Showing 24001 words to 27000 words out of 165076 words

Chapter 9 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74000

sakeyi, yayinda kukan Hibbah ke ci musu zukata matuƙa. Cikin bada umarni Yaya Muhammad ya ce su dagata a kaita asibiti. Yanda ya faɗa ɗin haka sukai, sai dai suna fitowa harabar gidan ƴan sanda na shigowa. Basuyi yunkurin bi takansu ba. Sai dai muryar Abba da sukaji yana nuna Ammar da cewar shine ya kashe masa yaro ya saka hankalinsu rabuwa biyu.
A ɗan firgice Yaya Usman ya furta, “Kisa?”.
“Eh mara mutunci, ko ƙarya zan masa ne? Tun ɗazun likitoci suke akan Junaid amma babu alamar numfashi tare da shi, dan haka ku kamasa, inhar na rasa ɗana shima sai an kashesa.”
Tarin Ummi ne ya ƙara ƙarfi, sai ga jini na fitowa ta hancinta. Hankalinsu ne ya sake tashi. Sai a lokacinne Abba ya lura da halin da Ummi take a ciki. Maimakon ya saki batun ƴan sanda ya shiga sahun masu kula da ita, sai hakan ta gagara. A kausashe ya bama ƴan sandan damar kama Ammar yana tabbatar musu pretending Ummi keyi kawai.
Ganin duk sun shiga mota ƴan sanda kuma sun cukuykuye Ammar dake turjewa dan hankalinsa nakan halin da mahaifiyarsu ke ciki bata tasu yake ba. Yaya Muhammad ya cema Yaya Usman ya fita yabi ƴan sandan dan susan inda za'a kai Ammar ɗin. Su kuma zasu kai Ummin asibitin.
Badan yaso ba ya fita domin bin umarninsa. Dan duk da an haifesu babu wani yawan tazara a tsakaninsu hakan baya hanasu respecting junansu saboda ƙyaƙyƙyawan training da suka samu da ga mahaifiyarsu.......


★★★★★★★★★★★


A lokacin da wancan tashin hankali ke baibaye da ahalin Hibbah, anan headquarters ɗin ƴan sanda ƙoƙarin fitar da bayanan harin da Hibbah ta kaima master sukeyi. Sai dai kamar yanda Yaya Abubakar yay hasashe sunansu ne ya fito matsayin waɗanda sukai aikin. Sun kuma tabbatar nan da lokaci ƙanƙani zasu gurfanar da Master a saman gwiwoyinsa gaban duniya.


Babban abinda ya ɗauki hankalin jama'a da media baki ɗaya shine. Rahoton ƴan sanda na fita da mintuna uku kacal. Sai ga wani babban labari kuma da ga wannan shahararren ɓarawo mai suna *(MASTER)*. Ya fitar da jerin sunayen wasu manyan kaddarori na matar gwamna da mutane basu taɓa kawoma ransu hasashen tana da alaƙa da su ba a wani shafi nasa. Sannan ya rabasu a manyan gidajen redio da television ta hanyar tura musu saƙwanni kai tsaye a shafukansu na sada zumunta masu matuƙar muhimmanci da yawan mabiya.
Sosai ƙura ta tashi cikin lokaci ƙanƙani, manyan ƴan siyasa abokan takarar wannan jami'iyya suka samu damar baje kolin nasu faɗar albarkacin bakin dan dama tamkar kaɗan ake jira. Yayinda a gefe kuma da yawansu suke goyon bayan shi wanann master da ƙoƙarin wanke laifukansa a idanun mutane.
Fitar wannan kace nace keda wuya takardar gayyata ta bayyana da ga hukumar *(Yaƙi da ta'annatin kayan gwamnati)* zuwa ga matar gwamna. Acewarsu, suna gayyatarta zuwa ofishinsu da ga nan zuwa awanni ashirin da huɗu domin amsa musu wasu tambayoyi. Idan bataje da kanta ba, zasuje har gida su su ɗakkota.


Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga ɓangaren gidan gwamnati suma sun yunƙuro wajen maida murtani ta hanyar jifar abokan hamayyar TAKUN SAƘAAr nasu da dangantaka da Master. Suna mai tabbatar ma duniya lallai akwai lauje cikin naɗi. Sannan akwai ayar tambaya dangane da wanzuwar Master. Shin kodai? Kodai......😂🤐.


Ta kowanne fanni gari ya ɗauka zafi, babu wani babban labari sai na wannan badaƙala ta TAKUN SAƘAA tsakanin Master da ya haɗa gurmin zuwa jami'an tsaro da na gwamnati. tare da ƴan siyasa da masu radin faɗin albarkacin baki. A gefe kuma ga talakawa ƴan bani na iya nata faman sharhi akan komai, kai kace agabansu aka ƙulla al'amarin..........


