Showing 147001 words to 150000 words out of 165076 words

Chapter 50 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74022

sanadinsa na sanshi”.
A razane A.G yake duban Abba, haka su Alhajin Mande ma a rikice suke kallon A.G ɗin. “Kai munafuki, ya kake neman ƙullamin sharri. Halilu anya ƙwalwar kanka kuwa bata samu matsala ba!!”.
“Na rantse da ALLAH kai ne”.
Abba ya sake faɗa cikin kuka wiwi. A.G da tuni zufa ta jiƙesa zaiyi magana Engineer ya katsesa cikin tafa hannu yana ƴar dariya. “Jama'a ga maganar Alhaji Sallau fa ta bayyana!”.
“Ban gane ta bayyana ba! Mi kake nufi?”. Cewar A.G yana kallonsa hankali tashe.
“Abinda kowa yaji a kunnensa mana A.G”. A matuƙar hargitse A.G ya miƙe ido rufe ya yarfama Engineer wani gigitaccen mari da sai da wutar kansa ta ɗauke. Abinka da jami'in tsaro yasan sirrin cin uban mutum. A razane duk suka miƙe baki buɗe. Har suna haɗa baki wajen ambatar sunan A.G ɗin.
A.G da gaba ɗaya ya birkice yace, “Sunana ne. Tayaya wannan mara mutuncin zai duba tsabar idona ya alaƙantani da cin amanarku. Duk iya ƙoƙarin da nake muku akan ɗan iskan yaron nan baƙwa gani har takai yau za'a kalleni da wannan suffar. In ban kashe Engineer ba kuce bani bane A.G”.
Da sauri Alhajin Mande ya riƙosa. “Haba A.G yada harzuƙa haka daga magana. A gabanka fa Halilu yace kaine minene laifin Engineer?”.
“Okay bakagama laifinsa ba! To yayi. Kai kuyita dukan Halilu da uwarsa har sai ya faɗi gaskiya”.
Tamkar ƙyaftawar ido zaratan samarin suka shiga lugudar su Abba har sai da suka suma aka zuba musu ruwa suka farfaɗo. Sake cigaba da dukansu sukai kuma babu ko tausayi balle duban tsufan Hajiya mama. Ganin zasu iya mutuwa Dr Sufi yace, “Nifa ina ganin duka bashi magani, idan kuma kun kashe Halilu ta ina zamu samu wani information kenan”.
Maganarsa ce ta saka Alhajin Mande dakatar dasu. Da ga Hajiya mama har Abba nishin azabar fitar rai kawai sukeyi. Dan tabbas sun sadaƙar yau kam zasu iya barin duniyar nan ma baki ɗaya.
Faɗa ya cigaba a tsakaninsu dan sufa sunƙi yarda da rantsuwar da A.G ke kwarara musu akan ƙarya Abba ke masa. Shi kuma ganin sunƙi fahimtarsa ya sake birkice musu kawai har takaisa ga fara dambatawa shi da Engineer da yafi kowa zaƙewa duk da tsufansu....


