Showing 6001 words to 9000 words out of 94393 words
ne dubu Biyu da dari 3 shine yace na kawo miki in ba damuwa wai ki yi gobe da wuri sbd ana siya da safe sosai"
Karbar kudin nai na ciri dari ukun kai na mikawa Aisha naira dari, dari biyun kuma na bawa Kamal nace "gashi Kai da Khalil ku raba"
Godia suka fara min suna murna don dama haka nake musu in har nayi ciniki toh ina basu dari dari wannan ina ragewa Abba kudin kashewar sune tunda in na basu kudin basa tambayar Abba kudin makaranta har sai ya kare.
A gajiye na mike bayan mun gama jera Zobon a fridge nace "gaskia Kamal Ka fadawa Mansur ba lalle nayi cake din gobe ba, kaga gobe kamun Khadija kuma ni ta bawa In Mata cake da donut ga kunun Aya da zobo zanyi jibi na yini gaskia ba lallai wannan satin nayi cake ba kuma fa Monday zamu fara waec"
Marairaice fuska Kamal yai yace "Ya Batul zamu taya ki don Allah ko a cake din goben da zakiyi ki kara kayan hadin kawai sai kiyi duka hadda Wanda za'a Kai shagon"
Aisha ce tace "laaaa kuma haka ne basa banba sumu munzo da shawara mai kyau"
Harara ya sakar mata sannan ya juyo ya kalle ni yace "ko Ya Batul zamu taya ki Allah gobe Friday muna dawowa daga school in baki gama ba sai mu tayaki ko Aisha"
Harara Aisha ta sakar masa tace "wai sa'ar kace ni shekara biyu na baka amma Ka raina ni don wulakanci baxa ka dinga cemin Ya Aisha ba sai wani Aisha kana ganin yadda Khalil yake cemin duk zai kira ni sai yace Ya Aisha Amma Banda kai banza mara kunya"
Zai yi magana na janyo hannunsa na tura sa palour nace "wuce muje toh ka taya ni duba abinda Banda Shi na cake din sai Ka siyo min tunda ga kudi sun shigo"
Shiga palour mukai yana fadin "me yasa baki ce su Khadijan su baki kudi ba kafin ki musu Ya Batul"
Dariya nai nace "kawai na fison sai na gama maka abinka tsaf in kazo dauka Ka ban kudina cas kaga wannan kudin da aka ban zan ware ribata nasa a banki ragowar kuma na kara siyo kayan flour"
A Palour muka zauna muna lissafi har Abba ya shigo gidan anan aka hau hira kowa na bada labarin abinda ya faru daya basa mamaki ko wani Abu da yai Wanda Abba zai gyarawa mutun yai masa in na fada ne yayi, haka muke muna da fahimtar juna sosai mun dauki iyayen mu matsayin aminan mu da ba wani sirrin mu da muke boye musu shiyasa ko lokacin da KADDARA ta fada mana akan samuwar cikin Mimi sosai iyayen mu suka fahimci zancen kuma suka karbi KADDARAR da hannu bibbiyu duk irin bakaken maganganun da suka dinga ji suka toshe kunnen su har Mimi tazo duniya komai Abba ne yake mata sai dana fara Sana'a nema komai na samu akan ta nake karar da shi gurin siya mata sitiru masu kyau daidai talaka mai rufin Asiri.
Sai karfe 10 sannan Abba ya kashe TV yace kowa yaje ya kwanta dama haka dokar sa take tun muna kananu karfe goma kowa yake shiga daki ya kwanta sbd school sai in ranakun daba makaranta ne ma yake barin mu wataran mukai 11, dakin mu muka shiga nida Aisha su Kamal ma suka tafi dakin su dake jikin dakin mu, sai dakin su Umma dake kallon dakunan mu, koda muka shiga daki sai da muka sha hira sosai nida Aisha kafin mu kwanta bacci.
