Showing 33001 words to 36000 words out of 165076 words

Chapter 12 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74038

ta shigewarta cikin gida. Sai Ammar ne ya kama Ummi suka shiga cikin suma. Babu motsin kowa a gidan da alama yaran duk sun fice. Hajiya mama kuma maybe tana barci ko kallon nata na masifa dan bata gajiya da sanya ido a television, shiyyasa jikokin nata har tsiya suke mata akan hakan.


Ko mintuna ashirin basuyi da shigowa ba maƙwafta suka fara shigowa ƙara yima Ummi sannu. Ciki harda Zahidah da Hafsat tare da iyayensu. Sune suka taimakawa Hibbah wajen gyara gidan tsaf. Suka kuma daura girki. A kitchen ɗinne suka sami damar mata tambayar abinda ya faru ranar game da tafiya da ita da ƴan sanda sukayi.
Duk da aminanta ne tun ƙuruciya sai bata faɗa musu komai ba yanda ya faru saboda tuno gargaɗi da akai mata akan idan ta fitar da zancen za'a saka mata ƴan uwa a tarko. Ta dai basu labarin iya abinda zata iya. Sosai sukaji takaici har cikin ransu. Nan fa suka shiga labarin rauni da hukumomin tsaron ƙasar nan suke da shi.
Zahidah tace, “A kullum ca ake ana aiki amma babu alamar hakan a ƙasa. Shin laifin gwamnati ne ko na jami'an tsaron?.”
Cikin taɓe baki Hibbah ta amshe da faɗin, “Kema dai ƙya faɗa Zahidah. Ita kullum gwamnati tana faɗar kuɗaɗe da take warewa domin harkar tsaro. Amma su jami'an tsaron kullum ca suke basu da kayan aiki isassu. To wai kuɗinne ba'a warewa? Kokuwa jami'anne basa saye? kasa kuɗin suke a tebir kowa ya dauka kasonsa?”.
Da tsantsar takaici Hafsat tace, “Duk ma yanda sukeyi ɗin ai akwai ranar tonon asiri. Ranar da babu wani gacci ko mayafi da ya isa lulluɓe tsiyar da aka shuka aka binne. Ranar da za'ai walƙiya muga kowa da ayyukansa”.
A tare Zahidah da Hibbah sukace, (Insha allahu kuwa).
Haka dai suka cigaba da tattauna abubuwa da dama har suka kammala girkin suka sake gyara Kitchen ɗin. Koda suka fito ɗakin Hibbah suka wuce dan har yanzu ƴan dubiya nata shigowa. Sai dai bayan maigadi ko karen da ke a cikin gidan har yanzu bai leƙo ba. Dama kuma basuje asibitinba. A cewarsu ai ba'a sanar musu bata da lafiya ba.


Sai dare samarin na Ummi suka dawo. zuwa lokacin sashen tsit da ga Ummi sai Hibbah kawai. Hibbah ma tayi barci a kujera dan akwai gajiyar asibiti tare da ita. Sai sautin kiɗa dake tashi da ga sashen momynsu Junaid da hayaniyar ƴammatanta. Da alama wani fati sukeyi, duk da dai shan kiɗa a gidan ba sabon abu bane ba dama.
Sannu Ummi tai musu. Yayinda suka zagayeta kowa nason jin yaya karfin jikinta?. Cike da jin daɗi da fara'a take amsa musu. Kafin tace suje suci abinci kar yayi sanyi. Ammar zai tada Hibbah Ummi ta hanashi.
“ALLAH ka tada ita sai naci gidanku, ka barmin yarinya ta huta ta gaji wlhy, dan tamace kanta ke ciwo”.
“ALLAH yasa gaskiya ne Ummi. Ni naga a kwanaki ukun nan wani sabon hankali take ji da shi. Ko ciwonki ne ya sata nutsuwa oho”. Ammar ya faɗa yana dariya.
Suma su Yaya Muhammad duk murmushi sukayi suna nufar dining.


★★★

Har washe gari babu wanda yazo ya duba Ummi a cikinsu hajiya Mama. Abba dama bai dawoba har yanzun. Ummi ko a fuska bata nuna ta damuba. Haka suma su Yaya Abubakar babu wanda yace uffan akan hakan. Sai ma tarkata Hibbah sukai ta wuce islamiyya tun safe kasancewar yau ɗin weekend ce akwai tahfiz da take zuwa dama har suma kansu.
Badan taso zuwan ba ta tafi harda ƙwallanta dan taga abokin hamayyarta Ammar yau bazai je ba. Da yake a kafane babu nisa ita kaɗai ta fita. Sai da ta fitane taci karo da Hafsat da Zahidah sun taho biyo mata dama. Gaisawa sukai da tambayar jikin Ummi sannan suka wuce islamiyyar.


