Showing 36001 words to 39000 words out of 165076 words

Chapter 13 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74043

baki tamkar tana a gabansa. Har takai abinda takeyi ɗin ya bama Ummi haushi ta balbaleta da faɗa har su Yaya Muhammad suka shigo.
Sune suka bama Ummin haƙuri da fara tambayar Hibbah cikin lallashi ko wani abu ke damunta ne?. Sam batasan wani boye-ɓoye ba. Musamman ma awajen yayunta da suke da matukar shaƙuwa da juna. Kanta tsaye ta shiga basu labarin abinda takema tsakin.
“Woow, ƴar Tanee ɗin Ummi anyi saurayi Congratulations. Yau ɗaya a tarihi dole na rubuta na ajiye na haɗa da shagalin barbaje kolin fati na musamman a gidan nan nayi suriki a matsayina na yaya mai lasisin cin gadon Muhibbat Aliyu Hamza (Tanee)”. Ammar ya faɗa yana tafa hannaye cike da tsokana. Filo Yaya Abubakar ya ɗauka ya jefe sa da shi. Dariya gaba ɗayansu suka kwashe da shi saboda yanda Ammar ya baje a ƙasa da bata fuska alamar yaji zafi..
Hibbah kam dariya sosai take masa harda faɗowa saman kujera. Ta saka yatsun hannunta a kunne tana masa gwalo kamar yanda yara keyi. Filon da aka jefesa da shi ya ɗauka zai jefo mata ta tashi da gudu tai hanyar ɗakinta.
“Ummi kanta sai da tai dariya. Cikin dariyar ne ta ce, “ALLAH dai ya shirye ku, kai da Tanee ɗin bansan wanda yafi wani shashanci ba. Ni tashi ka ɗakkomin magunguna na a ɗaki tunda ita ta gudu nasan ba sake dawowa zatai ba kuma”.
Amsawa Ammar yayi da to yana mikewa ya nufi ɗakin Ummin. A dai-dai kuma wanann lokacin Abba da hajiya mama da wasu tsoffin maza biyu suka shigo falon da sallama.
Da ga Ummi har yaranta da mamaki suke kallonsu, musamman ma Abba da basusan ya dawo gidan ba. Tsoffin kuma Ummi ce kawai ta sansu. Da ƙyar ta iya buɗe baki cikin ƙarfin hali ta ce, “Kawu sannunku da zuwa”.
Farin ne kawai yace, “Uhumm”. Ɗaya kam bai tanka ba. Sai dai bin su Yaya Muhammad da yake da kallo tamkar idanunsa zasu faɗo ƙasa.
Yaya Muhammad da ya lura da kallon ƙurullar da kuma yanayin da Ummi ta shiga tamkar na ruɗani ya saka shi fara gaishesu. Haka yasa suma sauran ƙannensa fara gaisuwar.
Amsa musu sukai suna cigaba da kallonsu. Yayinda hajiya mama keta faman ƙyaɓe baki. Abba kam sai wani harare-harare yakeyi.
Ummi tai ƙasa da kai cike da ladabi ta hau gaishesu itama. Basu wani amsa mata da ƙyau ba. Sai ma baƙin tsohon ne a kausashe ya ce, “Uh lallai Asiya an samu guri kam tabbas. Ga manyan sojoji kuma a gefe masu tare miki faɗa. Dama irin wanan ai ake gudu akan auren masu asali irin naki. Saboda shi hali naso yakeyi har jikokin bayan-baya. Gashi ko mun gani yau da idanun mu”.
Idanu Ummi ta lumshe a hankali kanta a ƙasa. Wasu zafafan hawaye suka silalo saman kumatunta. Sai dai cikin dabara ta kai hannu ta share dan kar ƴaƴanta su gani. Cikin dauriya da juriyar da kowa ya santa da shi ta ɗago murmushi a saman fuskarta. “Kawu ina fatan kunzo lafiya?”. Ta faɗa domin son kauda wancam zancen da ya fara.
Sai dai sam bataci nasara ba. Dan kuwa hajiya mama ce ta amshe da faɗin, “Ni ko zan faɗa maka hali naso yake Hannafi, dan kuwa gashi nan a zuri'a ta. Wlhy badan jinin ɗan inna (babansu Hibbah) na yawo jikin waɗan man yaran ba da tuni na daɗe da sallama su, babu wanda ya cuceni sai malam da ya ƙarrafa wannan auren da har na mutu bazan taɓa daina kuka da ALLAH wadai a kansa ba. Wai fa kuga waɗan nan sanƙama-sanƙaman yaran ne babu mai ko neman aure. Kuma uwarsu ta zuba musu ido saboda ita ɗin bata hanyar.......”
