Showing 156001 words to 159000 words out of 165076 words

Chapter 53 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74048

yay waɗan nan yashe-yashen kuɗaɗen har yanzu yasa su gaba ɗaya zarginsu akan master ɗan ta'adda yake. Dan haka aƙali dake cike fam da mikin tabon da aka bar masa ya shirya musu tsaf shima domin acewarsa *RAMUWAR GAYYA TAFI GAYYA ZAFI.*

Duk da shari'arsu shari'a ce buɗaɗɗiya hakan bai hana a bama lauyoyinsu damar fafatawa ba da lauyoyin gwamnati. Sai dai manya-manyan hujjojin da lauyoyin gwamnati ke riƙe da su yasa suka kada nasu A.G tun ma kafin shari'ar tai nisa. Dan dole aka matsi bakunan su Alhajin Mande suka zayyane kaso mafi yawa na daga tsiyatakun da suka aikata da rigunan mutunci da wanda master ɗan ta'adda ya aikata bisa umarninsu. Koda suka kawo maganar yashe asusan mutane ba master ɗinsu bane sam alƙali baima sauraresu ba. Dan ihu da boren dake faruwa ta waje daga jama'ar gari da kuɗin da alƙali yaci na manyan mutane irinsu matar gwamna yasa shi yanke musu hukuncin zaman gidan kaso na tsahon shekaru ɗari da hamsin-hamsin. A takaice dai kowa yasan ɗaurine na rai da rai wannan kawai.
Sosai wannan hukunci yayma kowa daɗi a cikin manyan, nan take aka cikuykuyi su A.G da aka hana sake cewa komai akayo waje da su domin miƙasu magarƙama (prison). Duk da wannan hukunci da aka yanke musu hakan bai hana jama'ar gari da sukai ready ɗin fitowar tasu ba fara jifansu da gasu har jami'an da suka fiddosu. Dansu burinsu kawai a basu su A.G su kashe kawai yafi hukuncin zaman gidan yarin a wajensu. Sosai ruwan dutsuna ke sauka a kansu har takai da ƙyar aka turasu mota. Nanma basu tsiraba dan motar mutane suka dinga jifa tako ina suna fasa glasses ɗin. Dole jami'an tsaro suka koma kare kawunansu kawai basu A.G ba. Kafin a bar harabar kotun da anguwarma baki ɗaya dasu an musu mugayen raunuka sunata ihu da kururuwa.
Dan dole aka canja akalar miƙasu prison aka nufi asibiti dasu domin fara treating nasu. Da wannan damar Master yay amfani wajen yima master ɗan ta'adda allurar guba batare da kowa ya farga ba, yayi kuma hakanne domin ɗaukar fansar iyayensa tamkar yanda yay ƙudiri a ransa tun farko. Bayan anyi treating ɗinsu dole nan ma aka bar asibitin dasu zuwa asibitin cikin prison ɗin saboda tsaro ba tsoro ba. Dan duk da boren nan na jama'a akwai magoya bayan su A.G a gefe musamman ƙasashen ƙetare da suke kallon ƙazantar da su A.G ɗin ke aikatawa wadda jama'a ke tada jijiyoyin wuya a kanta ba komaiba. Za'a kuma iya yin amfani da wannan damar a kuɓutar dasu, duk da kuwa a prison ɗin ma dai bawai sakaran tsaro aka barsu da shiba. An sakasune cikin tsatstsauran tsaro da horo mai tsananin gaske da sai sun gwammaci mutuwa da da rayuwa. A yanda mutane ma suka jigatasu da raunikan ruwan duwatsu da wahala wasu a cikinsu sukai labari.