_________________________


A ɓangaren Master kam koda suka baro wajen su Ummi kai tsaye station suka nufa dan I.G ya shigo gari suna tare da C.P ma. Yaya Abubakar yayi matuƙar mamakin ganin inda sukazo, musamman daya san ana neman Isma'ill ɗinne ruwa a jallo. Sai dai kuma zargin daya jima a ransa ya sakashi yin shiru domin ganin ƙarshen wasan. Kasancewar Master bada fuskar Muhammad Shuraim yazo musu ba babu wanda yace da shi uffan. Sai dai saboda Abdull da wasu tsiraru ke gaishesu kasancewar sunsan yaron I.G ne. Sai ko shi yaya Abubakar daya haɗu da mutane biyu da ya sani.
Dama I.G ya shigo ne saboda case ɗin dake a hannun Master ɗin, dan haka sunayin knocking aka basu iznin shiga. Yaya Abubakar da Master suka ƙame kusan a tare domin girmamawa ga I.G da C.P.
Yaya Abubakar yay saurin juyowa ya duba Master, shima da yake shiɗin yake kallo sai ya sakar masa murmushi kawai ya ɗauke kansa ya maida ga I.G dake magana.
“C.P wannan shine A.S.P Muhammad Shuraim Aliyu, jami'i ne mai ƙwazo, dan haka na ɗorasa akan case ɗin nan na yaron nan master a sirrance. Bakuma hakan na nufin su waɗancan da suke aiki akan hakan bazasu cigaba ba”.
“Okay sir”.
Cewar C.P a girmame yana duban Master da ya ɗan sake ƙame jikinsa domin girmamawa ga C.P.
“A.S.P!”.
“Yes sir”.
Master ya amsama C.P ɗin.
“Tunda boss ya tabbatar da ƙwarewarka hundred percent muma mun yarda. Ina fatan kasan wannan aikine na gaggawa kuma mai buƙatar jajircewa. Duniya gaba ɗaya ta ɗauka burinta kawai taga Master a hannunmu, kowace hukuma ta tsaro farautarsa take domin ta kasance mai nasara. Kamar yanda wasu daga cikin jami'an mu suka tabbatar da harbinsa har sau biyu bazai kasance yayi nisa ba. Lallai-lallai yana cikin garin nan baije ko'ina ba, dan babu wata hanya da ba'a saka jami'an tsaro ba tun bayan mintuna goma sha bakwai da harbin nasa. Waɗannan mintunan kuma sunyi kaɗan ace ya fita a garin nan. Dan haka munada tabbacin yana cikin garin nan. Akwai teams da yawa dake zagaye da case ɗin nan, dan haka kaima zaka haɗa naka team ɗinne dan bama buƙatar duk waɗan can a naka operation ɗin”.
“Yes sir!”.
Master ya sake faɗa.
Sosai yaya Abubakar ya narke a tsaye, dan shikam yau Isma'il ya matuƙar jefa tunaninsa a garari da ruɗani. C.P ya katse masa tunani ta hanyar kiran sunansa.
Maida hankalinsa yay ga C.P ɗin yana ƙoƙarin dai-daita yanayinsa. Shima yace, “Yes sir”.
“Zaka taimaka masa a wannan aikin saboda na yarda da ƙwazonka matuƙa, shiyyasa mukasa ya ɗakko mana kai, dan mune muka saka aka ɓoyeku saboda information da muka samu cewar jami'an farin kaya zasuyi amfani da ku saboda ƙanwarka dake a hannun master. Kaga wannan shine amfanin sanar da abu da wuri, da baka sanar min ba da nima zan shiga tawagar masu zargin kasan master kai da ahalinka”.
Yaya Abubakar da duk suka rikitasa ya ce, “Thanks you sir” kawai, dan yafi buƙatar jin komai da ga bakin Isma'il, zuciyarsa ta fara raya masa Isma'il rainama su C.P hankali yake kenan suma? Kokuwa wani abu ne daban......
I.G dake rubuce-rubece jikin takarda ya miƙama Master. “A.S.P a yau zaka dawo filin daga, sai kayi ƙoƙarin haɗa sabon team. Ga wannan file ɗin zaka samu dukan bayanan da zaka buƙata a ciki insha ALLAH”.