“Waɗan nan kuma fa? Da ga ina?”. Cewar Ammar da ya fito da ga ɗakin Ummi yaci karo da abinda bai bari ba. Furucinsa kuma ne ya katse zancen da Hajiya mama ta ɗakko tiryan-tiryan.
Babu wanda ya bashi amsa. Sai zuba masa ido da tsoffin sukai tare da Abba. Baki ya buɗe zai sake magana Ummi ta girgiza masa kanta. Kansa ya ɗauke kawai tare da durƙusawa gabanta ya na ajiye ɗan basket ɗin da magungunan nata ke a ciki. Ɓalla mata ya shigayi yana miƙa mata tare da saka mata ruwa akan baki.
Wani uban salllami farin tsohon nan ya shiga jerawa yana tafa hannaye. “Kai mizan gani haka ni Ballo (Bello😂). Wannan wane irin kafurcine kuma haka Hasiya?. Wannan ƙurmisheshen gardin ɗan ke baki ruwa a baki kuma?. A to lallai zancen Hannafi gaskiya ne. Da alama ma ke kinfi uwar taki iya shege”.
A fusace Yaya Umar ya miƙe zai bar falon. Abba ya katsesa a gadarance da faɗin, “To mara mutunci da baiyi gadon arziki ba sai ka tsaya dan zuwan nakune ai”.
Ido Yaya Umar ya rimtse da ƙarfi yana dunƙule hannunsa.
“Kai fitsararre, idan shi ka rainashi ai mu ka ɗaga mana ƙafa kodan rashin saninmu da kai ko.”
Ƙafa Yaya Umar ya ɗaga zai cigaba da tafiya wasu hawaye masu zafin gaske na gangaroma kumatunsa.
“Dawo ka zauna”. Umarni da ga Ummi ya hanashi ajiye kafar da ya ɗaga ɗin.
“Iyeee! A lallai Haƙilu kuna ganin jalalar rayuwa. Wato itace kawai mai sawa da hanawa akan ƴaƴan, bayan wahalar da kaci na kula da su tsahon shekaru. Tabbas Hasiya kinyi asara kekam.
Da sauri Ammar ya ɗago ya kallesa. Ya miƙe tare da nuna Kawu Bello da ɗan yatsa cikin kaushi da ɗaci yace, “Kai kaine kai asara tsohon banza ɗan tasha”.
A tare Hajiya mama da Abba da kawu Bello da kawu Hannafi suka zazzaro ido suna zabura. Ummi tai saurin fisgo hannun Ammar tare da daka masa tsawa. “Aliyu!!”.
Cikin ficewar hayyaci ya fisge hannunta a cikin nasa da faɗin, “Haba Ummi, wai sai yau she ne zaki daina zama anacin kashi akanki a gidannan ne? Babu ruwana da alaƙarsu gareki. Na rantse da ALLAH idan tsoho bai gyara kalaman harshensa ba to kafin ya fita a falon nan zan datse harshen kuwa na jefar ƙasa”.
Ɗimmm
Ummi ta sauke ma Ammar dundu. “Ammar kanada hankali kuwa? Miyasa kai bana faɗa maka kaji ne wai?. Kasan waɗan nan ɗin su wanene a wajena? To iyayena ne, ƙannen mahaifiyata ne, tamakar yanda Hajiya mama ta ke uwa a gareni itama. Ka shiga hankalinka kona saɓa maka kaji ko”.
“Amma Umm.....”
Wani kallo da ta masa ya sakashi yin shiru ya haɗiye sauran maganar.
Wata ƴar dariya Abba yayi da faɗin, “Kun gani ko? Hakafa gidan yake kullum kamar na ƴan tasha. Sun rainani basa ganin mutunci na bale na mama, bayan ma yaƙi nai da zuciyata wajen rufa mata asiri. To uwar tasu ma ba wai raga mata sukeyi ba. Dan haka na ɗakko ku nan dan ayita ta ƙare. Bazan iya cigaba da ciyar da ƙattan banza ba. Dan haka na yanke shawarar aura musu su Amlah, inba hakaba wataran yankan rago za'a samu sunmin a gidan nan. Ita kuma waccan fitsararriyar uwar ƴan janye-janyen jidalin da suke ɗaurama ƙugu a gidan tana zuba taɓara saboda ita ƴar ido ce Junaid zan aurawa. kunga shikenan anyi tuwona maina ko ba komai sun huta da gori ma asalin uwarsu.”
“Wannan gaskiya ne Haƙilu. Ai kama taimaki rayuwarsu. Dan a zamanin nan kowa yaji tushen zancen ta ina zai basu ƴarsa. Balle ma ita da take ƴa mace. Bayan ma ka riga ka bata Junaidu ɗin ai wlhy da nayima Musa kamu ma”.
Da sauri Abba ya ce, “Shi Musan sai yay haƙuri tunda na riga naima Junaid ɗin alƙawari dai. ALLAH ya bashi ta shi”.


