Showing 42001 words to 45000 words out of 94393 words
Chapter 15 - TASWIRAR KADDARA BOOK COMPLETE PDF .txt
shine aka fake da cewa fyade aka mata.
Ranar da aka sallami su Khadija, ina xaune a tsakar gida ina tankade garin masarar da zan mana tuwo anjima suka shigo Umma ce rike da Khadija dake tafiya a hankali sai Yakumbo a bayan su.
Dagowa nai muka hada ido da Khadija kawai ta ware min hannunta, cikin karyewar zuciya na mike da gudu naje na rungume ta itama rungume ni tai kawai muka fashe da kuka.
Umma itama da kukan yazo mata shigewa daki tai tana fashewa da kuka, Yakumbo ce ta goge hawayen ta ta shiga rarrashin mu.
Da kyar mukai shiru na rike ta muka shiga palour, sai dai me muna zama Uwani da Hama suka shigo.
Kallon Khadija Uwani tai tace "sannun yar nan ashe haka abu ya kasance toh Allah ya kiyaye gaba amma kam an cuce ki ynxu ke waye ma zai aure ki bayan wannan tabon da aka shafa Miki."
Hama ce ta cafe da fadin "ai abin tausayin ma in an samu wani ya aure ta tofa iyalan ta ne abin tausayi shiknn sai ana musu gori cewa Uwarsu ba budurwa aka same taba.."
Umma da ta fito daga daki tace "bakin ku ya sari danyan kashi , Insha Allah ba abinda zai biyo baya sai alkhairi kuma kaddara ce tana kan kowa"
Da sauri Uwani tace "dakata Sadiya ban gane mai kike nufi da kaddara na kan kowa ba badai fata kike ace muma yayan mu amusu fyaden bakoh?"
Hama tace "kyaleta Uwani inaga bakin ciki take mana mu ya'yan mu suna nan da budurcin su ita kuma nata gashi an dauke na daya saura biyu"
Umma zatai magana Yakumbo ta daga mata hannu, kallon su Uwani tai tace "xaku iya tafiya in kun gama fitsarar taku zan hadu da mazajen naku"
Cikin dan tsoro suka fita don sun san halin Yakumbo bata sakar wa sirika fuska kuma yayanta suna matukar Jin maganar ta, tabbas in ta fada musu sun kade..
Matsa hannun ta nai dago idon ta dake zubar da hawaye tai ta kalle ni, murmushi na sakar Mata ina goge Mata hawayen...
A daren ranar na nunawa su Abba abin hannun dana cire a hannun mutumin, naso yarwa Abba yace na ajiye wata ran zaiyi amfani.
Tun daga ranar rayuwar mu ta sauya koda muka koma makaranta gaba daya sai aka tsane mu duk inda muka wuce sai an nuna mu ana fadin gasu can waccan ce wacce aka kama tana iskanci, a islamiyyar ma bamu tsira ba gashi a unguwa duk kawayen mu sun daina kulamu.
Hakan yasa nima na Kara zama mara hakuri da farko in aka zage mu shiru nake amma daga baya daina shiru nai ana zagin mu ina ramawa in ta kama ma na zaune yan iska mu dambatu.
Dole Abba ya chanja mana makarantar boko da islamiyya, kawayen layin mu kuma duk na watsar da Yan iska, a unguwar ma da maman Hidaya kawai muke shiri don lokacin tana amarya.
Rashin kawayen da nai yasa muka Saba sosai da cilla, a gidan su ake mana markade kuma ni nake kaiwa, tun in nakai muna fada da shi sbd a lokacin yana ganiyar rashin jinsa duk da ya girme ni kuma in ya min abu ramawa nake har muka zo muka Saba sosai.
Wata uku da faruwar lamarin Khadija ta soma wani irin haske, ga kwadayi da ba ruwanta amma ynxu komai ta gani sai ta ci ita tasa na fara kayan cake sbd son da take masa, ga cin abinci ko yaushe bakinta cikin motsi yake.
