Showing 75001 words to 78000 words out of 165076 words

Chapter 26 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74013

hasashenta yayi dai-dai azzalumi Abba ne ya farga naji sirrinsu yasa aka satoni aka kawo nan. Shikenan an ɗaura auren yayunna da ƴaƴansa. Shikenan zai kashe min ƴan uwa) ta shiga ayyano hakan a ranta. Tai saurin dafe kanta da ya sake sara mata.
“Abba mi mukai maka da zafi haka? Miyasa kai azzalumi ne maci amana. Ya ALLAH ka karemin ahalina daga cutarwar waɗanan azzalumai fasiƙan mutane. Ya ALLAH bamu da wani ƙarfi sai naka, kai ne bangonmu abin jingina ka tallafi maraicinmu dana mahaifiyarmu ka bamu kariya”. Yanda take maganar tana kuka abin tausayi.
Sai kuma taɗan zabura saboda tunowa da ko sallar Azhar na ranar jiya batayi ba. Dan a dai-dai lokacin da akeyinta tana tare da su Abba. Miƙewa tai a zabure. Duk da jirin da ke kwasarta bata saurara ba sai da ta dangane da ƙofar da take ƙyautata zaton toilet ne da ƙyar. Cikin sa'a kuwa ta samu toilet ɗinne, duk kuma abin amfani akwaishi a ciki. Shawarar zuciyarta tabi cike da dauriya ta haɗa ruwan wanka mai zafi sosai, kayanta ta cire tana faman layi da dafe kai. Bayan ta cire kayanta da ƙyar cikin ruwan ta shige gaba ɗayanta tana sauke nannauyar ajiyar zuciya da numfashi. Yanda ruwan ke ratsa kowacce gaɓa ta jikinta haka jijiyiyin jikinta ke saki a hankali wani ɗan ƙarfi-ƙarfi na mamayeta. Sai da taji hankalinta ya dawo jikinta kafin ta miƙe daga ruwan da har ya huce tai wanka sama-sama. Ganin sabon brush ya sata ɗauka tayi sannan ta ɗaura alwala. Tasan bata da wasu kayan anan. Babu kuma tabbacin samu dan haka ta maida wanda ta cire ta fito. Dan gaba ɗaya hankalinta kuma ya koma ne ga sallolin da ke a kanta.
Ɗan kwalinta ta shimfiɗa a ƙasa tare da ɗaukar yagaggen hijjab ɗin ta ta ƙulle daidai wuyan ta saka tama mamakin yanda akai ya yage haka ta tada salla. Duk yanda shaiɗan yaso mata kutse cikin sallar da bijiro mata damuwa da tashin hankalin da take a ciki haka ta dinga turesa tai sallarta a tsanake tana faman zirar da hawayen. Tsaf ta kammala rama sallolin har zuwa sallar asubahi. Taja doguwar addu'a akan wannan yanayi da suke ciki tana kuka. Ta jima a wajen zaune har rana ta fito sosai. Agogon ɗakin ta kalla, ganin takwas har tayi yasata miƙewa ta sake nufar gadon saboda yunwar da takeji da rashin ƙarfin jikinta. Karaf idanunta suka sauka akan wayarta dake tsakkiyar gadon, da alama dai a wajen bacci ta fita da ga cikin zaninta. Wani irin daɗi ne ya lulluɓeta. Ta kai hannu ta ɗauka da sauri tana murmushi da share hawayenta. Cikin rawar jiki da matsanancin ɗoki ta danna kiran number yaya Muhammad.
Sai ɗan yarfa hannuwanta ta ke da cizar lip ɗinta na ƙasa cike da zumuɗin son jin ya ɗauka......
“Ko zaki shekara kiransu bazasu gani ba, koda kuwa ta shiga ne”.
Wata ƙasaitacciyar murya ta faɗa a bayanta. A zabure Hibbah ta juyo duk da rashin ƙarfin da jikinta ke da shi. Babu shiri ta sake zabura tai baya, duk da kuwa tayi tunanin shiɗin zata gani anan tunda yaron su Abba ne. “Shuraim?!” ta faɗa a ɗan kausashe tana masa wani irin kallon tsana.
“A.K.A Master!”. Ya faɗa yana cigaba da takowa cikin izza da kasaitarsa tsakkiyar ɗakin. Sai da yazo gab da ita ya kai hannu saman face nashi ya cire facemask ɗin face ɗin Shuraim.
“What?!!”. Hibbah ta faɗa tana sakin wayarta ƙasa a ɗan firgice.
