Batul da ke kwance har lokacin hawaye kawai take, ganin alamun tsoro a tare da ita yasa Baffa cewa "ki kwantar da hankalin ki kinji Aisha ba abinda zamu muku tambayar kawai zaki amsa"


Cikin rawar baki tace "na baban Mimi ne'


Da mamaki sosai Mami tace "baban Mimi kuma? Nidai a iya sanina wannan abin guda biyu ne iri daya na Junaid dana Azlan gashi kuma wannan ma iri daya ne sak alamun na Azlan ne kenn.."


Baffa ne yace "kar ku ruda ta zo kinji jikata'


Sai da ta kalle ni taga idona a rufe yake sannan ta juya ta kalli Mimi dake bacci jikin Azlan sannan ta nufi gurin Baffa tana juyo wa tana kallo na, dafa kanta Baffa yai yace kamar ya na babban Mimi ba kunce ya rasu ba


Girgiza kai tai tana hawaye tace "bamu San ko waye baban taba abinda muke dashi Wanda zai nuna mana baban ta wannan bracelet din ne kawai"


A ynxu kuwa kan kowa dake palourn ya rude, cikin bugawar zuciya Azlan yace "kee me kike nufi da baku san waye baban beauty ba"


Daga kai tai tana hawaye tace "bamu san waye baban taba wannan bracelet din ne kawai mallakin baban ta da yake hannun Ya Batul"


Mikewa Baffa yai ya kalli Abie yace "Muhammad zama bai ganmu ba a wannan gabar, gidan su yaran zamu je mu gana da iyayen su, don kaina ya rude kuma."


Shima Abie da ya gama rudewa Jin wannan maganar yace "Baffa muje toh," kallon Aisha yai yace "xamu samu baban ku a gida ynxu"


Daga masa kai tai tana share hawaye, Mika mata waya Baffa yai yace "samun number dinsa na kira sa tukun kar muje masa haka kawai"


Cikin rawar jiki ta karbi wayar tasa ma baffa numbern Abba, dialing numbern Abba yai ringing biyu ya dauka


Sallama Baffa yai cikin muryar sa mai cike da dattako


Daga can bangaren Abba ya amsa yana gaishe sa Jin muryar ta babban mutum.


Cikin dattako Baffa yace "muna tare da su Aisha ne da Batul in ba damuwa muna son zuwa mu hadu in zamu same Ka a gida"


Cikin dan fargaba Abba yace "suna lafia? Ko wani abun sukai"


Murmushi Baffa yai yace "ba abinda sukai magana ce dama muke so muyi akan Mimi"


Da mamaki Abba yace "Mimi kuma?"


Daga kai Baffa yai yace "eh ita shiyasa nace in ba damuwa zamu iya samun ka ynxu"


Abba da yake zaune a gefen Umma yace "insha Allah ina gida dama zan fita ne amma zan tsaya na Jira ku"


Murmushi Baffa yai yace "mun gode sosai sai mun iso"




********
Umma da tunda Abba ya fara waya take kallon sa da son Jin karin bayani duk da kuwa wayar a speaker take, kallon ta Abba yai bayan ya ajiye wayar yace "Umman Aisha bari naje na Kira yan uwana su zo kafin su iso duk da ban san me suke so suyi magana akai ba amma ina ji magana ce mai muhimmanci"


Daga kai Umma tai tace "Allah yasa muji alkhairi dai kawai amma ni duk gabana sai faduwa yake Abba"


Murmushi Abba yai yana Jan kumatun ta cike da kauna yace "yaushe Sadiyayye ta ta fara jin tsoro nidai nasan Sadiyayye ta jaruma ce"


Murmushi Umma tai tana juya idon ta tace "har ynxu baka tsufa jika ce fa dakai"


Murmushi yai ya dan dale mata baki yace "kul kika Kara cewa bana tsufa har ynxu jina nake garau, ko so kike na auro yar yarinya ce na tabbatar Miki da garau nake"


Harara Umma ta sakar masa tana turo baki, dariya Abba yai yace "Sadiyayye ta uwargida kuma amarya har abada Insha Allah, Allah yai miki albarka Matata"


Murmushi Umma tai tace "Ameen Mijinaa."