A wannan lokacin kuwa hankalin Umma ba karamin tashi yai ba don ta fahimci ciki ne da Khadija, koda ta fadawa Abba ce Mata yai ta bari a tabbatar tukun.
Asibiti ya kai Khadija gwajin farko likita ya tabbatar da ciki ne da ita na wata uku har da sati biyu, zan iya cewa tashin hankalin da muka shiga baxai iya misaltuwa ba, ba yadda Umma batai ta a zubar da shi amma Abba da Yakumbo suka hana.
Uwani da Hama kuwa an samu abin yamadidi a unguwa yadda suka sako Umma a gaba sai da Yakumbo tace musu duk Wanda ya Kara wata magana sai tasa mijinta ya sake ta sannan suka shiga taitayinsu.
Nidai na tsani cikin Khadija bana sonsa don kiyayya nake nuna masa kuru kuru wani lokacin har dukan cikin nake bama daya soma girma.
Tunda cikin yai wata biyar Khadija ta daina fita ko kofar gida, tayi kiba sosai muna iya kokarin mu ganin mun kwantar Mata da hankali, Abba ne ya bawa Umma kudi taje kasuwa tayi siyayyar baby badon ranta naso ba.
Cikin Khadija tun da ya shiga wata tara rabonta da lafia knn, kullum cikin ciwo take yau ciwon baya gobe ciwon kafa jibi ciwon ciki.
Muna kwance a katifar mu hira muke Sama Sama don bacci nake ji, kallon Khadija nai data min kyau sosai tayi haske Dan tsaki nai nace "ke dallah ki daina kallona haba kin ishe ni"
Murmushin ta mai sanyi tai tace zanyi kewar ki yar uwata, ina matukar kaunar ki sosai yar uwata
Gaba nane ya buga da karfi cikin dauriya nace "ina zaki da za kiyi kewar tawa"
Murmushi kawai tai ta janyo hannuna ta dora akan cikin ta, Dan zabura nai jin cikin yana motsi sosai, ganin yadda nai ta fashe da dariya tace "matsoraciya"
Murmushi nai kawai duk da na sani cikin Amma sai na kasa dauke hannu na, a hankali itama ta dora hannun ta akai tace "baby kina ji ko wannan itace mamanki sunanta Batul kiyi mata biyayya sosai tana sona"
Dan hade rai nai Zan janye hannuna tai Maza ta rike tace "Batul meyasa baki son cikin nan"
Dan kallon ta nai sai na juya nace "sbd cikin mutumin dana fi tsana ne a rayuwata Wanda yai silar lalacewar rayuwar mu"
Murmushi mai sauti tai tace "amma ai hadda jinina a jikin cikin koh, kuma nasan ni kina matukar sona baxa ki kaunaci cikin ba kodan sbd ni batul, yau cikin nan in ya fito duniya zai budu idonsa ne a matsayin kece mahaifiyar sa in kina nuna masa kiyayya ya zaiyi?"
Zare hannuna daga kan cikin nai nace "naji zan kokarta"
Dariya kawai tai tana lumshe idonta, daren ranar haka kurin na kasa bacci sai zubawa Khadija dake bacci cikin nishadi ido nai, sai gaf da asuba na matsa jikin ta na rungume ta ina sauke ajiyar zuciya.
Washe gari da Asuba Khadija ta fara nakuda, a rikice Yakumbo dani da Abba muka nufi asibiti da ita, ko da muka je nurse din data dubata tace ce haihuwa ce mu zauna a asibitin.
Shiru amma har la'asar sai wahala da Khadija take sha kawai, kanwar Umma Aunty Bilkisu itama tazo gurin azahar.
Nidai sbd tashin hankali ko ruwa ban shaba nayi zuru zuru sai gab da asuba sannan haihuwar tazo, labour room aka shiga da ita a lokacin Abba daya koma gida shima ya zo don kasa bacci sukai shida Umma gashi kuma sunyi kawaicin kin kiran wayar su Yakumbo su tambaye su.
Minti 40 da shigar su nurse ta fito da guje ta nufi office din likita sai gasu sun dawo da likitoci biyu, mudai muna tsaye a gun muka ji kukan jaririya.