Washe gari da kaina na raka Mimi makaranta bayan tasa nai mata alkawarin zan koma na dauko ta da kaina, ina komawa gida na fara aikin cake dina tunda da wuta Allah ya taimake ni kafin 11 har na gama don da toaster biyu nake yi da toaster daya ce dani da aka fara bani order din cake na biki ko suna sai na tara kudina na siya wata toaster din sbd na rinka sauri, doughnut din na kwaba na ajiye a rana, hijab dina na zumbula har kasa dark blue nai ma Umma sallama na tafi school din su Mimi dake cikin Unguwar mu.
A compound din school din na same su itada Hidaya suna zaune suna wasa da kasa, suna gani na suka taso a guje suka taho suka rungume ni, dariya nai ina shafa kansu ina son Hidaya sbd ita kadai ce kawai Mimi mutane sun jahilci Kaddarar data same mu basa son yayansu suna kawance da Mimi duk da kuwa yadda yarinyar take da farin jini amma banda cikin layin mu don duk Wanda yasan ta yadda aka same ta kyamar ta suke banda gidan su Hidaya.
Riko hannun su nai sai murna suke nazo daukan su, sai da na tsaya na siya musu awara ta goma goma da ice cream sai murna suke suna tsalle, har gida na kai Hidaya kasancewar gidan su a jikin gidan mu yake mamarta ba wata babba bace Aunty Zainab tana da kirki sosai Hidaya ce yar ta kadai sai ynxu da take dauke da wani cikin.
Muna shiga gida wanka nai ma Mimi na sa mata atampar ta ta sallah powder da kwalli na samata sai vaseline dana shafa Mata a lips dinta, dankwalin ta na daura mata, abincin da Umma ta dafa na Rana na zuba mata na koma gurin aikin doughnut din da nake, kafin karfe 2 na gama doughnut din na ajiye a gefe, kafin na mike daga gurin kanwar Khadija da yayar ta suka shigo, gaisawa mukai bayan sun gaishe da Umma, a tare muka kirga cake da doughnut din sai da na tabbatar ya cika iya adadin Wanda suka ban na jera su a cikin kwali, dubo Goma Yayar Khadija ta miko min tace "ga kudin nan Batul mun gode sosai sai gobe insha Allah kinsan yini da wuri ake yi don Allah kafin karfe daya muke son zobon da kunun Aya."
Karbar kudin nai na mikawa Umma sannan nace "Insha Allah zaku samu da wuri sai dai ku kawo kulolin da zan sa zobon a ciki tunda kinga sai na zuba kankara akai yadda zasuyi sanyi koh"
"Insha Allah goben da safe za'a kawo mun gode sosai"
Kati ta mika min guda biyu tace"gashi na kamun ne karfe 4 ne za'a yi don Allah kuzo keda Aisha"
Kallon Umma nai ganin bata kallona ma yasa na karba nace "zan Kira Abba na tambaye sa in ya bari mai zai hanani zuwa"
Har kofar gida na raka su sannan na shigo na gyara gurin Aisha da dawowar ta knn ta tayani muka kintsa inda na bata, cake din da nai na zuba a Bokitin fenti na ajiye a gefe ina jiran khalil ko kamal wani ya shigo na basa ya kaiwa Mansur, Zama nai gurin Umma muna lissafin yadda za'a yi da kudin sai murna muke sbd wannan ne order da aka taba bani mai tsoka ragowar duk basa wuce na 5k koh 7k Amma ynxu gashi 10k zuwait ga gobe ma Insha Allah zan musu zobo da kunun Aya na 5k.