Islamiyya ce babba matuƙa. Dan tun da ga ƴan shekara uku har zuwa saba'in duk zasu iya karatu a cikinta. sai dai su yara da ga shekara uku zuwa ashirin da biyar suna zuwa ne tun safe har yamma. Daga ashin da shidda zuwa har tsoffi suna zuwa bayan sallar azhar har magriba, kuma iya weekend ne kawai. Dan haka su su Yaya Muhammad sai karfe biyu zasuje. Itace dai da Ammar dama ke tafiya tun safe. Ammar kuma yau akwai abinda zaiyi shiyyasa bazai je ba.
Kamar kowanne sati yau ma sun ɗauki darasi daban-daban har zuwa ƙarfe biyar na yamma da aka tashe su. A ƙafa suka taho Zahidah da Hafsat nata hira banda Hibbah. A yanda suka lura gaba ɗaya ta zama wata shiru-shiru. Kafin faruwar wannan al'amarin a kowane sati sukaje islamiyya sai ta addabi kowa a ajin ko ta takalo faɗa. Su kansu malam sun buga har sun bari, dan mafi yawancin lokaci ƙoƙarin ta ne ke cetonta akan wani tsiyar idan ta tafka.
Cike da jin haushi Hibbah ta ja tsoki tana tsayawa cak da ga tafiyar da sukeyi. Kallonta Zahidah da Hafsat sukai cikin alamun sonjin lafiya?. Bata tanka musu ba, sai kallonta da ta maida kan motar da ke bin bayansu ta gefen titi tunda suka fito Islamiyyar. Suma su Hafsar ɗin sun lura tun ɗazun, sai dai basu kawo a ransu mai motar su yake bi ba. Musamman da ya kasance ya ɗan basu tazara.
Domin tabbatar da su ɗin yake bi a bayyane yay fakin dai-dai inda Hibbah da ta cika tai fam da takaicinsa take.
Cikin takun nutsuwa da cikar haiba ga ma'abocin kallo ƙyaƙyƙyawan saurayi mai tarin kamala ya sanyo kafarsa ƙasa dai-dai yana buɗe ƙofar motar mai baƙin gilashi (tinted glass). Wani shegen ƙamshin turarensa ne ya daki hancunansu tare da sallamar da ke fita cikin ƙasaitacciyar muryarsa mai tarin nutsuwa da sanyi.................✍



*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥












*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*








*_Typing📲_*






*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*


https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share


*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*


https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb


_________________________




*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻


*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*


_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._


*_Muna da haɗin_*


_Turaren wutane_
_Humrh_
_Kulacham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_


_Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_


*_Da magungun nan mata_*
_Irin su kaza_
_Tantabara_
_Tsumi_
_Gumba_
_Zuma_


*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*


Wushishi road KADUNA


08067807620
09057713999




_________________________




*_Chapter Thirteen_*


............Gaba ɗaya jin su Hibba ya ɗauke ɗaf a cikin kunnuwansu lokaci guda. Dukansu sun zuba masa ido tamkar waɗanda sukai gamo da wata baƙuwar hallita. Namiji ne tsayayye da za'a iya kiransa namijin gaske a kowacce irin nahiya ko ƙabila. Sanye yake cikin shadda oxblood da ta fidda ainahin kalar fatarsa mai sheƙi. Fuskarsa cike take da ƙasunba da wani madaidaicin gemu mai kama da na gayu irin na ustazan wanan ƙarnin (😳Bily🤐).
A kallo ɗaya zaka fahimci rashin son hayaniya daga garesa. Da alama kuma ba mutum bane mai yawan sakewar fuska a mu'amula ko a yanayi.
Ganin sun shagala wajen kalon sa ya saki wani shegen murmushi yana ƙarasa takowa gaban Hibbah gab. Haka kawai takaici ya kama Hibbah da kallo guda tai masa ta ɗauke kanta tun ɗazun. Cikin ɓata fuska da yatsineta ta ce, “Malam lafiya? Tun ɗazun ka ke ta binmu sai kace wani mai gadin mu”.
Murmushi ya kuma saki, jerarrun haƙoransa farare na bayyana. Ƙoƙarin saka ƙwayar idanunsa cikin nata yake, amma sai taƙi. Sai ma harara da ta sake zuba masa ta ɗauke kai. A hankali taja siririn tsakin da yasa Hafsat da Zahidah shurin ƙafarta da galla mata tagwayen mintsini.
“ALLAH ya isa”. Ta faɗi tana hararsu bayan ta saki ƴar siririyar ƙarar data saka baƙon nasu ƙyalƙyalewa da wata dariyarsa da ke fita a nutse. Harara ta sake zuba masa zata bar wajen yay saurin shan gabanta.
Haushi ya sake kama Hibba. A tsiwace tace, “Malam kana shigarmin hanci fa”
“Ba malam ɗin bane ai. *_Muhammad Shuraim Aliyu_* ne. Idan kina son nabar shiga hancinki address da number kawai nake buƙata”.
“Baka da man kai” ta faɗa tana raɓawa ta gefensa ta wuce batare da ya samu koda harar ba yanzun. Badan Zahidah da Hafsat sun so ba sukace masa (bye) suna bin bayanta. Motarsa yay azamar komawa ya cigaba da binsu duk da uban sauri da Hibbah ke zabgawa tamkar zataci da ka. Jitake a ranta da da akwai lungunan da zatabi ya kaita gidansu da shi zatabi dan taga ƙarshen naci. Sai dai kash, tun daga islamiyyar har zuwa gidansu layine ɗoɗar.
Itace ta fara shigewa gidansu, dan ata wannan hannun itace farko kafin su Hafsat. Dan haka mai mota Shuraim ya tsayar da su Zahidah. Dole suka tsaya dan baiyi kama da wanda za'a cigaba da yarfatawa ba.
“Kuyi haƙuri fa na takura muku, naga mahaɗi nane babu damar yin sakaci. Dan ALLAH miye sunan ƙawarku?.”
Kallon juna Hafsat da Zahidah sukayi. Roƙonsu da ya sake yi ne ya saka Hafsat cewa, “Muhibbat! Aliyu Hamza”.
“Masha ALLAH, nice name. Nan ne gidansu?”.
A taƙaice suka bashi amsa da eh. Shima sai bai sake jan zancen ba yay musu godiya ya koma motarsa ya wuce.
“Gaskiya Hibbah ƴar yawa ce, amma fa guy ɗin nan ya haɗu ALLAH. Yaci sunansa Muhammad Shuraim”. Zahidah ta faɗa tana lumshe ido.
Hafsat tace, “Shiyyasa ai na faɗa masa sunanta. Waya gaya mata ana sakaci da irin waɗan nan gayun a wanan ƙarnin.”
“Barta ai zamuyi maganinta. ALLAH dai yasa har a hallaya haka yake, da kuma zancen aure yazo mu raƙwashe. Dan zanso Hibbah ta auri guy ɗin nan kodan ta kere sa'a a cikin shaggun su Amlah ɗin gidansun can. Masu shegen kakkafi da son asani. Su adole suna hawa motoci. ALLAH idan suka ga guy ɗin nan sai sun haukace. Sai dai kuma ya musu nisa da na Hibbarmu ne”.
“Insha ALLAH”. Cewar Hafsat tana ƙyalƙyala dariyar mugunta. dan harta hango idon ƴan gidan su Hibbah da kullum suke mata iyayi akan su sun waye, sun girmeta. Suna hawa motocin da Abbansu ya saya musu su ƴaƴan so banda Hibbah.