Abubuwan sun ɗan lafa kaɗan, sai dai an cigaba da cecekuce a kafafen sada zumunta dana yaɗa labarai musam akan abubuwan da suka biyo baya daga bakunan ahalin su A.G, tun daga kan matansu, ƴaƴansu, zuwa danginsu daketa fitaowa suna nuna ƙyama da nisanta kawunansu da su. Yayinda wasu keshan tsinuwa a wajen tsoffinsu da basu riga sun mutu ba irinsu Hajiya mama dake kwance a asibiti rai hannun ALLAH. Dan da ƙyar take iya gane wanda ke kanta. Sai dai bakinta bai gajiyaba wajen jan tsinuwa da ALLAH ya isa ga Halilu.
Koda su Ummi ma sukaje dubata bisa tursasawar Ummi ɗin da ƙyar ta ganesu tana darzar kuka da roƙon su yafe mata musamman ma Ummi. Ummi tasha kuka dan duk mai imani yaga yanda ƙafar Hajiya mama zuwa rabin jikinta sukai wani masifar kumbura dole ne ya tausaya mata. Ahakanma wai an samu anyi mata gyaran karayar datai a ƙugun a daren jiya a asibitin. Ba itaba. hatta su likitocin kamsu basu san adadin sumar da Hajiya mama tayi ba saboda azabar wahala. Fitsari kam ai ba'a magana ko fanfon birtzatse ya shafa mata lafiya.
Ko'a jikin su Hibbah, dan ita hankalintama nakan mijinta da sam bataji ɗuriyarsaba yau ma. sai ganin data ɗan masa a tv sanda ake kotu da su A.G. Bisa jagiorancin Yaya Abubakar shima Abba aka kaisu suka dubashi. dan shima dai prison ɗin za'a miƙasa bisa hukuncin alƙali zaiyi shekaru ashirin a gidan yarin. Anan ko Ummi komai batajiba sai ma kallon kaɗan ka gani dataima Halilun. Hakama su Yaya Usman ko'a kwalar rigarsu tamkarma ba dubiyarsa sukazo ba. Basu wani jimaba suka koma gida abinsu.


___________________________________


Tun Hibbah nasan ran Master harta cire rai, dan tsahon kwanaki biyar kenan babu shi babu alamarsa. Harma sun bar wannan gidan sun koma gidansu da yau Hibbah ta fara shiga. Duk da damuwar rashin ganin mijinta dake cin ranta haka ta danne ta nuna farin cikinta akan cigaban da yayunta suka samu. Dan ko gida sai sam barka komai yaji gishiri da magi. Sai fatan ALLAH ya sauki su Hafsat lafiya kuma.
Sarai Ummi na lure da halin da Hibbah ke ciki na kewar mijinta amma ta fuske. Kowa yaƙi mata maganar Master ɗin ma a gidan dan ba'ason sanar mata baida lafiya kamar yanda ya roƙa a ɓoye mata har sai ya warke kan hankalinta ya tashi. Ba kuma dan ciwon ma kaɗai ya nisanceta ba. Harda shirye-shiryen ƙarin girma da zai samu shi da wasu tawagar jami'ai irinsu yaya Abubakar. Dan haka yay tunanin haɗewa da ɗan walimar cin abinci na ƙara'in bikinsu da ba'ayiba dana komawa sabon gidansu da yake fatan suyi rayuwa ta din-din-din shi da sauran ƴan uwansa.
Sai da Ummi taga damuwar Hibbah na fitowa ƙarara akan fuskartane ta zaunar da ita tai mata nasiha da kwantar mata da hankali akan wani babban uzirine yasa Master ɓuya amma yana nan dawowa daga tafiyar da yayi nan kusa. Ta ɗanji sanyi, amma taji ciwon rashin sanar mata da yayi bai kuma nemeta koda a waya ba balle ta san tanada kima a garesa.
Da wannan damar Ummi da Mama Jiddah amaryar Sheikh Aliyu Maina da Uwargida ran gida Maimunatu sukai amfani wajen gyare Muhibbat ɗin ciki da bai da kayan gyaran jiki dana fata gangariya da ƙamshi. Tare da zaunar da ita suka fara ɗora mata karatu na musamman akan aure da zamantakewar cikinsa. Haƙoƙin miji akan mace da na macen ma akan mijinta.
A gefe kuma kayan auren Hibbah da aka shirya tun lokacin auren a gidan da Master ya bada matsayin Muhammad Shuraim tuni an kwashesu an maida inda zasu koma ɗin an jere mata su tsaf.