(😖Wai, sunan wata karya. Sharaton. Bily aɗan dinga sassautawa dai🚶🏻😌😒😏😣😝)


*________________________________*


Wani ƙayataccen murmushin da ya saka yaransa shagala a kallonsa ya saki lokacin da yake faman duba wasu da ga cikin Comments na mutane da ke wanzuwa a yanar gizo. Cikin salon ƙasaitarsa da izza ya wani juya kujerar da yake zaune cike da ƙwarewa yana lafewa a cikinta hankali kwance. Tare da wani salon da su kaɗai suke gane mi yake nufi idan yayi sa.
Dariya suka sanya cike da jin daɗin. Dan kobai faɗaba sunsan yana cikin farin ciki matuƙa. A duk sanda ya tada irin wannan ƙurar ya ga taja hankalin ƴan ƙasa da waɗanda yayi dominsu su kansu yakan yafe musu laifuka da sukai masa. Ko ya bisu da ƙyauta mai tsoka da ke sakasu farin ciki. Zai kuma kasance tare da su cike da nishaɗi duk da shiɗin ba mutum bane mai yawan magana akoda yaushe.
Da wannan damar Habib yay amfani wajen gabatar masa da rahoton binciken da ya gudanar akan aikin da ya basu ɗazun. Dan sun wuce adadin awannin da ya basu sosai. Kuma sunsan bawai ya manta bane, ya sharesu ne kawai bisa wani dalili nasa daban. Zatama iya yuwuwa shi tuni ya gama aikin binciken, suma ɗin ya sakasu yi ne kawai domin hukuntasu bisa laifin sakacinsu.
Komai baice akan takardun ba. Hasalima baiko buɗesu ba ya cigaba da duba sakwannin. Yayinda murmushi ke cike da ɓoyayyar fuskarsa da har ake ganin bayyanarsa bisa ta bogin da ke a kanta, wadda idan ba faɗa maka akaiba bazaka taɓa cewa ba fuskarsa bace ba. Su kansu yaransa inda ace da ita kawai yake amfani baya canjawa tabbas zasu ce itace ainahin fuskarsa. Sai dai zuwa da mabanbanta da yakeyi ya sakasu fidda wanann hasashen a cikin ransu.
Ya kai tsahon lokaci tare da su yana bibiyar kowacce kafar yanar gizo da ta yaɗa labarai. Kafin ya miƙe yana faɗin, *“7:30am* zamu koma *L.E street.* Jahje na buƙatar bada ƙafa”.
Wani ihun farin ciki suka saka. Dan a gaba ɗaya gidajen da suke zama gidan *_L.E STREET_* yafi kowanne girma da ababen more rayuwa. Suna matukar mamakin yanda yake sama musu manyan gidajen da suke zama, a kuma manyan anguwanni batare da an farga shiɗin baneba. Tsabar hatsabibancinsa kuma a wasu lokutan sukan koma anguwannin talakawa su zauna har na tsahon wani lokaci. Haka suke tamkar fulanin tashi. Da wahala suyi zaman wata uku a gida batare da sun koma wani ba.
Kansa ya ɗan girgiza da kai kofin coffee ɗinsa saman baki yana barin wajen nasu zuwa jikin windown ƙaramin falon da suke ciki na gidan da ya kawosu ɗazun. Wanda har yanzu basu san taka-maimai a cikin wace anguwa yake ba, dan basu fita ko soro ba har yanzu. Shi kadai ne ya fita bayan awanni takwas ya kuma dawo.
Wani hatsabibin murmushi ya sake saki idonsa kyam akan ƙwan wutar lantarki da ke a tsakar gidan. Haka ya cigaba da tsaiwa a jikin window ɗin yana cigaba da shan coffee ɗinsa da sauraren iya shegen yaransa akan Comments ɗin mutane da suka koma bibiya suma suna kwasar dariya.
Kofin da ya sake kaiwa baki yaji babu komai a ciki ya sakashi ɗago kofin ya kalla. Ba komai ciki ya shanye, hakan sai ya bashi dariya. Amma sai ya gintse kayansa baiyiba sai a zuciya. Juyowa yay da baya ya ajiye cup ɗin ya ɗauka file ɗin da Habib ya ajiye. Cikin muryarsa da sautinta ke fita da nutsuwa da amo yace, “Ayi addu'a kafin a kwanta. Goodnight”.
Kusan a tare suka haɗa baki wajen faɗin, “ALLAH ya tashemu lafiya boss. Sweet dream tare da ƙarin ƙyaƙyƙyawar idea akan ƴan ruda”.
Daƙƙuwa yay musu batare da ya juyoba. Sai dai ya saki murmushi dai-dai yana shigewa. Duk da basuga murmushin nasa ba kasancewar ya juya musu baya hakan bai hanasu yin kananun dariyar farin ciki ba gaba dayansu.
Yana shigewa suka farma gasassun kajin da ya kawo musu tun shigowarsa da ci. Dama sun ɗan ɗaga kafa ne ganin yazo a cikin yanayin babu wasa. Yanzu ko sunsan komai normal ne, sai abinda ba'a rasaba saboda rikita-rikitar Master ɗinsu bata taɓa karewa. Daya toshe waccan matsalar zai ɓallo wata da kansa kafinma ƙurar wadda ya tayar ta lafa.