Kasancewar inada banki da nake tara kudi kodan university din da nake son shiga in na gama waec, sbd na ragewa Abba wani abun yasa Umma yanke shawarar a ajiye 10k din duka a bankin nawa,
Kallon Umma nai nace "a'a Umma keda Abba kudai dubu biyar kusa albarka ko Umma"
Girgiza kai tai tace "A'a basai mun dauka ba ke da kike Tara kudin ki"
Damun Umma nai dole sai da ta dau 2k tace "zamu raba wannan nida Abban naku Allah ya karo kasuwa mai albarka yai muku albarka gaba dayan ku"
Nida Aisha muka hada baki gurin fadin "Ameen Umma"
Wayar Umma na karba don kiran Abba na gwada tambayar sa zuwa bikin Khadija ko Allah zai sa ya barmu
*********
Gyara zaman sa yai yana kallon Baffa yace "toh kai tsoho meye damuwar ka da aure na"
Kallon sa baffa yake yana gyara zaman glass din idonsa yace so nake kaima kayi aure kamar yadda da uwan Ka yai kana kallo dai shekarar Dan uwanka biyar da aure amma kana zaune Kai baka da aiki sai zuwa gidan casu kuna juya mazaunai"
Murmushi Azlan yai har saida jerarrun hakoran sa suka bayyana yace "tsoho kaima fa Ka iya vawulence fah ynxu meye na cewa mazaunai"
Salati Baffa ya saki yace "ynxu Azlan nine na iya vawulence din"
Gira daya ya daga yace "yesss tsoho"
Comments are share plz
Mrs A.M🥰
[07/08, 22:05] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 5
Barkan mu da shan ruwa Allah y karbi ibadun mu Ameen
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Girgiza kai Baffa kawai yai yana bin Azlan dake danna min waya da kallo, ganin shirun bana karewa bane yasa Baffa cewa "kana zuwa gurin aikin kama kuwa Hussaini"
Dagowa yai daga danna wayar sa da yake ya zubawa Baffa lumsassun idonsa yace "me Ka gani tsoho"
Dan daure fuska Baffa yai kan yace"gani nai kamar baka zuwa don shashanci sun dauke ma hankali"
Hade rai shima yai sosai ya koma asalin Azlan din da Yan mata suke matukar tsoron tunkara, zakin da Maza suke tsoron shiga gonar sa, kallon baffa kawai yake yana kara kankance idonsa, tsaki baffa yai yace "ynxu dai ya maganar koyar war Ka yadda zaka fara"
Dan tsuke bakin sa yai ya juya fuskar sa gefe yace "Tsoho bana son wannan lecturing din da wanne zanji ga company ina zuwa ga kuma wani lecturing ni nasan Abie yana son na fara ne kawai sbd na zama busy sosai"
Ruwa Baffa ya dauka ya kora kafin yace "aikin companyn fa ba ko yaushe kake zuwa ba da akwai ranakun daka diba kake zuwa mai zai hana Ka karbi tayin koyarwar in yaso rabakun da baka zuwa aiki sai Kana shiga makarantar kana koyarwa"
Dan tsirawa Baffa ido yai kafin yace "mai yasa kuke son dole wai sai na fara lecturing bayan kunfi kowa sanin bana son hayaniya kuma baxan iya jurar magana mai tsayi ba ga students"
Murmushin manya Baffa yai yace "zaka iya *ZAKI* Insha Allah kawai dai ynxu kana ganin abin kamar da wuya amma daka fara zaka saba"
Hade rai yai ya kwantar da bayansa a jikin kujera kafin ya mike hannun sa na dama yana kallon zanen tattoo din zakin dake kwance a damtsen hannun sa, dan lasar lips dinsa yai kafin yace "shiknn zan yi amma sai wata shekarar baxan yi joining ynxu ba gaskia"
Murmushi Baffa yai yace "Alhamdulillah dama ai yardar taka kawai muke Jira tunda dai baxa ama dole ba Allah yai muku jagora"
A kasan lebensa ya amsa da Ameen, daga haka ya kwantar da kansa a jikin kujerar yana tunanin yadda zai fara lecturing a university sufa su Abie gani suke kamar shiririta yake yi baya maida hankali a companyn da yake aiki, wani malalacin murmushi yai yana tuna zanen gidan da yai kasancewar sa Architecture...
Baffa ganin yadda yai yasa shima yaja bakinsa yai shiru ya maida Kallonsa kan TV yana kallon Sunna TV...