★★


A ɓangaren Master ma cike yake da tsanin kewa da buƙatar matarsa. Sai dai yayi ƙoƙari matuƙa ya danne wajen ganin yama Ummi kawaici dan itace da kanta ta buƙaci yabar Hibbah a kaita kamar kowacce mace gidansa ita da su Yaya Muhammad. Bazai iya musa musu ba, dan sunyi matuƙar ƙoƙarin a garesa. Hakan yasashi yin amfani da wannan damar shima yay nasa shirye-shiryen da ƴan ƙannensa bayan jiyyar daya sha ta gajiya da sauran raunin jikinsa.
Abinda kuma bai sani ba su Habib gagarumin biki suke shiryawa tare da Abdull da su I.G dayay burin hakan akan auren Master sai dai ALLAH bai nufa ba. Dan haka yay ƙudiri da aniyar biyan bashi a yanzu bayan yayi tattaki har gidan Sheikh Aliy Maina sun bada haƙuri akan yanda abubuwa suka faru, kasancewar su Yaya Muhammad suma suna tare da Sheikh Aliy ɗinne akan zaman dama duk sai suka nuna babu komai ƙaddarace ai wadda ta riga fata. Fatansu dai ALLAH yasa hakan shine alkairi ga Master ɗin da Muhhibat a yanzun.


Al'amarin kamar wasa sai ga Muhibbat ta cika watanni biyu a gida tana jiran tsammani. Tayi wani irin masifar ƙyau da haske dake bama kowa mamaki, su Zahidah na tsokanarta akan cikine. Ita dai bata tanka musu duk da tanajin fargaba har cikin ranta. Dan da gaske watanni biyun nan datai a gida bataga al'adarta ba sam. Sai dai kuma ita sam batajin ciwon komai a jikinta dan haka take fatali da batun nasu.
Ummi kam a yawan barcin da Hibbahn keyi a kwanakin nan yasata zargin ko cikinne da ita. Sai dai rashin ganin sauran alamomi yasata ajiye zargin nata itama dai.
A randa Hibban ke cika wata biyu da sati guda a gida aka sallamo Hajiya Mama. Ƙin amsarta su Momy sukayi acan gidan dan haka yaya Abubakar ya kawota nan wajen Ummi. Ummi bata musa ba ta amsheta kodan yaranta da darajar Aliyun ta da bazata taɓa iya manta hallacinsa ba shi da Malam. Ɗaki guda aka warema Hajiya maman ta cigaba da jiyya. Su Yaya Muhammad suka ɗakko mai kula da ita acan ƙauye cikin ƴan uwanta da ƙyar. Ko sau ɗaya Hibbah bata taɓa leƙa ɗakin hajiya mama ba domin dubata. Hakama Ammar da Yaya Umar da sukafi kowa tsanarta. Ummi tayi nasihar harta gaji ta sanya musu ido kawai.


Shirye-shiryen tarewar Hibbah ake sosai a gidan, dan kwanaki biyu kacal suka rage amarya harta sha lalli ƙafa da hannu, tare da kitso na musamman irinn ƴan maidugiri da wata ƴar da Jiddahn ya Sheikh ke riƙo ta fanin Umminsu tai mata. Gyara kam ta shasa harta gaji, dan bayan gyaran dasu Maimoon uwar gidan yah Sheikh ke mata a ɓangaren mamansu Zahidah ma sun gayyato shahararriyar mai haɗaɗun kayan gyaran jikin nan mai kamfanin *mg's skin care*, tun daga kan mayuka, sabulai kala-kala na maida tsohuwa yarinya. *(08062991549)* akan farashi mai sauƙi da rahusa ta haɗa mata kayyaki na musamman da dorata akan kayan shafa dana gyara na mata masu aji ta kowanne fanni itama tana katalleta.
Haka kawai yau Hafsat ta tashi da ƙwazabar son yin gasashen kifi saboda ƙwazaba irin tamai ciki. Kasancewar matar Yaya Muhammad ita kuma sam bata shiri da kifin yasa Hafsat tahowa sashen Ummi tayi dan maƙwafta sashen Hafsat da Maimunatu (Kausar) suke. Koda ta gayyaci Hibbah ta tayata ƙin zuwa tai, kamar wasa ƙamshi ya fara sirɗaɗowa falon Hibbah na kwance tana kallo. Da farko dai ta ɗan fara yamutse fuska har Ammar na tsokanarta da cewar gulma. Ƙin kulashi tai dan ita kaɗai tasan mi takeji a tsakkiyar kanta game da ƙamshin kifin nan. Ammar da bai fahimci halin da take a ciki ba ya miƙe yana mata gwalo ya shiga kitchen wajen Hafsat ɗin. Ko mintuna uku baiyi cikakku da shiga ba suka jiyo tamkar gudu a falon. Cikin hanzari suka leƙo dan Hibbah suke zargi dama.


