Showing 114001 words to 117000 words out of 165076 words

Chapter 39 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74016

da su hajiya mama suka toshe kunnuwa suna miƙewa tsaye a matuƙar firgice ganin Abba ya yanke jiki ya faɗi a wajen wayoyin duk sunyi gefe.


★★★★★


Abinda ke a kunnensa ya danna lokacin da yake shiga motar da sukazo yabar wajen, dan tuni su Zaidu sun ware. “Habib ka ɗauki yarinyarnan yanzun nan kubar gidan nan, ka tabbatar kafin ku wuce ka kashe wayar hannunta ka cire sim card ɗin ciki kayi flushing ɗinsa. Ga su Zaidu nan isowa. Kubi ta cikin store ɗin kitchen akwai hanyar da zata fiddaku ta wancan layin.”
Sosai hankalin Habib ya tashi, dan yanzun nan dama ya kama Hibbah da waya. Yana tsaka da tambayarta ne kiran master ya shigo masa. Wayar ya fusge daga hanunta a fusace ya takata bayan ya fashe. murfin ya ɓalle da kyar, ɗan pin ɗin dake jikin blackboard ɗin inda computers ɗin suke ya ɗauka ya cire sim card ɗin ya karya. Yay azamar danna wani abu a jikin teble ɗin yay ƙasa.
Baki Hibbah ta taɓe dan a ganinta kafin ya gama duk wannan abun da master yace ta tabbatar ƴan sanda sunzo. Ranta fes yau ALLAH yayi dubun masu aikata saɓon ALLAH ya cika.
Dawowar Habib yayi dai-dai da shigowar su Salis kusan a tare. Gaba ɗaya firgice suke. Jakunkunansu suka shiga ɗakin da suke kwana suka tattaro. Habib ya fisgi hanun Hibbah da duk abinda suke tana tsayene kamar dogariya tana kallonsu. Sai faman taɓe baki take irin ko'a jikinta ɗin nan. Hannun ta fige tana ture Habib, a dai-dai na Master ya shigo falon shima.
“Ku tafii!!!”.
Ya faɗa da ƙarfi jin jiniyar ƴan sanda na gabato anguwar. Yay maganar yana nuna musu hanyar kitchen, kallo ɗaya zakai masa kai kanka ka firgita dan gaba ɗaya ya rikiɗe tamkar wani bajimin zaki. Kobi takan Hibbah da tsawarsa ta firgita baibi ba. Ya nufi ɗakin da suka kwana cikin zafin nama. Mintun uku tsakani ya dawo falon, wanda yay dai-dai da ƙarasowar ƴan sandan ƙofar gidan. Ga kuma Hibbah data nufi hanyar waje da gudu. Baya ya take mata shima. Sabon tashin hankalin daya yunƙuro masa ne yasashi fisgo Hibbah cikin zafin nama ya yarfa mata wani shegen mari mai azabar zafi da saida jinta da ganinta suka gushe na wucin gadi. Ya kama kunnenta ya murɗe da shegen karfi yana magana cikin matuƙar hasala da hargowar da bata taɓa gani tare da shi ba. “Stupid girl!!, idan ni baki kasheni ba, ke da hannunki da wannan shegen taurin kan naki zaki kashe ahalinki”. Wani irin rawa jikinta ya fara hawaye na mata ambaliya akan fuska. Ya turata ta zube ƙasa dan ji yake kamar yay mata bugun mutuwa kozai huce daga abinda yakeji a halin yanzun. Sake miƙewa tai da gudu, Fitowarsu compound ɗin gidan yayi dai-dai da shigowar ƴan sandan cikin gidan.
“Ku buɗe musu wuta gaba daya!!!”.
A.G ya faɗa da ƙarfi.
A razane wani a ciki ya bashi amsa da cewar, “Oga yarinyarfa data bamu information akai gata tare da shi”.
“Har ita ku haɗa”.
A.G ya faɗa cikin karaji. Ba ƙaramin firgita Hibbah tayi ba. Ta waiga ta dubi Master take biyota ta kalli ƴan sandan da suka saita bindugu akansu da alamun cika umarnin ogansu zasuyi ta rumtse idanu da ƙarfi wasu zafafan hawayen nadama da dana sani na sakko mata. Ita data bada bayani akansa amma jami'in tsaron daya kamata ya bata kariya wajen kubutar da itane ke cewa a harbeta baida matsala. Wace irin ƙasa muke da ita kenan? Ahaka akeson wanda yaga mai laifi ya tona masa asiri.......
Master da gaba ɗaya kamaninsa sun canja duk da bindugun da aka saitasu da shi ya nufota a guje da alamar son kubutar da ita saboda harsasai guda uku da jami'an suka harbo gaba ɗaya kanta sukayi gadan-gadan, sai ɗaya ne ya nufosa shiko ya saka bullet proof jacket a jikinsa, yasan duk tsiya harbin bazai samu makasrsa ba sai dai idan kwanansa ne ya ƙare yau. Yana gab da isowa gareta bullet ɗin ya shiga cikin kafarsa. Ƙaramar ƙara ya saki yana kaiwa duƙe, hanunsa ɗaya na zaro karamar bindigar jikinsa shima ya fara maida murtani. Wani irin zabura Hibbah tai babu shiri ta nufosa, hakan ya bata damar gocema bullets ɗin da suka nufo kanta har guda biyu ɗaya ya sake samun master a hannu.