Takardan da file ɗin master ya amsa da faɗin, “Thanks you sir”.
Daga haka suka fito, Master ya sake salute ɗin I.G cike da wani salo. A waje suka bar Abdull, dan haka ya miƙe suka fice a tare magana fal bakin yaya Abubakar.
Sai da suka fito da ga katafaren gate ɗin Yaya Abubakar da abu keta masa kaikawo a cikin rai ya duba Master.
“Anya kuwa Isma'il baka ɓoye mana wani abu? Zuciyata ta kasa riƙe zargin da take maka a wannan gaɓar gaskiya. Dama kai jami'in tsaro ne?”.
“Jajirtacce ma kuwa! Gwarzo abin kwatance da alfahari ga al'ummar wannan ƙasa.”
Abdull ya bama Yaya Abubakar amsa kai tsaye yana murmushi da juya sitiyari.
“Karka yarda da shi”.
Master ya faɗa yana duban Yaya Abubakar dake kallonsa ta mirror yana wani ƙayataccen murmushi dake tafe da ma'anoni da yawa. Murmushin shima Yaya Abubakar yayi a karon farko ya ɗauke kansa yana jinjinawa. “Dama na jima ina wannan zarigin a raina, a randa aka kaimu gidan can kuma na sake tabbatarwa. Jira da sauraren zuwanka kawai nake dama ai. Amma abinda ban fahimtaba anan shine, suma su I.G basusan kaike basaja matsayin master ba kenan?”.
Shiru Master yay tamkar bazai amsa ba. Sai kuma yay murmushi da kai hannu ya zare mask ɗin fuskarsa. Yaja tissue ya goge real face ɗinsa yana furzar da huci. “Ɗan uwana nake kallonka, dan tunda har kasan wanene Isma'il wannan ma zan iya sanar maka saboda a ƙarshen tattare aikin nan nake bana son abinda zai maidani baya kodan Muhibbat.” ya ƙare maganar da ɗaga idanunsa suka kalli juna da Yaya Abubakar. Murmushi sukayi a tare, master ya sake ɗauke idanunsa. “I.G yasan komai, C.P ne bai saniba.”
Ko tari kasayi yaya Abubakar yay. dan kuwa a yau ɗinnan ya sake tabbatar da zancen nan na mutane dake kiran Master ɗin Hatsabibi duk da su ɗin bama su gama sanin wanene shi ba. Abdull dake saurarensu yay ƙaramar dariya yana ɗan duban Yaya Abubakar ɗin ta mirror shima. “Yayanmu ai mana afuwa. Wannan surikin naka baida maraba da aljanin kan kuka mai leƙa gidan kowa. Sai kun haɗa da addu'a gaskiya”.
Mangare masa ƙeya Master yayi, hakan yasasu kwashewa da dariya su duka dan Abdull sitiyarin ya saki sai da Master ya riƙe da sauri. Har yana magana cikin suɓutar baki.
“Kai ɗan iska karka zubar damu wlhy ban gama angwanci ba, Baby luv na buƙatata a kusa da ita”.
Abdull ya tsaida motar yana kwasar dariya. Yaya Abubakar ma dai dariyar yakeyi, ransa fal farin ciki duk da sun jima da fahimtar irin son da Isma'il ɗin kema autarsu.. Master ya harari Abdull yana ƙumshe tasa dariyar dan harga ALLAH suɓutar bakice. Cikin borin kunya yace, “Ɗan haɗa gurmi in bazaka tada motarba zamu fita mu barka dan munada abunyi”.
“A'a miyay zafi na Baby luv. Bara na kaiku nikam kafin ka ƙonemu a titi. Shiru Master yay bai sake tanka masa ba. Yaya Abubakar ma dai sai ya saki zancen ya cigaba da duba file ɗin da I.G ya bama Master ɗin har suka kaisa station ɗin da yake aiki suka ajiyesa bayan Master yay masa bayanin shine zai haɗa musu team ɗin, shi kuma zaije ya ƙarasa tattare abinda ya rage daga nan zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu zasu fita operation ɗin. Cike da gamsuwa Yaya Abubakar ya basu hannu sukai musabaha sannan ya fita.