Hibbah da aman daya yunƙuro mata yaci ƙarfinta dole ta durƙushe tan gab da isa ɗakinta ta sakesa a matuƙar wahale. Kanta suka nufo da gudu cikin tashin hankali da tambayarta lafiya?. Ina bama tasan sunai ba. Dan da alama dai aman baizo da wasaba. Hatta Ummi dake ɗaki tana azkar na yamma da sauri tayo waje. Haka ma mai kulla da Hajiya mama babu shiri ta fito duk suka rufu akan Hibbahr datai matuƙar jigata. Dan ko aman yayi kamar zai tsaya da ƙamshin kifin ya sake shiga hancinta saita sake sabon yun ƙuri.
Fashewa tai da kuka jikin ta na rawa ta sake mamuƙe hanun Ammar dake riƙe da ita. “Y...ya...ya Ammar banaso ku fita da ki.f.in”. Ta faɗa da ƙyar tana sake sakin sabon kuka. Cikin sauri Hafsat ta nufi kitchen domin fita da kifin, yayinda Ammar ya ɗauka Hibbah ɗin gaba ɗaya sukai ɗakin Ummi dan a samu tabar jin ƙamshin kifin.
Yanda ta galabaitan dole ne ta baka tausayi, da taimakon Ummi ta gyara mata jikinta a toilet ɗinta da Ammar ya kaita can direct. Kuka take wiwi jikinta duk ya saki harda su ɗan zazzaɓi. Har yanzu kuma jin kamshin kifin take har tsakkiyar ƙwalwar kanta saboda tsaya mata da yay a rai. Ummi data gama gaskata cikine da Hibban ta kamota suka fito a toilet ɗin. Zaunar da ita tai a gado ta fita zuwa ɗakinta ta ɗakko mata wasu kayan. A falo ta wuce Ammar da Hafsat na gyara wajen da Hibbah ta ɓata.
Ummi na dawowa da kayan ta iske Hibbah harta kwanta. Ɗagota tai ta taimaka mata ta saka kayan tana jera mata sannu tausayin autar tata na ratsata.
“Ummi ki bani wani abun na shinshina ko zan daina jin ƙamshin banaso zan sakeyin amai”.
Cikin lallashi Ummi dake murmushi ta shiga shafa kanta bayan ta kwantar da ita a jikinta. “Tanee ki ciresa a ranki kawai shine zaisa kibar jin ƙamshin a hancinki, dan tuni Hafsat ɗin ma ta fitar da shi a sashen nan. Amma faɗamin mikike son ci?”.
“Ummi banajin yunwa, sai dai kozan samu tumatur masu ƙyau da suka nuna sosai zansha”.
“Abu mai sauƙi”.
Ummi ta faɗa tana miƙewa bayan ta kwantar da Hibbah. Cikin lokaci ƙanƙanin sai ga Ammar da duk yay kalar tausayi kamar shine mara lafiyan da manya-manyan tumatur masu ƙyau a ƙaramin bowl har kusan goma ya kawo mata. Dan anyi sa'a an kawo musu cefanen dama babu jimawa.
Sagade yayi yana kallon Hibbah nashan tumatur ɗin cikin rawar jiki tamkar wadda ta samu wani apple ko inibi. A wannan halin su Yaya Umar da suka shigo gidan matansu suka sanar musu suka shigo suka sami Hibban. Su kansu mamakin shan tumatur ɗin suka tsayayi har Yaya Umar na yima Ammar faɗa.
Amarairaice Hibbah ta ce, “Yaya inasone akwai daɗi”.
Yaya Umar zaiyi magana Ummi ta ɗan girgiza masa kai. “Karka damu Umar barta tasha. Tunda shi zuciyarta keso shi kaɗai zatasha a zauna lafiya inhar ya zauna.”
Shiru kawai sukai badan hakan ya musu ba. Hibbah na kammala shan tumatur ɗinta kuwa ta zame ta kwanta dajan bargo tana sauke tagwayen ajiyar zuciya, nutsuwa na ratsata. Wahalar data sha yasa barci saceta cikin ƙanƙanin lokaci batare data shirya hakan ba.