Likitan ne ya fito yace wace "Batul a cikin ku"
Cikin bugawar zuciya Abba ya nuna ni, daga Kai likitan yai yace "biyo ni".
Da wani irin rawar jiki nabi bayansa har cikin labour room din, a kwance Naga Khadija ta kara haske sosai dukda an mata kasanta zanu hakan bai hanani ganin yadda Jini yake gudu a jikin taba.
Nurse ce ta miko min babyn data shirya cikin fararen kayan sanyi sai motsi take tana tsotsar hannu, Dan zuba mata ido nai ina tasbihi a raina sbd tsantsar kyaun yarinyar kamar yar larabawa lokaci daya naji wani masifaffiyar kaunar ta yana huda zuciya ta.
Cikin dashewar murya Khadija ta miko min hannun ta tace "zo yar uwata"
A hankali na daga kafa ta har na isa kusa da ita, hannuna ta kama tana murmushi ta kalli fuskar yarinyar sai ta sa dariya mai hade da kuka, cikin muryar ta data dishe tace "ga yarinyar kinan batul na bar miki ita duniya da lahira dama kuma taki ce, bana son tasan cewa bake kika haife taba don Allah kina sonta"
Da sauri na daga mata Kai hawaye suna zuba daga idona, murmushi tai tace "in anga babanta kice masa na yafe masa Batul"
Dan hade rai nai nace "ni baxan taba yafe masa ba"
Girgiza kai tai tana dariya tace "kicewa Umma da Abba da kowa ya yafe min kinji"
Tsaki nai nace "ke Khadija bansan iskanci meye kike mun magana kamar wata mai barin
Wasiyya"
Murmushi tai jikin ta na rawa ta dora hannun ta akan yarinyar tace *"ALLAH YA MIKI ALBARKA YA KARE KI ADUK INDA ZAKI SHIGA"*
Murmushi nai nace "Ameen"
Hannuna ta rike tana kallona fuskar ta dauke da murmushi ta shiga yin kalmar shahada ni ma sai na shiga yi ina sakar mata murmushi don a nawa tunanin tana yine kawai.
Idonta ne Naga ya tsaya cak sai hannun ta daya saki, murmushin dake Kan fuskata ne ya dauke nace "Khadija ya kikai shiru"
Girgiza ta na shiga yi amma bata motsi gaba daya jikinta ya saki, a rikice na juyo gurin doctor da nurses din da suke tsaye suna kallon mu cike da tausaya wa, cikin tashin hankali nace "doctor bata motsi"
Janye ni wata nurse tai ta fitar dani daga dakin, muna fitowa ta kalli Abba tace "sai dai hakuri Allah ya mata cikawa, Allah ya jikanta"
Salati Yakumbo da Aunty Bilkisu suka saki yayinda Abba ya rufe idonsa hawaye yana zubo masa.
Ni kam daina gane komai nai sai binsu da ido da nake yi kawai, gawar Khadija aka bamu lokacin dasu Kawu Nasiru suka zo da mota.
Gida aka nufa da ita ina rike da babyn a jikina na rungume ta sosai, gaba daya kaina daina aiki yai sai bin mutane da kallo kawai nake.
Umma ba karamin dauriya tai ba ita da Yakumbo ne suka ma Khadija wanka suka shiryawa aka ajiye ta a tsakar gida kafin azo a fita da ita, Aisha dasu kamal sai kuka suke suna zaune a gabanta suna mata addu'a kamar yadda Aunty Bilkisu tace musu.
Jikina na rawa lokacin dana ga anzo fita da ita na karasa inda take, akan gwiwowina na tsugunna na bude fuskar ta babyn na dora akan kirjin ta nace "Khadija ta ki tashi kinji, ni nasan Wasa kike min ba ki mutu ba ga babyn fa kin ganta mai kyau da ita, don Allah in tsorata ni kike don nace bana son babyn wasa nake miki Allah ina Santa"
Kuka mutanen gurin suka kara saki, Abba ne yazo ya dauki babyn ya mikawa Yakumbo don itama ta farka sai ihu take, janye ni ya shiga yi ina mika hannu ina kamo makarar ina fadin "don girman Allah Abba kayi hakuri kace kar su tafar min da ita wallahi Wasa nake mata ina son yarinyar"
Umma ce ta rungume ni kawai na tusa kaina a jikinta na fashe da wani irin kuka, itama lumshe idon ta tai hawaye masu zafi suna zubo mata a daidai lokacin da ake fita da gawar Khadija...