Sai da ya tabbatar hankalin ta ya kwanta sannan ya fita don zuwa tahowa da su kawu Nasiru




*********
Baffa ne yace Muhammad sai mu tafi ko da Mustapha da Junaid sai Azlan ku matan ku zauna.


Mummy da take so ayi komai a gabanta tace Baffa don Allah muma muje tare mana ayi komai muna gun


Hade rai yai yace banyi ra'a yi ba ku zauna mazan ne kawai zasu je, mikewa yai ya kalle ni da har ynxu nake kwance sai dai na dena hawayen amma idona a rufe yake.


A hankali cikin nutsuwa baffa yace "taso kinji jikata"


Ban masa musu ba na mike a hankali don dama na gaji na rasa yadda zanyi ne kawai bana.


Ko bangaren da Mimi take ban kalla ba na fita daga palourn motar Junaid muka shiga nida Aisha sai uncle Mustapha a gaba, Azlan kuma ya dauki Baffa da Abie sai Mimi dake kwance a jikin Baffa a back sit.


Tafiyar minti 30 ce ta kawo mu kofar gidan mu, muna zuwa na bude kofar na fita na shige gidan a soron gidan na hadu dasu Kawu Nasiru a gaggauce na gaishe su na shige cikin gidan, ban hadu da Umma ba haka yasa na shige dakin mu kawai na kwanta akan katifa ina rufe idona.....


Aisha ce data shigo ganin su Kawu Nasiru yasa ta fada musu bakin suna jiran su a waje, fitowa sukai sai dai Suma tozali da sukai da su Junaid ba karamin daga musu hankali yai ba bama ganin mimi kwance a jikin Azlan.


Khalil da yazo wuce wa Abba yasa shi shiga da Mimi cikin gidan gabansa yana faduwa da alama magana ce mai muhimmanci za'a yi yau dinnan.


Babban gida suka nufa gaba daya don gidan Abba ba gurin da za'a sauke su, a Palourn baki suka zauna bayan an gaisa Baffa yai gyaran murya yace "abinda yasa muka zo nan sbd wani Abu daya shige mana dubu gaba dayan mu, na farko kamannin da Mimi take kama da jikokina kamar an tsaga Kara na biyu kuma abin hannun jikana da ya bata kusan shekara biyar knn sai gashi yau a jakar Batul, sannan kuma Aisha tace abin hannun na baban Mimi ne toh abin ya daure mana kai sosai shiyasa nake son sanin shin waye *baban Mimi?*"


Sunkuyar da kai Abba yai hawaye na taruwa a idonsa, Kawu Nasiru ne ya gyara zama yace "gaskia ba'a san waye baban ta ba don fyade akai ma Yarinyar mu ta haife ta"


Salati Baffa yai yace "subhanallah amma naga karamar yarinya ce Batul din har yaushe ta haifi Mimi"


Azlan kuwa sunkuyar da kansa kawai yai gaban sa yana faduwa jin ta hanyar da aka samu Yarinyar sa lallai da zaiyi ido hudu da ko waye sai yaci ubansaa


Murmushi wanda yafi kuka ciwo yace *"BA BATUL BACE MAHAIFIYAR MIMI"*














Comments Nd share plz












Mrs A.M🥰


[31/08, 11:28] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️


*TASWIRAR KADDARA*


♠️♠️♠️♠️♠️




Written by
Mrs A.M🥰


Page 23


*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃




*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*




*LOCATION KANO*


08062073990


BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM




Murmushi wanda yafi kuka ciwo Abba yai yace "ba batul bace mahaifiyar mimi".