*******
Cikin farin ciki muka fara waec don Alhamdulillah ina da basira sosai, satin mu biyu da fara waec mukayi yi jamb kamar dai yadda yake duk Wanda yai jamb hankalin sa ba'a kwance yake ba har sai yaga result dn nima haka yake a gurin na, duk da Alhamdulillah ina saran na yi abin kirki tunda nasan fiye da rabin questions din kuma na amsa su sbd nacin karatun da nai akan jamb din ga kuma Abba yana tayani kullum da daddare sai ya mun lesson kasancewar sa principal din makarantar gwamnati.
Jiran result nake yau sbd tun jiya an fara saki munea yau muke saran za'a saki namu, a hankali na janyo sabuwar wayata Tecno wacce Abba ya siya min satin dana fara waec ya bude min email da WhatsApp a ciki sbd wasu abubuwan ana turowa ta WhatsApp bama masu yin waec, kafin ya ban wayar sai da ya min nasiha sosai akan yadda zanyi amfani da wayar kuma ya ja mun kunne, ranar daya ban wayar su Aisha sunfi ni murna ma, Mimi kuwa sbd murna ranar ko kofar gida bata je ba tana tare dani motsi kadan zata ce nai mata hoto.
A hankali na janyo wayar na Kara tura message ga numbern da za'a turo mana jamb result dinmu ta ciki, ai kuwa ko 3 minutes ba'a dauka ba message ya shigo ta numbern, a zabure na mike ina yarfe hannuna ciki na na juyawa sbd tsoron abinda zan gani.
Da gudu na fada palourn mu ina haki, dagowa Umma tai ta kalle ni kafin tai tsaki ta juya tace "ke kuwa wani lokacin kamar baki da man kai ynxu meye na fado min a guje kamar yarinya"
Yarfe hannu nake kamar zan fashe da kuka na mika mata wayar nace "Umma duba min an turo min result dina na Jamb wallahi tsoron budewa nake Umma"
Hannu tasa ta karbi wayar ta shiga message dn ta duba, da Dan karfi tace "Alhamdulillah ya Allah"
Tsugunnawa nai na fada hannun ta nace "Umma nawa naci nayi kokari ko"
Wayar ta miko min fuskar ta dauke da murmushi mai nuni da tsantsar farin ciki, cikin rawar hannu na karbi wayar na duba, ihu nasa cikin murna kafin na kalle ta nace "Umma 228 na samu Alhamdulillah"
Itama dariya tai tace "Maza Kira Abbanku ki fada masa don shima Naga alama komai yake cikin sanyin jiki yake yana jiran yaji nawa kika samu"
Da sauri na danna numbern Abba sai da ta kusa katsewa sannan ya dauka, yana dauka ko magana ban bari yai ba nace "Abba Albishirin Ka"
Murmushi yai yana sauke ajiyar zuciya daga Jin muryar ta yasan ta samu point din da take so cikin zakuwa dason sanin nawa ta samu yace "Goro fari kar"
Dariya nai nace "Abba 228 na samu Insha Allah in naci waec dita Nima next year zan shiga university"
Dariya shima Abba yai yace "Alhamdulillah har an fara maganar university knn toh Allah ya bada sa'a ya tabbatar da alkhairin sa"
Murmushi nai nace "Ameen Abba sai Ka dawo" kashe wayar nai na zauna ina kallon Umma da take kallona, dariya nai nace "wallahi Umma tunda aka fara cewa an saki result nake gudawa ynxu ma fa wata nake ji bara naje nayi kafin su Mimi su dawo daga islamiyya yau wainar fulawa zan mana"
Tabe baki Umma tai tace "ku kuka sani nidai baxn ci wannan wainar taki ba wacce kuke cikawa yaji duk ta batawa Mutum ciki"
Mikewa nai ina dariya nace "Ummanmu knn ai Abba yana ci nasan in nayi zai ci Shi"
Kitchen na shiga na dora abincin dare ina yi ina duba Physics dina, bayan na gama daki na koma na kwanta akan gado.