(Innanillaihi wa innanillaihir raji'un😭😢😭 Allah ya jikan Al'ummar musalmai muma in tamu tazo Allah yasa mu cika da kyau da Imani Ameen )
Mutuwar Khadija ta girgiza mutane da dama, ko su uwani sunji mutuwar ta tun daga lokacin na dauki kauna da soyayyar da nake ma Khadija ta koma kan Khadija small, wacce aka mayar Mata da sunan khadija nake ce mata Mimi.
Duk abinda na gani in har mimi tana so sai na siya Mata, sbd ita na fara Sana'a don na ringa siya Mata Kaya da abin wasa duk da ba abinda Abba ya rage ta dashi.
Tunda ta budi baki take cemin Maa don a fahimtar ta nice mahaifiyar ta, haka kuma duk Wanda ya sanni bayan mutuwar Khadija dauka yake nice asalin mahaifiyar Mimi.
Mutuwar Khadija yasa na kara tsanar ko waye baban Mimi kullum sai na masa Allah ya isa ba tsallake duk da Khadija tace ta yafe masa ni ban yafe ba.
Yusuf ya kasance saurayin Khadija ne wanda yake sonta, kowa a familyn mu ya san soyayyar da yusuf yake ma Khadija itama kuma tana sonsa, lokacin da tsautsayin ya fadawa Khadija baya nan yana Malaysia karatu sai bayan rasuwar ta ya dawo.
Ba karamin mutuwar ta yaji ba da tausayin Mimi shine ynxu kuma yake nuna cewa yana Sona da aure kuma zai rike min Mimi.
Ni Kam mai zanyi da Yusuf Allah na tuba in ba cin amana ba taya Zan auri Wanda Khadija ta taba so ai har abada.....
*Cigaba*
Hawaye Abba ya share yace "wannan shine asalin sanadin Mimi kuma a takaice rayuwar Mimi da yadda aka same ta."
Hawaye Baffa ya share yace "tabbas kunga jarrabawa amma don Allah kuyi hakuri dan ynxu Ka Haifa baka haifi halin Saba"
Abie da jikinsa ya gama sanyi ya kalli Azlan da kansa yake sunkuye yace "Amma Ka bani kunya Azlan, ban taba tunanin cewa haka kake na Ashe bayan yawon club har fyade kake ma kananun Yara"
Da sauri ya dago ya kalli Abie sai ya juya ya kalli Baffa yace "Abie baka yadda ina da budurci naba wai?"
Xaro ido Kawu Kabiru yai yace "dama Maza suna da budurci"
Cikin tabbatar wa Azlan ya daga kai yace ban taba kusantar wata mace ba Kuma ni yadda nake tanadin budurcina ai baxan haike wa yarinya ba don nasan ko babba
Ce na kamata mutuwa zatai
Junaid ne yace na shiga uku Azlan meye haka don Allah wai Kai baka da kunya
Kafada ya daga yace Junaidu ina zanyi kunya kana ji ana tantamar budurci na
Abie ne ya mike a fusace ya "dauke fuskar sa da mari cikin fushi yace don ubanka in ka kara magana sai na nuna ma ni dinnan Muhammad nina haife Ka kuma nafi Ka iskanci, abin hannun da aka cire a hannun mutumin naka ne, mimi dakai take kama kaine mara ji duk cikin Yayana sannan ga dan uwanka nan shekarar sa biyar da aure matar sa ko batan wata bata bata yi ba sbd baya haihuwa kana kallo kullum cikin yawon neman magani yake a duniya shi kake so mu zarga ko me?"