Yaya Muhammad da ya ƙule matuƙa da takaicinsu ya buɗe baki zai yi magana. Amma sai Ummi tai saurin girgiza masa kanta cikin gargaɗi. Kawai sai gani tai hawaye suna sakko masa tsabar zuciyarsa ta kai ƙololuwa a ɓaci.
Ummi itace ke katange dukkan yunƙurinsu, sun rasa miyasa take hakan a gare su game da dangin mahaifin nasu. Abinda ma basu gane ba shine a yau. Shin ta amshi ballagazayen ƴaƴan gidan da ake iƙirarin an basu kenan matsayin matansu ko mi? Koda ace zasuyi haƙuri suyi mata biyayya bazasu taɓa amincewa a aurama Junaid Hibbah ba. Sai dai komi zai faru ya faru wlhy...........✍


*_Tofa masu karatu, yaya kenan? Wanene zai ci nasara tsakanin su Abba da su Yaya Muhammad? Ni kaina inason jin wace ƙaddarace baibaye da Ummi da ta fi bukatar haƙuri da cin kashin waɗan nan mutane haka?. Kumuje zuwa. muna gab da tsunduma cikin wasan gadan-gadan😉👎🏻_*






*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥










*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*




*_Typing📲_*






*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*


https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share


*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*


https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb




*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD_*


https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS




*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM_*


https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw




_________________________




*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻


*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*


_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._


*_Muna da haɗin_*


_Turaren wutane_
_Humrh_
_Kulacham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_


_Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_


*_Da magungun nan mata_*
_Irin su kaza_
_Tantabara_
_Tsumi_
_Gumba_
_Zuma_


*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*


Wushishi road KADUNA


08067807620
09057713999


_________________________




*_Chapter Fourteen_*


.............A gidan Ummi komai ya canja. Gaba ɗaya ya ranta sun bar walwala. Sun daina fara'a. Sun daina zaman hira, abinci ma kaɗan suke tsakura. Idan tai magana suce sun ƙoshi. Ta ko ina ta gaza gane kansu.
Da farko tayi biris da su, duk da kuwa ta fahimcesu tsaf. Sai dai ganin abin nasu bana ƙare bane sai itama lamarin ya fara damunta. Dan ita kanta sun jefata a cikin kaɗaici. Hatta da Hibbah ƴar karamarsu itama ta ɗauke mata wuta. Saboda wannan abun daya faru ma ta tattara ta koma makaranta duk da Yaya Abubakar ya hanata zuwa da.
Duk da ta ɗan fuskanci ƙalubale a wajen mutane a ranar data koma saboda tafiya da itan da ƴan sanda sukazo sukayi ranar haka ta daurema zuciyarta ta cigaba da zuwa. Bakuma ta sanarma kowa ba. Dan a ganinta da zaman gidan su tana cigaba da ganin Abba da baƙinsa gara kallon da ƴan makarantar zasu mata.
Tunfa Ummi na ɗaukar lamarin nasu wasa sai ƙara girmama ya keyi. Dan kwanakin nan biyu ma basa dawowa gidan sai sun dai-daici tayi barci sannan. Hankalinta sosai ya kuma tashi. Ga damuwar yaranta, ga damuwar auren da aketa ƙulle-ƙullen nana musu na son zuciya. Wanda tsaf ta gama fahimta da gane ina hakan ya dosa. Sarai ta gane manufar Abbah akan son ƙulla auren ƴaƴanta da nashi, manufar kuma duk ɗaya ce tsakaninsa da hajiya mama.
Gaba ɗaya ta rasa ina zata saka kanta taji sanyi, babu uwa babu uba, babu abokin shawara a cikin ƴan uwa, babu wanda zata kaima ƙara ya duba matsalarta ya share kukanta. Gudun abinda zaije ya dawo kuma ke sakata kwaɓar ƴaƴanta akowane lokaci. Bata son abinda zai rabata da su. Bata son a cutar mata da su. Dan sune hope ɗinta, sune murmushin fuskarta. Sune masu share hawayenta da tun tana ƴar ƙanƙanuwarta suke kwaranya a bisa kumatunta. Tasan nuna ƙarfinsu ya kawo kuma zai iya zama sanadin da komai Abba zai iya aikatawa a garesu domin samun cikar burinsa, kuma kamar yanda yasha faɗa koda ya salwantar da rayukansu babu mai yarda shine ya aikata. Wasu hawaye ne masu zafi suka silalo mata saman fuska.
Wata banzar dariya Abba da ke shigowa cikin sashen ya shiga tuntsurawa yana tafa hannaye. Cike da izgili ya dubeta sheƙeƙe yana faɗin, “Kuka kuka kuka! Ai kuwa yanzu kika fara kuka Asiya. Yo ina jarumtar taki ne yau? Shin har kin fara zuwa ƙasa ne tunkan ma a ɗaura auran manufarsa kuma ta tabbata?. Tunda har kikace ni ban isaba Asiya, to wlhy kema bazaki taɓa isa ba. Yau ina wanda kike gadar da shi? Ya tafi tamkarma ba'ayisa ba. Abinda kika hanashi yay mana ta hanyar zagon ƙasa ya dawo hannunmu a lokacin da ko ido baki isa ɗagawa akai ba. To suma ƴaƴa mazan da kike ɗagawar kin haifa masa zasu mamaye komai tafin hannunmu zasu cigaba da zama ballagaza kawai. Zaki iya tashi kuma mu shige ciki dan ina bukatar haƙƙina. Inba hakaba kuma zan ƙwata anan cikin falon babu ruwana....”
Hanyar bedroom ɗinta ya nufa yana gama faɗa alamar ta biyosa. Ummi da ke jin wani ƙullutun abu yazo ya tokare maƙoshinta ta shiga karanto duk addu'ar da tazo mata a saman harshe saboda jin numfashinta na fita a gwagwgwame. A hankali sanyi ya rinƙa shiga cikin ƙashinta, yayin da jikinta ya fara wani irin rawa, har haƙwaranta na haɗuwa waje guda. Hannu takai domin lalubo wayarta da ke saman centre table. Sai dai hakan ya gagara sakamakon gushewar gani da ta risketa a lokaci ƙanƙani. Hannunta ya goce da ga lalube wayar, sai gata ƙasa wanwar da ga saman kujera.....
A dai-dai wannan lokacin Hibbah ta shigo tana masifar bibiyarta da kullum Shuraim keyi babu fashi balle nuna gajiyawa duk da yarfatashin da take yi a kulum. Data fita da ga gida zuwa makaranta yana biye da ita. Hakama idan ta dawo sai ya rakota har gida ta hanyar bibiyarta. Zuwa yanzun tun lamarin nasa na bata mamaki har ya koma takaici da al-ajab. Har tabbayar kanta take shin baida aikinyi ne ko mi?. Wannan takaicin nasane ya sata yau ana saukesu a napep taje tai masa knocking glass. Yana saukewa ta balbalesa da masifa batare data yarda sun haɗa ido ba dan karma yay mata kwarjini. Sai dai abin ALLAH wadai da takaici, harta gama masifar tata ma bai nuna yaji haushi ba. Sai ma murmushin da ya nema rikita mata lissafi ya sakar mata yana wani narkewa a cikin kujera.
Wani uban kara ta ƙwalla tana isa inda Ummi ke kwance wanwar tana wani irin tari dake fita da ƙyar. Kiran sunanta ta shigayi tana girgizata hankali tashe. Sai dai ina Ummi ta fita hayyacinta. Dabarar rarumar wayar Ummin ce tazo mata a rai. Batare data nutsu wajen ganin wanda ta kira ba kawai tai dailing numbern farko, dan tasan su ne dai kawai suke yawan kiran no din Ummin tasu a koda yaushe.
“Yaya dan ALLAH kazo gida, Ummi...Umminmu. Na shiga ukuna. Ummi dan ALLAH ki tashi. Wlhy kika mutu nima mutuwa zanyi. Dan ALLAH Ummi na roƙeki karki mutu. wlhy bazamu sake yin fushi da ke ba. Mun tuba Ummi, mun daina. Mun yarda zamu auresu Ummi.......”
Sambatu taketa faman yi tama manta da waya a kunnenta. Kukanta ya fiddo Abba da ga ɗakin Ummi ɗin wando a hannu. dan harya cire kaya ya baje a gado yana jiran jakarsa ta shigo ya murza a wulaƙance. Ido huɗu sukai da Hibbah da ke sake ƙwala kuka tana kiran Ummi da girgizata. Ai sai ta sake fasa wata ƙarar ganin a yanda ya fito, saboda bai saka wandon dai-dai ba an samu mishkila wajen bayyanar jikinsa.
Sakin Ummi tai ta fita a guje da ga sashen baki ɗaya jikinta na rawa. Tana da yayu maza manya. Amma tunda take da su ko zama da singlet da boxers basu taɓa yi a gabanta ba balle a yanayin da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login