Koda ta farka kusan bayan magrib garau ta tashi tamkar ba'ita ba. Sai dai ɗan rashin ƙarfin jiki da takeji shima bamai cutarwa ba. Salloli tayi ta fito falo inda take jiyo hayaniyar yayunta da matansu suna hira. Duk sunyi farin cikin ganinta garas. Suka shiga tambayarta jikinta tana amsa musu cikin shagwabar tata saba musu. Suko da kulawa suketa sake sonjin ko tana son wani abu da zataci. Kanta ta girgiza musu tana kaiwa zaune da faɗin, “A'a yaya ku kwantar da hankalinku zanci duk abinda aka dafa indai babu wancan abun na ɗazu (ko sunansa batason faɗa dan ma karta tuno). Sunji daɗin hakan suka sake mata addu'ar sauƙi mai ɗorewa. Daga haka suka cigaba da hirarsu tana lafe a jikin Umminta da tun ɗazun take cikin tsantsar farin ciki akan baiwar da ALLAH yay mata na albarkar auren ƴaƴan nata biyar reras kusan lokaci guda. Bata yarda tayi zancen cikin dasu ba dan batason ma zancen ya fita har sai Hibbah ta tare gidan mijinta. Shiyyasa tunkan aje ko'ina ta cewa Hafsat ma tai shiru da bakinta ko mijinta karya sani tunda ta lura Ammar shi dama bai fahimci komai ba garan😂.............✍




*_MATAYEN ƘWARAI KUNA INA NE?._*




_Maza ku garzayo da gudunku ga ƴar zuru mamar zee-zee mai kayan mata na maida tsohuwa yarinya💃🏻._


*Kayan matan ƴar zuru zasu maidaki shalele ƴar gaban goshin maigida koda kina da kishiya ƴar birnin shehu😂💃🏻*.


_Kayan ƴar zuru nada matuƙar sirrika da inganci irin wanda sai an gwada akansan na ƙwarai. Idan da ƙyautar gida akemiki a master room kikai amfani da kayan ƴar zuru Nigeria za'a baki harda jirigin sama na yawata ƙasashen duniya😉💃🏻_.


*MUNADA KAYAYYAKI KAMAR HAKA*👌🏻


Kaza akwai 10k
15k
5k
Tsimi 5k 10k
Matsi 5k
Gumba uku 2k
Zumar gorun tula syrup3k
Garuka 3k
Cicccibi 5k
Zakara 20k
Zabo20k
Humra
Turaren tsugunni
Butar tsarki
Maganin infection
Tsimin tabaje
Turaren al,ajab


*Muna maraba da maisayen ɗaya ko sari, kayanmu garantee ne in har basuyimaba zan maidama kudinka*.

_Address maberar jariri bayan FGC sokoto_
08068526455


*Zaku iya saving number ta domin ganin hajata*


Zaku iya samun mu amanhajar


Facebook
Istagram


Yar_zuru_mamar_zeezee- kyn_mata.


Sai kunzo🥰🥰🥰🥰💃🏻👌🏻.







*_Typing📲_*






______________________




*_MATAYEN ƘWARAI SARAKAN ADO DA ƘAWATA JIKI DA KWALLIYA KUNA INA NE?._*




_Maza ku garzayo da gudunku ga mutunuyar taku maida tsohuwa yarinya ta sake dawo muku da sabon salo, sabon sunfarin kayan gyaran jiki na mayika da sabulai ƴan gaske💃🏻._


*Kayan kwalliya na mg's skin care zasu maidaki shalele ƴar ƙwalisa tamkar wata ɗan daren sha biyar koda kina da kishiya ƴar Morocco bata girgizaki ba, balle saurayi ɗan son ƙyale-ƙyale da ƙawa ga burwallensa😂💃🏻*.


_Kayan mg's skin care nada matuƙar sirrika da inganci irin wanda sai an gwada akansan na ƙwarai.




*MUNADA KAYAYYAKI KAMAR HAKA*👌🏻


Hajiyata shin menene matsalanki, pimples ne?
Spot? sunburn,acne, stretch marks, knuckle, wrinkles, Black head,ko kinshafa Maine yabatamiki jiki
Inamai shaidamiki cewa ynx ne lokacin dayakamata kiyake dukkan wadannan kema kidinga fita sakayau abunki baruwanki da kunshe fuska ko kice sekinyi makeup hjy fita zar abunki kinuna ainihin natural beauty dinki😍domin kayanmu gbdynsu organic ne babuna bleaching zssu sa ki haskaka fatarki tayi ta kyalli kamar madubi ze fiddomiki d ainihin natural beauty dinki ne😘kunaji barin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login