Wani ƙasaitaccen murmushi ya saki da cigaba da takawa gabanta har yanzu hannayensa duka na zube cikin aljihun wandon jeans ɗin jikinsa. Ganin yanda ya ke tinkarota yasa ta fara ja baya tana jifansa da wani irin kallon tsana da ruɗanin ganin facemask a matsayin fuskar Shuraim, (kenan sace Shuraim yayi ya maye gurbinsa da shi?). Jin ta dangane da jikin bango ya sata rumtse idanunta da ƙarfi zuciyarta na wani irin harbawa dan gaba ɗaya tama rikice, gashi babu ƙarfin yin tsiwar dake cin ranta gareshi.
Sosai ya matsa jikinta har suna jin fita da saukar numfashin juna. Hibbah ta sake maƙurewa a bango dan tsoro da rashin sabo. Shiko tsumammun idanunsa ya zubama fuskarta tare da zaro hannunsa ɗaya daga aljihun wandon ya ɗaura bisa bangon ya tokareta ganin zata zille.
Matse jikinta tayi da sake rumtse idanunta dan har cikin ranta bata fatan ya taɓata kodan tuna ƙazantar da suke aikatawa shi da su Abba da tayi. Shiko fuskarsa ya sake kaiwa gab da tata tamkar zai haɗe bakinsu sai kuma ya waske akan kunnenta. Cikin kaushin muryarsa mai amo da saka razani ga abokin gaba ya fara magana,
“Babu farauta mafi wahala a duniya sama data *_DAMEESA_*. Da ga yau da ga yanzu ki sani. Master tamkar google yake. A kowane lungu da saƙo yanada ido tamkar google a yanar gizo. Duk wanda ya ce zai hanani barci, shima bazaiyi nasa ba. Ina fatan kin ganee karatun?!!”.
Ya ƙare maganar da ɗan bubbuga hanunsa jikin bangon cike da tabbatarwa da kaushin murya yana jan jikinsa baya.
Nannauyan numfashi Hibbah ta fisga jin ya matsa a jikinta. Ta buɗe idanunta ta watsama bayansa da ya juya harara. Cikin yunƙurowar tsiwar tata da a yanzu ta samu filin fita tace, “Ni kuma Muhibbat Aliyu Hamza gwarzo sai na karya wannan alwashin naka, ina a cikin gidan nan tare da kai zanyi sanadin da za'a faraucekan cikin sauƙi a kuma kama ka. Idan takamarka haɗa hannu da munafukai kuna zaluntar mutane ku sani ko'ina bazakuje ba. Kuma wlhy ko ƙwarzane ya sami ɗaya da ga cikin yayuna sai kayi nadama da ga kai harsu ƙazamai masu ɓoyayyar manufa suna aikata ƙazanta da fasadi aban ƙasa. Shuraim kuma da ka saci fuskarsa kazo ka wargaza aurenmu a ranar ɗaurasa, idan ma ɓoyesa kai ko halakashi kasani sai na ɗiba fansar jininsa akanka”.
Wani shegen malalacin murmushi ya saki. Tare da fara tafa hannayensa a hankali yana juyowa gareta cikin salo da ƙasaita. “Nice baby girl, ina son irin haka👌🏼.”
Sai kuma ya tamke fuska yana sauke mata razanannen kallon da har cikin ranta takejin hantar cikinta na kaɗawa. Amma tsaurin ido da tsiwa ya sata ƙoƙarin danne hakan tana hararsa harya ƙara takowa inda take.
Gira ɗaya ya ɗage da yin mutsu-mutsun fitina da idanunsa. “Da ni Master kike tunanin yin *_TAKUN SAAƘA?._* Lallai zan baki dama, tabbas kuwa zan baki, amma sharaɗin faɗuwa ko nasara zan zartar da sune a lokacin da ɗaya ta kasance.....”
“Ko ka bani ko karka bani dama damata a hannuna take na tona muku asiri. Satoni da kukayi nan bashine ke nufin nasara ba ko cigaba da rufuwar sirrinku. Ɗaura auren yayyena da ƴaƴansa da kuka ƙulla bashike nufin nasarrku akan ahalina ba. Dan haka ka sani, *_TAKUN SAƘA_* da kai dama a cikinta nake tsundum. Dan koba komai a harin farko na maka TAMBARIN da ya saka gudun ceton rai batare da kayi tsammani ba mai idon google”.
Ƙafa yasa ya taɗeta ta faɗa saman gadon, cikin zafin naman da ALLAH ya azurtashi da shi ya ɗaura ƙafarsa ɗaya akan gadon tare da ranƙwafowa kanta. Ƴar mitsitsiyar bindigar da ya zaro a aljihun bayan wandonsa ya ɗaura mata a kan kunne yana zuba firgitattun idanunsa cikin tsakkiyar nata. “Zan iya kasheki a cikin wannan gidan. Na binne gawarki batare da wani mahaluki ya taɓa tunanin binciko inda na kafa ramin ba”.............✍



TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*






*_Typing📲_*








*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*


https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share


*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*


https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb




_______________________






*_Chapter Twenty Five_*


...........Hibbah ta haɗiye yawu da ƙyar da ƙoƙarin haɗiye tsoronta ta zuba masa harara. “Dan ka kasheni ai ba abin mamaki bane, mutumin da ya ke gawurtaccen ɗan Homo ne kashe rai zai zama abin damuwa a garesa, wama yasan iya adadin nawa ka kashe ka binne a gidan”.
A yanda tai maganar cikin tsoro da ƙarfin hali yay matuƙar bashi dariya. Sai dai ya shanye abarsa cikin rai, a zahiri ma sai sake tamke fuska da yay yana yamutseta. Ya janye bindigar a kanta tare da kaita ya ɗan buga a saman laɓɓanta. “Wannan bakin naki shine zai halakaki stupid girl”.
Ya faɗa yana sauke ƙafarsa ƙasa da miƙewa da ga ranƙwafowar da yay a kanta yana ƙwafa. Nannauyan numfashi Hibbah ta sauke a ɓoye da lumshe idanunta ganin ya fice a ɗakin ko waiwayenta baiyi ba, tai saurin kai hannu saman ƙirjinta ta dafe saboda yanda yake bugawa da sauri-sauri. Dan harga ALLAH ƙarfin hali kawai tayi da ganin wannan bindigar akanta. Ga shegun idanunsa da ke saka zuciyarta tsargawa tamkar zatai zallo ta fito waje idan ya zuba mata su. A fili tace, “Gashi ɗan iska ɗan homo, amma sai shegen kwarjini.


(Hibbarmu karki sake kiji tsoronsa. Dan karma su o.e ƙannensa suji kansu ya ƙara girma ehe😖😎🚶🏻😏.)


★★★★★★



Dauriya Ummi kawai takeyi na rashin ganin Hibbah bata shigo musu ba har kusan goma na safe. Tanaji a ranta anya su Yaya Muhammad basa ɓoye mata wani abu kuwa? Dan babu yanda za'ai su kwana gida ɗaya da Hibbah ta iya haƙurin kawai yanzu bata nema inda take ba. Musamman anan da take ganin sabon gida tunda ba'a taɓa zuwa da ita ta gani ba sanda ake ginin. Hasalima babu wanda ya taɓa sanar mata ita da Ammar. Sai da ga baya ne Ammar ɗin ya sani, suka kuma gargaɗesa da kar ya faɗama Hibbah.
Shigowar Isma'il gidan kusan sha ɗaya na safe ne ya ɗan rage mata ƙulafucin son ganin Hibbahn. Bayan sun gaisa cike da girmamawa yay mata bangajiyar biki tare da yima anguna addu'ar zaman lafiya.
Cike da kulawa a garesa Ummi da ke murmushi ta ce, “Saura kai Isma'il. Ya kamata ka nemo matar aure haka nan, dan shi aure cikar kamalace ta ɗan adam koda ace ya kasance mutumin banza ne. Idan kuma kaima irin nasu Usman ɗin zan maka to”.
“Ƙayataccen murmushi ya saki da sake duƙar da kansa yana shafa ƙeya. Ummi karki damu kiyimin addu'a kawai”. Ya faɗa murya a tausashe saboda yanda yake jin Ummi matuƙa a rai kodan yana ƙishirwar mahaifiya.
“Kullum addu'ar nan ita muke muku Isma'il. ALLAH ya cigaba da tsareku a duk inda kuke. Ya baku kariya da ga dukkan abun ƙi. Yay muku albarka ya baku ƴaƴa nagari da zasu kwatanta muku ƙyautatawar da kuke mana da biyayya”.
Tasowa yay ya durƙusa gaban Ummi hawaye na ciko idanunsa, yay haɗiyesu da ƙyar yana faɗin, “Amin ya rabbi Ummi nagode”.
Hannunta ta ɗora saman kansa ta shafa dan tsaf ta fahimci abinda yake buƙata kenan. Tausayi yake bata yaron har cikin rai, dan ta jima da nazartar yana matuƙar bege da ƙishirwar mahaifiya ne.
“ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai albarka Ummi”.
“Amin Isma'il”. Ta faɗa tana murmushi da sake shafa kansa har fararen haƙwaranta na bayyana.
“Uhmm kaga ɗan gatan Ummi, ashe kana nan?”. Su yaya Abubakar da ke shigowa suka haɗa baki wajen faɗa suna kallon Isma'il ɗin. Ƙaramar dariya yayi da miƙewa da ga gaban Ummin ya koma inda ya taso. “Gara nai sauri na kwashi rabona kafin kuzo ai mana raba dai-dai.
Usman da ke dariya ya ce, “Gaskiya Yaya Isma'il i'm jealous”.
Dariya suka sanya gaba ɗayansu harda Ummi. Kafin su ƙaraso cikin ɗaki su mimmiƙa masa hannu har Yaya Muhammad. Da ga haka suka zauna aka dasa sabuwar hirar da ta sake ɗauke hankalin Ummi duk da kuwa zuciyar tata naga son ganin Hibbah ta shigo. Dan a cikin firarma sunayi suna sakko sunanta da rashin jinta suna dariya. Basu taso gaban Ummi ba sai ƙarfe ɗaya suka fita massallaci. Da ga nan Isma'il yay gaba su kuma suka koma cikin gidan da yake ya ƙara cika da dangin amare ƴan buɗar kai dan yau anguna zasu shiga ɗakunansu.