Shima ko da ya shiga ɗakin zazzafan numfashi ya furzar. Ko'ina fes dan tun bayan barinsu da yayi suka gyara komai. Ya jefa file ɗin hannunsa saman madai-daicin gadon. Kayansa ya shiga zamewa alamar son watsa ruwa. Ya rage da ga shi sai singlet da boxer. A haka ya nufi toilet ɗin.
Tsahon mintuna ashirin ya ɗauka a ciki kafin ya kammala, tun kafin ya fito da ga bayin ya ziro hannu ya kashe wutar ɗakin baki ɗaya. Batare da damuwa da duhun da ya mamaye ko ina ba ya fito a haka. Ta cikin duhun ya iso bakin gadon, ya kai zaune cikin lalube ya ɗakko wayarsa ƙarama. Fitilarta ya kunna, tare da ɗaukar file ɗin da Habib ya bashi. Sam ba'a ganin fuskarsa. Sai dai shi yana ganin rubutun file ɗin kasancewar shi ya haska kai tsaye. Sai alamun bathrobe ɗin dake a jikinsa wadda iya inda hasken ya haska kawai ake gani.
“What?!”.
Ya faɗa cikin subucewar baki ganin bayanan na nuna cewar da taimakon mace aka kai musu harin ɗazun. Macen ma ƴar 18 years kacal. Cikin wani irin rawar jiki yay wurgi da file ɗin yana faɗin, “Impossible! Ni! Ni! Ni ne yarinya ƙarama kamar wannan zata hara. Hari irin wanda wani mahaluki bai taɓa samun galabar yimin shi ba. Kuturun ubacan kayyasa😳............✍


*_HHHH anayi muna ɓallar rake na funtuwa mai zaƙi. Alaji Master yaya take ne😉😝🐒?. In baka saniba ma yanzu ne wasan zai fara😂👎🏻_*




*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*












*_Typing📲_*






*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*


https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share


*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*


https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb


_________________________




*_Chapter Eleven_*


..........Cikin gaggawa aka amshi Ummi a asibiti. Dan da ƙyar take fitar da numfashi, ga jinin da yake fita mata ta hanci da tayo tari da ya harmutsa dukkan zukatan su Yaya Muhammad. Hibbah kam ai tama koma musu tamkar zararriya. Dan koda za'a shige da Ummi sai da Yaya Umar ya riƙota shima hawaye masu ɗaci na cika masa idanu.
Yaya Muhammad kam da baida wahalar zubda hawaye gefe kawai ya maida kansa yana sharewa. Umminsu itace duniyarsu. Itace farin cikinsu. Itace ta maye musu dukkan gurbi na dangin mahaifinsu da giɓin mahaifin nasu da suka rasa tsahon shekaru goma sha tara. Tayi haƙuri da damuwoyi kala-kala domin taga sunyi farin ciki. A kullum ƙoƙarin ta su zama mutanen kirki. Su zama masu haƙuri, su zama masu juriya. Su zama.... Su zama... Da yawa. To sukam idan akace sun rasata ina zasu saka kansu da rayuwarsu. Idan suna a gabanta sam basa tuna sun girma. Ganin kansu suke tamkar ƴan shekaru goma-goma. Bazasu so Ummi ta tafi ta barsu batare da sun cika mata burinta na ganin sunyi aure ba. Kamar yanda take addu'ar ganin zuri'arsu suma hakan shine fatansu a yanzun. Suna son yawan ganin dariya a saman fuskarta kamar yanda mahaifinsu yay sanda yana raye. Amma hakan duk bazata tabbataba sai tana a kusa da su........
“Ya ALLAH ka bama Ummi lafiya ka tashi kafaɗunta. ALLAH yasa ni na mutu a madadinta”.
Furucin Muhibbat da ke kuka ya katsema Yaya Muhammad da su Yaya Abubakar tunaninsu. Gaba ɗayansu suka zuba mata idanu na ɗunbin tausayinta da ƙaunarta. Yarinya ce ita mai yawan walwala, kazarkazar, wauta, tsiwa, rawan kai, surutu duk a dalilin gata da kulawar da take samu da ga garesu. Tana matuƙar son Ummi, suma haka. Batasan mahaifinsu ba, shiyyasa suketa ƙoƙarin ganin sun cike mata gurbinsa.
A hankali Yaya Abubakar ya taka inda take durƙushe gaban Yaya Umar da rauni ya cika zuciyarsa na tausayin kansu da autar ta su. Hannu biyu yasa ya kamota ya ɗaga tsaye. “Haba Muhibbat, maimakon kima Ummi addu'ar samun lafiya sai ki dinga ma kanki addu'ar mutuwa a madadinta?. Insha ALLAH Umminmu zata tashi da lafiyarta kinji. Ki mata addu'a da fatan alkairi, ALLAH ya na tare da ita kinji”.
Kanta ta jinjina masa wasu zafafan hawayen na rige-rigen sakko mata. Yasa hannu ya share mata yana murmushin ƙarfin hali.
“Ƙyaƙyƙyawa mai kama da Umminta a komai, sai dai raguwa ce bata kai Ummi jarumta ba”.
Yaya Abubakar ya faɗa cikin ƙarfin hali yana ɗan ja mata kumatu. Maimakon tai dariya da tsalle kamar yanda ta saba idan ya faɗa mata hakan, sai ta faɗa jikinsa ta fashe da kuka. Kusan atare duk suka rumtse idanunsu, dan kukanta na matuƙar sake tada musu hankali.