★_____________★____________★


A ɓangaren Master kam tunda suka koma L.E street shida yaransa sukai luf abinsu tamkar basa ƙasar. Da wannan damar jami'an tsaro suka sami na barazanar cewar ya tsorata da harin da suka kai masa ne, ƙilama sun sami nasarar kashesa dan sun harbesa.
A lokacin da yaga wannan rahoto ba ƙaramin dariya abin ya bashi ba ƙwarai da gaske, ya saki wani malalacin mmurmushi mai ƙunshe da ma'anoni masu yawan gaske da shi ya barma kansa saninsu. Har cikin ransa yana mamakin sai yaushe ne ƙasarmu ta gado zata canja ne? Ji dai shareriyar ƙarya da wanɗan da suke amsa sunan iyaye manyan ƙasa suka karkace suka gilla dan kawai su burge su kuma kankaro ma kansu girma.
Yaransa kansu abin ya basu dariya. Har cikin ransu suna tausayin ranar da Master ɗinsu zai maida murtani ga waɗan nan mutanen. Inhar bai kaisu kwance ba tabbas sai ya sakasu kuka da hawayensu ko su ajiye aikin koda lokacin ritaya ɗinsu baiyi ba.
Shi ba'a sakashi yin abu dole, dan haka baice uffanba sai ma sake lafewa da yay domin tabbatar da zancen nasu. Yayinda a gefe kuma idanunsa ƙur akan batun matar gwamna da hukumar sa'ido akan ta'annati da kayan gwamnati take bin cika har yanzun. Jira suke suyi wani sakaci ko kaɗanne ya sake bankaɗo wasu surukan nata ma duniya harma da su kansu...


____________★__★__★___________



“K kuma lafiya kika shigo kina cikama mutane baki da iska?”. Ummi ta faɗa tana kallon Hibbah da dawowarta kenan da ga islamiyya.
“Babu komai Ummi. ALLAH yunwa nake ji ne”.
“Shi abincin da kika tafi da shi fa?”.
“Ummi naci fa. Kawai wata yunwar dai nake sake ji”.
“To ALLAH ya ƙyauta, sai kije ki fara yin wanka kiyi salla sannan kizo kici”.
“Ummi dan ALLAH ki barni in fara ci ni dai”.
Komai Ummi bata sake ce mataba. Sai ma miƙewa tai ta shiga takawa a hankali domin zuwa ɗakinta tai salla. Dan har yanzu jikin nata bawai yayi ƙarfi yanda ya kamata bane. Abincin ma Yaya Usman ne ya yisa kafin su wuce tasu Islamiyyar.
Sai da Hibbah taci tai nak da abinci sannan ta shige ɗakinta. Bata fito ba sai wajen 8:30 da tajiyo hayaniyar yayunta. Cike da ɗokin dawowar tasu ta fito. sai dai ganin harda Isma'il ya sata yin turus.
Komai babu wanda ya ce mata a akan yanayin nata. Sai ma tsokanarta faɗa da Ammar ya shigayi. Amma sai bata tayashi sunyi ba. Masifa ma taketa faman yi a ranta na yanda yayun nata suka sakema Isma'il ɗin kai kace ɗan gidan ne. Shi kansa yanda yake komai kansa tsaye sai ka rantse gidansu ne.
Bata wani jimaba tai musu sai da safe ta shige, ta barsu a falon suna kallon ball suna hira da cin abinci. Ummi ma tunda ta leƙo suka gaisa da Isma'il ɗin ta koma ciki abinta. Dan haka Hibbah bata san sanda Isma'il yabar gidan ba.


Washe gari dai an tafi islamiyya babu fushi. Sai dai kuma damuwar ƴan sandan can da ke damunta har yanzu ya sakata komawa wata silent kwana biyun nan. Ko magana ma bata cika sakin jiki tayi ba. Sannan har yanzu bata sake hawa computer ba. Dama wayarta tunda ta dawo take a kashe taƙi ta kunna.
Yau ma suna fara tafiya a kan hanyarsu ta zuwa islamiyya ta fahimci ana binsu a baya. Wani takaici ne ya turnuƙe ta dan tsaf ta gane guy ɗin jiya ne da tun a ƙofar gate ta watsar da lamarinsa. Ba kuma ta sake tunawa da shi ba sai yanzu da taga motarsa. Sam Zahidah da Hafsat su basu lura da shi ba. Hakan yasa Hibbah fuskewa batace komai ba har suka shige cikin islamiyya.


Ƙarfe biyar suka ta shi yau ma tamkar kowane weekend. Da ga nan kuma sai wani satin. Gaba ɗaya ta sake watsar da lamarin wani Shuraim. Amma a mamakinta sai gashi ta sake ganin yana biye da su har gida. Kamar da safe yanzu ma bai yunƙurin fitowa ba. A yanzu kam su Zahidah sun ganshi. Koda sukaima Hibbah magana sai tai musu tsaki ma.
Ƙyaleta sukai ganin shima bai fito a motar ba.


★★


Duk yanda Hibbah taso watsar da lamarin Shuraim sai hakan bai yuwu ba yau. Dan lokaci-lokaci yakan faɗo mata a rai. Sai dai takan ja tsaki da murguɗa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login