★★★★★


A ɓangaren Abba kam barazanar rashin barci da ya fuskanta a daren jiya ce ta kaisa ga makara sai kusan takwas ya farka. Farkawar ma ba kaitsaye yayita ba masifar Momy ce da ta dawo asibiti ta gansa yana barci ta farkar da shi.
“Yanzu wannan wane kalar rashin mutunci ne haka Hadiza? Ina tsaka da barci kizo ki tadani saboda rashin mutunci”.
“Ni da kai a tantance mara mutuncin Abban Junaid. Yanzu dan ALLAH ko kunya bakaji ba ɗan ka namiji tilo na asibiti rai a hannun ALLAH amma kai kana nan kana barci hankali kwance. Bakaje kaga halin da yake a ciki ba baka ɗauki wani matakiba kuma ga wanda ya aikata masa. To sai ka miƙe dan Asiya da yaranta duk basa gidan nan. Yanda alamu ma suka nuna basu kwana ba a cikinsa”.
“What?!”
Ya faɗa yana wantsalowa da ga gadon ƙirjinsa na wani irin bugawa. “Hadiza wace maganar banza ce wannan. Ita Asiyan idan ta fita anan gidan ubanwa zataje tunda bata ajiye kowa ba bayanan nan ɗin?”.
“To waya san ko tana da wajen zuwan abu a duhu. Ga dai Hajiya mama can ta gama bincike ko ina na gidan nan ita da su Garba amma babu komai kama da su. Alamuma sun nuna dama da shirin hakan tare da su dan duk sun tattare kayansu masu muhimmanci da ga sashen”.
“Kutuman bura'uban nan kayyasa”. Abba ya danna ashariya tamkar ɗan gidan maguzawa. Ita kanta Momy jin ashariyar tasa sai da ta zaro idanu waje. Hannu yasa ya ingijeta tare da fisgar sandarsa ya yo waje. Tun daga sama yake hango su kawu bello tsaye cirko-cirko a falo cike da tararrabi.
Bai iya tanka musu ba tsabar rikicewar da yay ya fice da sassarfa duk da azabar da yakeji sabuwa ƙafarsa na masa.


Tabbas babu alamar Ummi da ƴaƴanta a gidan. Wannan al'amari ya matuƙar hautsina kan Abba. Babu shiri ya shiga bige-bigen waya. Kafin ya tattara yabar gidan batare da ya tuna da ƙarin sallar asuba da ke a kansa ba bayan sallolin jiya da bai sauke ba har yanzun.
Yayinda ya bar ƴan biki nata kace nace akan wannan al'amari. Harda masu yima ƴaƴan Ummi da ita kanta addu'ar tsiya suna mai goranta mata asalinta. Oho bama tasan sunai ba, su aiki ya sama😜👎🏻.


★★★★★


A ɓangaren Hibbah kam Master na fita babu jimawa taji sallama a ƙofar ɗakin tare da knocking. Sam jikinta babu wani ƙarfi dan yunwa takeji matuƙa ga rashin ƙarfi. Hakan yasa tun bayan fitarsa bata motsa da ga inda take ba. Tunanin shine ya sake dawowa ya sakata harar ƙofar tamkar idanunta zasu faɗo. Ta kuma ƙiyin magana.
Baba Saude dake tsaye ta sake ɗan buga ƙofar da ɗaga murya sosai wajen sallamar. Ɗan zabura Hibbah tayi jin muryar mace. Ta amsa da ƙoƙarin son tashi, sai dai kafinma ta tashin Baba Saude da taji an amsa mata harta shigo abinta ɗauke da tray.
Wani irin daɗi ne ya tsarga zuciyar Hibbah ganin mace. Macen ma babba da zata iya kira uwa ko kaka. “Sannu mama” ta faɗa cikin girmamawa. Murmushi baba Saude tai mata tana ajiye trayn.
“Yauwa ɗiyata sannu kinji. Yaya ƙarfin jikin naki?”.
Da ɗan mamakin jin abinda tace Hibbah ta dubeta. Har zatai magana sai kuma ta fasa ta amsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login