Janyo wayata nai na bude WhatsApp anan naga kowa yana tura nawa ya samu a jamb, Wanda yaci na tayasu murna wadanda suka fadi kuma nai musu jaje, wata Halima Umar ceh ta tambayar ni kona duba nawa kuma nawa na samu, screenshot din danai na tura musu, nan suka hau taya ni murna don kusan dukan su nafi su samu.
Safiya idi ce tace dama Batul Auwal kokarine dake shiyasa bakya shiga cikin mutane ana hira, emoji din murmushi kawai na tura musu don bana magana sosai a group din haka kuma ko a school ban cika magana ba don bana son tashin hankali mutane da yawa sunsha samu na su fada min irin gulma ta da ake akan wai bana shiga cikin jama'a ana hira dani sbd ina da kyau kuma ina da kokari sai dai kawai nace Allah ya kyauta don ni tun da Mimi tazo duniya naja jikina da mutane sbd wulakanci da nuna kyama da wasu suke min, wai a haka don Abba ya chanja min makaranta knn ma.
Ina kwance ina game Mimi ta fado jikina tana fadin "Washhh Maa dita bayana lugude yake"
Ajiye wayar nai ina dariya nace "Mimin MAA dinta bayan ne yake lugude"
Lumshe idonta tai tace "uhm Maa na gaji sosai kawai ki barni na kwanta bacci abuna"
Mikewa nai nace "tashi magriba ta matso ki bari in anyi isha sai ki kwanta ko baki so ki samu ladan sallah ne"
Turo baki tai tace "inaso mana Maa"
Kaya na chanja Mata muka fito Palour ana nake fadawa su kamal nawa na samu a jamb, sai sabuwar murna ta barke mana Umma na zaune tana kallon mu fuskar ta dauke da murmushi, a kullum ta kalli yaran nata taga yadda suke hada kansu komai tare suke farin ciki ke lullube ta tana addu'ar Allah ya cigaba da hada mata kan yaran ta.
Sai bayan Magrib da Abba ya dawo hadda tsire ya siyo mana ai kuwa mun ji dadi sosai, wainar fulawar na soya mana nida Aisha sannan na bawa Aisha ta kai palour, sai da na wanke abinda muka bata Wanda Aisha bata wanke ba sannan na shigo palourn, fridge na nufa na dakko mana Zobo Mai sanyi na ajiye a tsakiyar palourn.
Mimi da tun da aka ajiye tsiren take zaune tana kallon ledar ce ta kalle ni tace "Maa party muke yi yau"
Dariya muka sa Mata mu dukan mu, Abba ne ya janyo ta jikin sa yace "zo na sa miki tsiren nan a baki dai ki dandana ko hankalin ki zai kwanta"
Washe yan kananun hakoran ta tai ta zauna akan cinyar sa, cikin nutsuwa muke ci muna hira rabin hirar duk nida Abba ne ina tambayar sa yadda university take yana bani amsa dai dai da tambaya ta, ji nake kamar na janyo tym na ganni a university a matsayin student, bayan mun gama physics na dakko Abba yana kara koya min inda yake ban wahala kasancewar Shi zan rubuta gobe sai wajen 11 na tafi daki lokacin Mimi da Aisha sun dade da bacci Nima fitanai toilet na kama ruwa nai alwala, kwanciya nai a gefen Mimi ina fuskantar ta lumshe idona nai da hawaye ke son zubo min a hankali na dora hannuna akan fuskar ta nace "INA KAUNAR KI MIMI duk ta yadda aka same ki mu muna sonki sosai kuma zan kasance mai kaunar ki har karshen rayuwa ta."
Kallon fuskar ta nake da bana gajiya da kalla ina tunanin duk yadda akai Mimi da Mahaifin ta take kama nidai kowa ya ganni yasan bana kama da Mimi don Mimi fara ce tass har wani jaja take ni kuma Baxa a