Azlan da tunda Abie ya mare sa ya sunkuyar da kansa a hankali a dago fuskar sa datai jajir idonsa ya kada yayi wani irin ja gashi dama yau ba'a sa masa kwalli ba cikin rawar murya yace kayi hakuri Abie karya nake MIMI *JININA CE YARINYA TACE*
Yau dai ba korafi na muku da yawa🥱
Comments Nd share plz
Mrs A.M🥰
[31/08, 16:31] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️
*TASWIRAR KADDARA*
♠️♠️♠️♠️♠️
Written by
Mrs A.M🥰
Page 24
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Duk mutanen palourn zuba masa ido sukai, ganin haka yasa shi mikewa a hankali ya durkusa a kusa da Abba yace "don Allah ku yafe min kuskure ne da sharrin zuciya so daya na taba yi ashe hadda rabo"
Baffa ne yace "meye haka kuma"
Juyo wa yai ya kalli Baffa yace "lokacin nima kuruciya ce ke damuna, amma na gane kuskure na tun daga lokacin ban sake ba".
Kallon Abba yai yace "don Allah ku yafe min, Allah ya jikan Khadija ya gafarta mata."
Wani murmushi Abba yai tun daga lokacin da yaron ya fara magana yake karantar sa tabbas wani abu ya darsu a zuciyar sa amma ya gyada kai yace "bkm nidai na yafe ma kuma itama Khadijan tace ta yafe, zan yiwa mamanta magana itama nasan zata yafe din insha Allah."
Baffa ne yace "Alhamdulillah, dama haka muke so amma tabbas Ka cika mahaifi na kwarai ba ko waye bane za'a ma diyar sa wannan abun amma ya yafe lokaci daya da alama itama Khadijan tana da kyaun Hali, Allah y jikanta"
Sai da aka Kara godewa su Abba akan yafiyar da sukai sannan Baffa yace "in ba damuwa ina nemawa Azlan auren babar Mimin Batul"
Da sauri Abba ya kalli Baffa sai kuma ya kalli su kawu Nasiru.
Azlan ma dagowa yai ya bude baki zai magana Baffa ya zare masa ido dole yai shiru.
Kawu Nasiru ne yace "zamu yi magana akai insha Allah Baffa, duk yadda muka ce zamu Kira ku".
Murmushi Baffa yai yace "Allah yasa muji alkhairi".
Mikewa Azlan yai ya fita yana sakin wani makirin murmushi ransa fess....
Bayan tafiyar su Baffa kallon Kawu Nasiru Kawu Kabiru yai yace "Yaya ya kuke gani ynxu nidai bansan Mai zance ba"
Murmushi kawu Nasiru yai yace "da alama gidan dattako ne, kuma a yadda yaron ya bada hakuri yana da hankali kamar, sannan bayan wannan hakan da za'a yi shine rufin asirin Mimin kaga zata tashi cikin dangin mahaifin ko dan sbd gaba, sannan kaga da alama baza a iya raba batul da Mimi ba don haka duk lokacin da ita Batul din tai aure ta tafi da Mimi gidan aurenta ko shi mijin bai goranta ba a cikin dangin sa sai an samu wani yayi".
Gyada kai Kawu Kabiru yai yace "tabbas haka ne Yaya kuma kaga ita Mimin ko auren ta aka tashi sai an samu Wanda ya ce ba mijin Batul ne mijin taba kaga dole a binciko dangin Mahaifin ta, amma in suna tare da Mahaifin nata komai zai tafi lafia insha Allah"
Kallon Abba sukai da tunda suka fara magana baice komai ba amma fuskar sa dauke da murmushi sannan Kawu Nasiru yace "bakai magana ba kai ya kagani"
Yalwataccen murmushi Abba "yai yace hakan shine daidai Yaya amma zan same su na fada musu tukun aji ta bakin yarinyar, sannan kaga sai na fadawa Yusuf shima tunda ya nuna yana son Batul din da aure"
Sai da suka kara tattauna wa sosai sannan kowa ya shige gida don fada ma iyalin shi bayyanar mahaifin Mimi.
Lokacin da Abba ya shiga gida tuni Aisha ta soma fesawa Umma duk