Cike da Mamaki su Baffa suke kallon sa, kasa jure wa Abie yai yace "ba ita bace mahaifiyar ta?"


Daga kai Abba yai yace "bara a takaice na baku labarin rayuwar ta"




*WAIWAYE*


Kamar yadda kuka sani haihuwa 3 ne Umma tai amma haihuwar ta farko ta haifi Yan biyu mata masu kama da juna inda aka sa musu suna Khadija da Fatima Batul sai ta biyu ta samu Aisha ta uku kuma ta kara twins maza Kamal da Khalil.


Sun taso kansu a hade duk da Khadija ta kasance mai sanyin hali da mutukar hakuri yayinda Batul kuma ta kasance Mai zafi da rashin daukar raini, kamar su daya sak don ta halayen su ne kawai ake banbanta su da kuma saurin maganar Batul.


Ajin su daya a makaranta komai tare suke basa boyewa juna komai, wannan hadin kan nasu ba karamin faranta ran iyayen su yake ba.


A lokacin da suke da shekaru sha uku wani mummunan abu ya faru da wannan ahalin wanda ya kasance sanadiyar tarwatsa musu farin cikin su.


Cikin sauri Umma ta fito daga kitchen ta daga kai ta kalli yadda garin ya hada hadari sosai gashi bata da magin da zata sa a girki ga kuma Magriba ta doso kai, kallon Khadija tai dake xaune tana bitar karatun Qur'ani.


Daki ta shiga ta dauko kudi ta mikawa Khadija tace "ungo Mamana yi sauri kije shagon Muntari ki siyo min magi na 50 da onga na 30 kinga magriba ta doso kuma gashi hadari ne a garin bana son aiken su kamal ne don wasa zasu tsaya yi."


Cikin nutsuwa ta mike tace "toh Umma" karbar kudin tai ta fita daga gidan tana tafiya cike da nutsuwa.....


Kusan minti 30 da fitar ta amma bata dawo ba, Batul da hankalin ta yaki kwanciya tun fitar Khadija ta kalli Umma da itama hankalin nata ba'a kwancen yake ba don har an Kira sallah tace "Umma bara naje na dubo ina ta tsaya, kinga har ynxu bata dawo ba kuma shagon Muntarin ba nisa ne da shiba"


Cikin fargaba Umma tace kiyi sauri don Allah kema kar ki tsaya kinji


Daga kai kawai tai ta sa hijab dinta ta fice daga gidan, shagon Muntarin ta fara zuwa amma yace mata bai ga Khadija ba, hankalin ta a tashe ta soma zagaye unguwar ko taje wani shagon bana muntarin ba amma duk inda taje sai ace mata bata zo ba.


Daidai wani uncompleted building dake kasan layin su tazo wucewa taji kamar muryar Khadija cikin kuka tana fadin "don Allah kayi hakuri ka kyale ni mutuwa zanyi"


Wani irin bugawa kirjin ta yai cikin sanyin jiki da kasala data rufar Mata jikin ta na wani irin rawa ta zagaya cikin ginin da sauri ta runtse idonta ganin wani mutum dake sanye da bakaken kaya ya danne Khadija dake kwance tsirara duk ya yaga kayan jikinta ga ruwan sama dake dukanta..


Wani karfi ne yazo mata tasa ihu Wanda ya fargar da Mutumin da sauri ya daga Khadija ya juya da nufin guduwa batul ta maza ta cafki hannunsa dambe suka fara Yana son ya kwace kansa ita kuma tana kaimasa duka da karfi tana kokarin bude fuskar sa don ya rufe fuskar da hular rigar sa, karfin mace dana miji ba daya hankada ta yai da karfi Wanda ita kuma dake rike da hannun sa ta fincike abin hannun da taji.


Guduwa yai bata tsaya bin sa ba ta kwasa a guje gurin Khadija dake kwance cikin jini tana kuka, tana zuwa ta rungumo ta a jikinta tana fashewa da kuka, wani irin kuka Khadija itama ta kara fashewa dashi mai cike da tausayi da rauni.