Daga nan gida suka wuce suma. Inda su Habib suke jiran dawowar master ɗin dan tun a jiya ya sanar musu yau ɗin ranar aiki ce da ga nan har zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu............✍






TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*






*_Typing📲_*






_______________________




*_MATAYEN ƘWARAI KUNA INA NE?._*




_Maza ku garzayo da gudunku ga ƴar zuru mamar zee-zee mai kayan mata na maida tsohuwa yarinya💃🏻._


*Kayan matan ƴar zuru zasu maidaki shalele ƴar gaban goshin maigida koda kina da kishiya ƴar birnin shehu😂💃🏻*.


_Kayan ƴar zuru nada matuƙar sirrika da inganci irin wanda sai an gwada akansan na ƙwarai. Idan da ƙyautar gida akemiki a master room kikai amfani da kayan ƴar zuru Nigeria za'a baki harda jirigin sama na yawata ƙasashen duniya😉💃🏻_.


*MUNADA KAYAYYAKI KAMAR HAKA*👌🏻


Kaza akwai 10k
15k
5k
Tsimi 5k 10k
Matsi 5k
Gumba uku 2k
Zumar gorun tula syrup3k
Garuka 3k
Cicccibi 5k
Zakara 20k
Zabo20k
Humra
Turaren tsugunni
Butar tsarki
Maganin infection
Tsimin tabaje
Turaren al,ajab


*Muna maraba da maisayen ɗaya ko sari, kayanmu garantee ne in har basuyimaba zan maidama kudinka*.

_Address maberar jariri bayan FGC sokoto_
08068526455


*Zaku iya saving number ta domin ganin hajata*


Zaku iya samun mu amanhajar


Facebook
Istagram


Yar_zuru_mamar_zeezee- kyn_mata.


Sai kunzo🥰🥰🥰🥰💃🏻👌🏻.




_____________________


*_Chapter Forty Seven_*


..........Su Hibbah na baje a falo suna kwasar hira ita da su Zahidah dake ta mata sheri itama cikine da ita, dan ta matsa musu tunda ta ƙyalla ido taga cikunna a jikinsu. Shinefa suma suka tasata gaba da nasu tsokanar Ammar na tayasu da dariya wai wayaga auta da ɗa. Tun tana kai ƙararsa wajen su Yaya Umar harta koma jifansa da throw pillows tana kukan taɓara.
Hatta Ummi kasa daurewa tai saida tai dariya dan taɓarar autar tata sai ita. Kiran da yaya Abubakar yayma Ummi ne ya sanar mata bazai kwana a gida ba ya sakasu barin Hibbah ɗin suka koma hirar rashin dawowar Master shima. Suna cikin zancen kuma sai ga ɗan halak ɗin ya kira Ummi shima ya sanar mata Hibbah zata kwana anan shi wani uziri ya riƙesu tare da yaya Abubakar. Addu'a tai musu na fatan alkairi baki ɗaya.
Yana katse kiran kuma ya kira Ammar yace ya haɗasa da Hibbah. Amma ya jata gefe dan yasan halin kayarsa. Da ƙyar Ammar ya danne dariyarsa ya kama hannun Hibbah suka nufi bedroom ɗin Ummi.
Zatai magana ya manna mata wayar a kunnenta ya fice. Hibbah dake hararar Ammar dake mata gwalo zai fice tace, “Mai kan gwanda kawai”.
“Nine mai kan gwandan?”.
Sassanyar muryarsa ta daki dodon kunnenta a bazata. Dan tama manta waya Ammar ya saka mata a kunne. Idanu taɗan waro tamkar tana gabansa. “ALLAH shine shaida ni dai bada kai nake ba da yaya Ammar nake”.
Master dake goge jikinsa dake raɓar ruwan wanka da ga can yay murmushi yana ɗan lumshe ido. “Ki shirya ganinan zuwa zan ɗaukeki”.
Kamar tana gabansa ta marairaice fuska. “Dan ALLAH ka barni na kawana wajen Ummi”.
“Idan na barki ni kuma na kwana da wa?”.
Ƙasa-ƙasa batare da tunanin zaiji ba ta ce, “To da dawa kake kwana?”.
“Okay hakama zakice, to nama fasa barin ki shirya kawai”.
“Dan ALLAH kayi haƙuri bazan sake ba”.
Yanda tai maganar da alamar kuka ya sashi danne dariyarsa da ƙyar. “Idan na barki duk bashin da kikaci zaki biyasa in kin dawo”.
Da yake so take a barta babu tunanin komai tace ta amince.
Murmushi ya sakeyi yana ƙoƙarin shiryawa. “Okay tunda hakane sai ki fara da sumba ɗaya ƙwaƙwara yanzun nan kona taho”.
“Ni dai a'a dan ALLAH”.
“Oh to ki shirya ganinan zuw.....”
Kafinma ya rufe baki ta mannama wayar kiss da yazo masa cikin kunne a bazata. Sai kuma ta yanke wayar ƙitt. Duk yanda yaso dannewa ya gagara sai da yay dariya yana girgiza kansa da ajiye wayar ya cigaba da shirinsa.