Hankalinta ya ƙara matuƙar tashi ganin shi ƙoƙarinsa ya bata kariya, yayinda waɗanda ya kamata su bata kariyar su son kasheta sukeyi. Sam rikicewa ya hanats gane fuskar dattijo A.G. Shiko Master ya gansa ne duk da yana ƙoƙarin ɓoye fuskarsa garesa. Duk da tasan ya mata nauyi haka ta miƙa hannu ta kamo nasa tana kuka. Haɗin kai ya bata ya miƙe shima da ƙyar cikin dakiya da dauriyarsa duk da tuni jini ya ɓalle masa ta ƙafa da hannu. Kasancewar suna gab da ƙofar falon suka sami nasarar afkawa ciki, Master ya danna security jin A.G ya bama yaransa damar bin bayansu duk da dama ba daina harbin sukaiba ALLAH dai ne ya bama su Master kariya bayan biyun da suka sameshi wasu basu sake taɓasu ba. Jakkarsa daya yasar a falon ya ɗauka, da sauri Hibbah ta amsa ta goya a bayanta. Ya fisgi hannunta cikin bama kansa ƙwarin gwiwa suka afka cikin kitchen ɗin suma. Sai dai su a tsakiyar kicin ɗin ya tsaya ya haye saman table ɗin wajen duk da jini dake kwaranya masa. Hannu ya miƙa ta tsakkiyar p.o.p ɗin kicin ɗin ya burma sai ga ƙofa. Ya ɗan daka tsalle ya fisgo wani zare mai kama da tsani. Hannu ya miƙa mata ta ɗora nata sai faman wai-waige take jin ƴan sandan nata ƙoƙarin buɗe kofar falon. Ta tabbatar suka shigo kuwa sun gama yawone. Cak ya ɗagota duk da tanada nauyi.
Da taimakonsa ta fara hawan zaren tsanin harta shige. Kafin shima ya fara hawa. Yana gab da shigewa suka sami nasarrar ɓalla ƙofar falon. Cikin sa'a ya ida shigewa da jan tsanin ya maido ƙofar ya rufo. Karan farko a tarihin rayuwa Hibbah a cikin zinc bisa gangancin da taso tafkama rayuwarsu. Wani ƙaton bututu kamar na ruwa suka samu cikin zinc ɗin, Master da ya fara ɗan galabaita saboda jinin dake fita a jikinsa dama ba isashen lafiyane da shi ba ya nuna mata cikin bututun da bata fitila ƴar karama mai shegen haske.
Ɗan kwalin kanta ta cire tana kuka ta yagashi biyu, ƙafarsa ta ɗaure masa dai-dai wajen da bullet ɗin ya shiga. Sauran rabin ta ɗaure masa hannunsa. Cikin taune lips ya turata cikin bututun shima yabi bayanta dan yasan jinin da yake zubarwane zai nunama su A.G inda sukabi.
Da rarrafe suka dinga kutsa kai cikin bututun batare da Hibbah tasan ƙarshemsa ba, balle inda suka dosa. Sunyi tafiyar da har sai da ta fara galabaita saboda ƙura sannan ta fara hango haske alamar karshensa kenan. Koda suka fito batasan inane nan ɗin ba. Amma dai gidane a wajen shima mai kyawun gaske. Ya fisgi hannunta ya danna cikin motar dake fake a wajen bayan ya yaye tanfol ɗin da aka rufeta da shi. Shima shiga yay yana jan numfashi da ƙyar dan idanunsa sun fara ganin jigari-jigari. A mamakinta sai gani tai ya danna wani abu gate ɗin ya buɗe kansa. Ya fita da motar da gudu daga gidan. Har daga nan tana iya jiyo jiniyar motocin yan sanda da karar harbe-harbe alamar gidan da suka baro kusa yake da wannan. Gudu yake tsulawa na fitar hankali wanda dole motoci da napep ke basa hanya. Masu zagi nayi masu kiransa ɗan giya nayi. Baimasan sunai ba. Dan bai tsaya ba sai a wata anguwa. Motar taga ya faka a wani dan lungu ya fita. Batare da yayi magana ba itama ya zagayo ya fisgota. Key wani mai shushaina dake a lungun zaune shi kaɗai yana gugar takalma ya jeho masa. Ya cafe dajan hannunta suka sake shiga wata motar, yayinda tunkan su fice a lungun ta hango mai shushaina ɗin nan na rufe waccan motar da tamfol.
Wani irin tsoransa ne ya tsargama Hibbah. Ta kafesa da ido cike da alamar tambayoyi sai dai babu damar yinsu. Yanzu kam ta cikin anguwanni ya dinga bi da su har suka sake zuwa wani layi sukai canjin mota, anan ko motar kawai suka samu sai mai tallan rake a gefe can shi kaɗai. Sai da ya shiga motar ne ya yafito mai tallan raken yana cizar leɓe. da gudu mai rake ya turo Wheelbarrow ɗinsa zuwa inda suke. “Rake na ɗari uku”.
Master ya faɗa da ƙyar yana lumshe ido.
Raken mai rake ya ɗebo ya zuba a leda. Ya turo kansa ta Window ɗin motar yana ajiye keys a cinyar master. “Gida mai lamba takwas, anguwar bauranya”.
Komai masbaiceba yaja motar suka bar wajen. Gaba ɗaya hibbah ta mutu a zaune a karo na biyu, kallonsa kawai take kamar gunkiya har suka iso anguwar da mai raken taji ya faɗa. horn yayi maigadi yay saurin wangale masa gate ya danna hancin motar. Gaba ɗaya su Salis dake tsaye sunata faman kaikawo a compound gidan mai sashe biyu sukayo inda yay fakin. Hakama baba saude dake can zaune goye da Sharifat ta mike da sauri duk da batasan ainahin abinda ke faruwa ba. Kawai dai su Habib sunje sun taho da itane acan L.E street batare da sun mata bayanin komai ba.
Kusan gaba dayansu suka rufu akansa. Yayinda wasu a cikinsu harsun fara kuka ganin yanda ya samu harbi. Ga jikinsa harya fara saki saboda jinin da ya zubar. Da taimakonsu suka nufi sashen da ke a hannun dama suna shartar hawaye. Yayinda Hibbah wani irin nadama ke sake shiga bargonta, dan itama kukan da taga su Habib nayine ya sake tayar mata da hankali.
Kanta baba saude tayo ta kamata itama tana tambayarta miya faru? Jikin baba saude ta faɗa tana girgiza kanta hawaye na kwarara mata. Sai kuma tai saurin barin jikin baba sauden tabi bayan su Adam. Itama Baba sauden bayansu tabi jikinta sai rawa yake ganin jikin Master duk jini.