Cikin rawar murya tace "Batul ya cuce ni ya raba ni da martaba ta"


Runtse ido Batul tai ta cire hijab dinta ta lullubawa Khadija, cikin karfin hali tace "Zaki iya tashi mu tafi gida"


Girgiza Mata kai kawai Khadija take idonta a rufe mike wa tai tace "ki tsaya kinji bara naje na Kira Umma"


Daga mata kai Khadija tai tana rufe idonta.


Cikin sanyin jiki Batul ta nufi gida a kofar gida ta tarar da Umma da Abba suna tsaye da alama Abban ya dawo ne.


Kallon ta kawai suke ganin tana tafiya tana kuka ga ba hijab a jikinta, da sauri Umma ta riko ta tace "lafia kin ganta Batul"


Fadawa jikin Umma tai tana fashewa da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro


Cikin tsinkewar zuciya Umma tace "ki min magana mana bana son iskanci"


Nuna musu hanya kawai take tana kuka, Abba ne yai dauriyar riko batul yace "Batul muje ki nuna min inda take"


Ina gaba suna bina a baya har muka isa kangon, a lokacin da muka isa Khadija bata numfashi tayi fayau kamar ba rai a tare da ita.


Umma da kafafun ta ke rawa ta isa kusa da Batul ta kasa kuka ma cikin rawar jiki ta warware hijab din da batul ta yafa mata ta sama ta a jikinta, janyo ta tai gabanta na faduwa.


Abba daya fahimci halin da aka jefa yarsa ya juya da sauri yace "bara na samo mana abin hawa mu kaita asibiti,"


Umma bata iya magana ba idonta kuri akan Khadija da bata numfashi, bai dade ba ya dawo da adaidaita shida Umma ne suka shiga ni kuma Abba yace na koma gida.


Lokacin da na shiga gida da kyar na iya zama akan kujera Jin wani abu a hannuna yasa na bude shi, wani kyakkyawan bracelet na gani sai kwalli yake wani irin jifa nai da shi cike da tsanar ko waye mai shi don nasan shine silar lalacewar rayuwar yar uwata.


Kamal dake kallona yaje ya dauko ya kalle ni yace "Ya Batul me yasa kika yar da shi na waye ne wannan abin kingan sa mai kyau".


Ban basa amsa ba sai hawayena da nake sharewa kawai


Aisha ce ta kalle ni don itama tana da dan wayo shekarar ta 11 lokacin tace "Ya Batul ina Ya Khadija dasu Abba"


Cikin dauriya nace "sun tafi Kai Khadija asibiti bata da lafiya"


Fuskar tausayi dukansu sukai suka ce Allah ya bata lafia








**********


Lokacin da su Abba suka kai Khadija asibiti kin karbar ta akai wai sai an zo da dan sanda, dole Abba ya kira kawu Nasiru ya fada masa halin da ake ciki.


Cikin dimuwa Kawu Nasiru ya kira wani dan sanda dake unguwar su tare da shi suka zo asibitin sannan aka shiga da Khadija, numfashin ta aka soma samu ya dawo daidai sannan aka duba ta abin tausayi har dinki aka mata don Wanda ya mata fyaden karfi yasa Mata.


Sai da tayi sati daya a asibiti sannan aka sallame ta kuma tunda ta farka batai magana ba, batai kuka ba ko an mata magana sai dai kawai ta daga kanta ko ta girgiza kanta, Batul kuwa bata taba zuwa ba kullum tana gida ita ke kula da abincin su.


Tuni labarin abinda ya faru da Khadija ya karade Yan uwa da mutan unguwa, don tunda uwani taji da hama suka shiga barbadawa, inda Shamsiyya ma ta fada a makarantar bokon su da islamiyya cewa an kama Khadija tana iskanci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login