Kusan mintoci arba'in da biyu likitoci suka ɗauka tare da Ummi. Kafin ALLAH ya basu ikon fitowa. A kusan tare su Yaya Umar suka miƙe a zabure harda Hibbah dake jingine jikin Yaya Umar barcin wahala ya ɗauketa.
Kusan a tare suka furta “Doctor ya jikin Ummin mu?”.
Kallonsu yayi cikin furzar da numfashi yana cire norsemask ɗin fuskarsa. “Inason yin magana da ku a office”. Ya faɗa yana ƙoƙarin wucesu. A take suka rufa masa baya har Muhhibat da Yaya Umar ke riƙe da hannunta. Kusan tare suka shiga da doctor cikin office ɗin. Hakan da sukai sai tausayinsu ya sake kamashi. Dan a kallo ɗaya zakai musu ka hango ɗunbin so da ƙaunar da sukema mahaifiyar tasu. Bai wani tsaya ja musu rai ba yay musu bayani akan matsalar da ke tare da Ummi a ƙasan zuciya da hanjinta. Bincikensu ya nuna kuma ta jima da ciwon yana ta cinta a hankali, sai dai yafi nuna kansane a duk lokacin da wani ɓacin rai ko tashin hankali ya sameta. Amma zasu mata aiki insha ALLAH suna mata fatan samun lafiya.
Duk da maganarsa ta ƙarshe taɗan sakasu jin sanyi hakan bai hana zukatansu shiga cikin matuƙar rauni ba. Ya ɗan ƙara faɗaɗa musu bayanai akan abinda za'a iya buƙata akan aikin da magungunanta. Tare da basu tabbacin inhar sun shirya a yau ɗin nan ma za'a iya mata aikin. A take sukace sun amince, duk da kuwa kuɗaɗen da ya ambata da wuya a iya samunsu kai tsaye da ga garesu. Badan suna da yawa bane sosai, kawai dai suɗin masu tasowa ne ba wasu ɗumbin kuɗaɗe suka tara ba. Amma dai tunda ya ce zasu iya bada rabi idan an kammala aikin su cika zasuyi ƙoƙarin su insha ALLAH.
Take ya basu takarda Yaya Muhammad ya saka hannu. Daga haka suka fito domin tattaunawa akan zancen kuɗin. Dan doctor yace sai sun tura zaiyi ƙoƙarin haɗa wasu da ga kayan aikin insha ALLAH.
Su dukansu suna aiki, Ammar ne kawai da Hibbah ƴan makaranta a cikinsu. Sai Yaya Umar da ke ɗan harkar kasuwanci saboda matsalar rashin samun aiki da matasa ke fama da shi a ƙasar nan. Sai ma yazam a yanzu yafi nutsuwa da kasuwancin sama da aikin da yay karatu akansa. Dama kuma su Yaya Muhammad ɗin nata son ganin sun ƙara masa ƙarfin jari tunda ALLAH yayma kasuwar tasa nasibi.
Sun ɗan tattauna wajen ganin sun haɗa kuɗaɗen, cikin amincin ALLAH ma sai gashi an samu kusan rabin a hannunsu su uku. Idan Yaya Usman yazo shima zasuji mi za'a samu daga garesa. Abba dai basa saka rai game da shi sam.
Basuyi zaman ɓata lokaci ba wajen fita su tattaro kuɗaɗaɗen har Yaya Usman da ya iso asibitin a yanzu shima, dan ya kasa jure zama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login