A falon suka zaunar da shi bisa wata kujera mara tudu mai laushin tsiya. Cikin sauri Musbahu ya dakko First aid box ɗin daya hango can gefe. Cikin sauri Khalid ya kai tsugunne ya fara warware dan kwalin hibbah data daura masa. Yayinda Idris ke kwance na hannun shi kuma. Cikin rumtse ido Khalid ya zuba masa ruwan magani akan wajen. Wata wahalalliyar ƙara Master ya saki yana sake damƙe hannun Zaidu dake gefensa. Khalid na kuka yasa wani ƙarfe cikin ramin ya fisgo bullet ɗin. Baki kawai Master ya datse da azabar ƙarfi. Tashi Khalid yay ya koma wajen hanun, yayinda Habib ya duka gaban kafar ya cigaba da treating ɗinta. Acan ma Khalid ya cire bullet ɗin hannun, ganin Habib bai gama treating ƙafar ba sai shi ya cigaba dana hannun.
Tunda aka cire bullets ɗin wani irin zufa ke ketoma Master akowacce hudar gashinsa. Yayinda yaketa faman sauke ajiyar zuciya a jajjere. Sai da suka kammala tsaf suka goge jinin da duk ya bata ko'ina sannan ya buɗe idanunsa da sauri saboda abinda yazo masa a rai yanzun nan.
“Ya ALLAH! Akwai matsala, akwai matsala!!”.
Ya shiga faɗa yana jujjuya kansa. Hankali tashe su Salis ke tambayarsa wace irin matsala kuma?.
Bai iya basu amsa ba, sai wayar da ke a jikinsa ya laluba da sauri yana duban su Adam. Cikin wani yare da ko Baba saude bata taɓa ji Mastern yayi ba yayma su Adam magana. Cikin sauri suka nufi hanyar fita a falon suna amsa masa da girmamawa. Su biyar suka fice aka bar Idris da Khalid kawai.
Da ido yayma Idris maganar da su kaɗai suke fahimtar yarensa ta hakan. Idris ya jinjina masa kai da duban baba Saude da har yanzu take sharar hawaye.
“Baba muje na kaiki ki huta ko? Karki damu komai yayi dai-dai insha ALLAHU ”.
Badan baba Saude taso ba tabisa ɗauke da Sharifat dake barci a bayanta. Dan tunda ta fasa kuka sanda su Habib ke shiga gida suna ce mata tafito saita lallaɓata tai barci lokacin da suka shigo mota, koda suka iso gidan kuma saita goyata da gyalenta.
Kuka sosai Hibbah keyi wanda ke sake hasala zuciyar Master. Sai dai da yake yanzu hankalinsa nakan wani abu daban yasa ya shareta. Sai da yaji ta cigaba da cika masa kunne ne ya daka matsawar da ba ita kadai ba hatta da Khalid sai da ya zabura.
Idan baki bar min wannan garshekan kukan ba saina daddage kanki da bullets a gidan nan!!. Kuma ki tashi min anan kafin na hambaraki a ƙasa kanki ya bugi tiles ɗin nan!!”.
Da gudu ta miƙe tabi bayan su baba saude. Dan yanzu kam ta tabbatar ada ba Master ta sani ba yanzu ne taga ainahin Master ganin idonta ba labari ba. Gaba ɗaya idanunsa sun koma na ainahin tsohon bahagon zaki da babu abinda ya sani sai farauta. Idanunsa kai kace aman wuta zasuyi saboda tsabar jan da suka koma.
Kansa ya dafe da faɗin, “Ina ji kamar na kashe yarinyar nan a yau na manta da shafin rayuwarta a tarihina.”
Sosai tausayinsa ya sake ɗarsuwa a zuciyar Khalid. Ya tabbatar yau Hibbah ta ballo ruwa na gaske wanda batasan harda aikin taimakon ahalinta suka fita ba. Mastern su baya kuka sai domin tausayin al'umma. duk haɗarin da zakaga ya jefa kansa a cikin domin taimakon wanine. Kullum wahala yake da mutane batare da sun san manufarsa ba. Kowa kallon ɗan ta'adda takadari yake masa. Hatsabibi shu'umi ɓarawo. Amma hakan bayasa ya sare daga aikinsa duk da waɗanda yake dan su ɗin ko 1% basu fahimcesa ba.............✍