Gudu-gudu yay shiri ya fito dan su Habib na jiransa a falo. Barka da fitowa suka shiga yimasa har yakai zaune. Lap-top ɗin dake ajiye saman centre table ajiye ya ɗauka yana gyara zamansa ƙafa ɗaya kan ɗaya. Cikin maida hankalinsa ga abinda yake a ciki ya fara magana batare daya kallesu ba. “Salis, Khalid, Habib. Kune zaku shiga cikin gidan. Khalid kaine zaka fara bubbuɗe ko ina ta yanda idan ya farka zaiyi tunanin kuskure akai wajen buɗesa. Sannan Salis ka tabbatar ka ajiye dukkan abinda zai iya gani da zai taimaka masa neman su A.G a farko kafin kowa, ko cikin yaransa. Da zarar kun kammala duk wannan Khalid sai kai masa allurar da Abdull ya baka. Kasancewar tanada ƙarfi zai saurin farkawa ya kuma dawo hayyacinsa da wuri. Habib zai amfani da wannan damar ta komawa da ga can ta bayan Windown ɗakin da yake ciki kayi wayar ƙarya akan abinda zaka shirya kansa a halin yanzu. Daga nan sai ku koma tacan sama bayan ƙarfen nan ku ɓuya har sai ya fito a gidan sannan ku kirani”.
Cikin girmamawa suka amsa masa. da hannu yay musu nunin suje, tare da cilla musu key ɗin mota. Salis ya cafe.
Sai da suka fice ya ɗago ya duba Adam tare da miƙa masa key ɗin Napep. “Kaje ka jira a bakin layin, da zaran sun kira ya fito ka ɗaukesa zuwa duk inda ya sanar maka zaine. daga nan na sani”.
“Okay Master”.
Adam ya faɗa shima cike da girmamawa.
Bayan fitarsa shima yaɗan cigaba da aiki, bayan wasu mintuna ya dubi Musbahu da Idris da Zaidu. “Nasan da ya samu damar fitowa babu wanda zai nema a halin yanzu sai yaransa biyu daya yarda dasu fiye da kowa bayan ni. Dage, da Katafila, Musbahu, Zaidu baku da matsala da hakan, dan kun iya komai nasu, ga wayoyinsu nan sai ku ɗauka, zaku haɗa hannu da Adam wajen kaisa inda su A.G suke”.
Suma cikin girmamawa suka amsa masa tare da ɗaukar keys ɗin mashin guda biyu da wayoyin suka bar wajen domin zuwa suyi nasu shirin. Ya dubi Idris daya rage, “Kai kuma zamu kasance tare da kai anan domin bibiyarsu da ga nan har zuwa lokacin dazan fita”.
Kansa ya jinjina masa shima, tare da neman waje ya zauna. Waya Master ya ɗauka, yay kiran yaya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login