*_Asirin da xoxo taimin yau ya warware🙄😏🚶🏻😖_*






TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥










*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*








*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*


https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS




*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*


https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw




_________________________




*_Chapter Thirty Five_*


..........Yaran A.G sun gama bincike ko ina babu Master da Hibbah a gidan. Sai da ga ƙarshe A.G ya farga da bin jinin da Master ya dinga zubarwa har cikin kitchen. Yay tsam yana auna inda jinin ya tsaya ya kuma zuba da yawa.
“John!”.
Ya kira sunan ɗaya da ga cikin yaran nasa cikin da ka tsawa. A guje sukazo. Batare da yayi magana ba ya nuna musu p.o.p yana zaro waya aljihu. Cikin ƙanƙanin lokaci suma suka shige cikin p.o.p ɗin. Koda suka shiga suma ta cikin bututun sukabi suna sanar masa abinda suka fahimta. Sai da suka ɓilla har ta wancan gidan sannan suka sanar masa ta waya.
Wasu yaran ya bari anan ya fito ta cikin layin, gida uku ne tsakanin gidan da inda su Master suka zauna.
“Lallai guy ɗin nan ya cika matsiyaci shu'umi. Kaga shege kamar wani kurege ta ko'ina fasa hanyoyi yake.”
Ɗaya da ga cikin yaran A.G ya faɗa rai a ɓace. Komai A.G bai iya cewa ba. Dan zuciyarsa tabbas tana gab da fashewa a cikin ƙirjinsa. Jin shigowar wasu ɓangarori na jami'an tsaro cikin layin ya sakashi fita. Cikin ƙanƙanin lokaci anguwar ma baki ɗaya ta gama hargitsewa. Bakaji da ganin komai sai jami'an tsaro da ƴan jaridu. Kowa burinsa yaji wani abu da ga bakin su A.G da suka fara zuwa wajen. Sai dai ina komai ya kasa fita da ga bakin A.G. da ga ƙarshe ma zare jikinsa yay ya baro anguwar saboda kiran da Alhajin Mande yay masa akan ya maza yazo inda suke tunda zancen guduwar master harta sake bazuwa cikin ƙanƙanin lokaci.


Gaba ɗayansu sun hallara ne a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login