Showing 72001 words to 75000 words out of 165076 words

Chapter 25 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74037

Isma'il yayi zaune sosai yana saki ƴar dariya. “Yayanmu lamarin tsohuwar nan ne sai da haka. Sai dai fa nasan wlhy ba haƙura sukai ba, dan da alama na jima wancan wawan yaron Junaid ciwo a haƙarƙari. Ummi inhar shirinku na barin gidan nan na nan to lallai dole ne ki tafi kema a yau ɗin nan. Kamata yay ma ace yanzu kawai. Kinga sai ki tarbi amare da kanki”.
Yaya Abubakar da har yanzu shi dai yake kallon Isma'il ɗin cike da nazari da wasiwasi ya gyaɗa kansa cikin gamsuwa. “Wannan mafita ce mai ƙyau. Dan Abba kam ba kanwar da za'a lasa bace aji kaifi kawai. Ummi kamar yanda Isma'il ɗin ya faɗa barin gidan nan yanzu shine mafita kawai”.
Sosai itama Ummi ta gamsu da zancen. Dan duk abinda zai ɓata mata taron auren yaranta bata fatansa. Sarai kuma ta fahimci abinda su Hajiya mama ke burin yi kenan. Sai dai kuma cikin damuwa da rauni ta ce, “Tanee ɗin fa an ganta?”.
Da sauri Yaya Umar ya gyaɗa mata kai. “Eh karki damu tana tare da ƙawayenta ashe. Zuwa anjima nasan zatabi masu kai su can kawai”.
Duk da zuciyarta a raunane take hakan bai hanata gamsuwa ba. Ta mike tana warware mayafinta da dama tana tare da shi tun ɗazun ta sake yafawa. Dama ba wani muaten bane sosai a sashen. Makwafta da suka shishshigo sukai mata ALLAH sanya alkairi duk sun fita saboda yamma tayi sosai. Sai ƙawayenta na kusa sosai irinsu Hajiya Mardiyya. Suko sunsan da shirin barin gidan. Dan dama sune zasuje amsar amare acan. Jin hukuncin da su Yaya Muhammad ɗin suka yanke ne ya sakasu mimmiƙewa suma suka hau kimtsawa.
Su Ummi basu da matsala da komai na sashen dan sun tsince masu muhimmancin sun killace sauran. Su hajiya mama nacan akan Junaid cike da ruɗani suka samu suka fice dan dama gari ya fara duhun magrib da ake ta faman kira a masallatan anguwar. Mutanen da ke a tsakar gida kuwa gulma da tsugudidin da suka haɗa kai sunayi group-group yasa basu hankaltu da su Ummin ba. A tunaninsu kawai ƴan biki ne zasu wuce gida.



★★★★★



A can L.E street kuwa cike da farin ciki da ƙaunar yaran har cikin rai baba Saude ta mike domin gabatar da sallar la'asar ɗin itama. Tana idarwa ta fito ta hau shirya musu abincinsu na rana da basu ci ba.
Kasancewar yunwar kuwa na ƙwaƙular cikinsu ana idar da sallar la'asar ɗin suka dawo gidan. Sai dai su kaɗai suka shigo falon banda Master da yay zamansa a ƴar runfar bunun da ke a gefen swimming pool ɗin gidan. Dan yasan tunda suka dawo gidan shegen surutinsu ba zai barshi ya huta yanda yake bukata ba.
Suko da ga can cikin zalamar kayan daɗin da baba Sauden ta baje musu a babban dining ɗin suka baje da fara ɗurama cikinsu. Yayinda kowa ya fara kai lauma sai sabon surutu ya ɓalle, baba Saude na gefe na musu dariya kamar yanda ta saba har suka kammala. Sune suka zaɓar mata ɗakin da zata zauna anan downstairs ɗin. Hundred percent kuwa ta gamsu da ɗakin, dan yana ɗan nesa da ɗakunansu ga shi kuma gab da kitchen.
Sune suka shiga gyara mata komai duk da bama wani datti bane da ɗakin. Bayan sun kammala Salis yay list ɗin abubuwan da yasan Baba Sauden zata buƙata na amfani musamman a toilet. Da ga haka suka dawo falo kowa ya kama hidimar gabansa. Lokaci-lokaci suka sakko zancen Zaidu da ke can gidan su Hibbah yana gano duk cakwakiyar da ke faruwa batare da kowa ya fahimci shi ɗin wanene ba.


*_8:16pm_* ya shigo gidan. Lokacin su Idris da dawowarsu da ga sallar isha'i babu jimawa na baje a falo suna kallon ƙwallo. Duk sun cika falon da hayaniyar gaddamarsu.
Khalid da ya fito da ga kitchen riƙe da drik ne ya fara farga da Master da ko sallamarsa basu ji ba. Cikin ɗan daga murya yanda zasu fahimta ya ce, “Barka da dawowa Master”.
A take falon kuwa yay tsit duk suka juyo ga ƙofa. Cikin ɗan hararsu ya ajiye ledojin da ya shigo musu da shi ya haura sama da ɗaya batare da ya amsa sannu da zuwan da suka haɗa baki wajen masa ba. Suna ganin ya gama hayewa har rige-rige tasowa Zaidu da bai jima da dawowa gidan ba suke shi da Salis wajen zuwa su ɗauka ledojin da ya jiye. Suma sauran tasowa sukai akan ledojin cike da farin ciki da ƙaunar Mastern nasu.
“Dalla malamai karkuyi mana hayaniya anan kuja a samu barcin dole”. Cewar Adam yana harar su Zaidu da suka ƙanƙame ledojin.
Cikin ƴar dariyar shaƙiyanci Musbahu yace, “Wanann kaɗan da ga aikin Master. Balle fa yau ango yake a gidan nan kuna ganin harda kazar tarbar amarya”.
A tare suka wage bakuna zasu ƙyalƙyale da dariya Idris yay musu nuni da sama. Saurin saka hannayensu sukai suka dafe bakunan kowa na ƙoƙarin danne ta shi. Da ga haka suka koma tsakkiyar falon zaune Salis na ƙoƙarin buɗe ledojin dake ɗauke da kwalayen pizza da shawarma.
Sosai suka shiga farin ciki kowa yaja shawarma ɗaya dan dama a lissafe suke. Pizza kuwa kwali huɗu ce itama.


Da ga ɓangaren oga Master kuwa koda ya haura sama a falo ya ajiye ledar ya nufi bedroom ɗinsa. Kusan mintuna goma sha biyar sai gashi ya fito. Ya sake ɗaukar ledar ya nufi ɗakin da ya kai Hibbah ɗazun. A yanda suka barta a haka ya isketa. Ya ajiye ledan a saman mirror fuskarsa na sake tsuƙewa. Ledar da Habib ya ajiye ɗazun ya ɗauka. Ya zaro handkerchief ɗin cikinta yana nufar gadon. Wata ƴar ƙwafa yayi dai-dai yana ranƙwafowa akan Hibbah da batasanma ya nai ba. Kansa tsaye ya ɗora handky ɗin saman hancinta. Tsahon minti ɗaya taja wani irin dogon numfashin da zai iya razanar da mai tsoro. Bai ɗaga handkerchief ɗin ba sai ma sake danna mata shi da yay akan hanci.
Numfashin ta kuma ja da ƙarfi tare da sakin tari lokaci guda. Ya janye hannunsa da jikinsa yana mikewa da ƙyau. Ganin yanda take jujjuya kanta da cigaba da tarin ya sashi ɗaukar goran ruwan da ya ajiye a bedsite tare da ɗora kafarsa ɗaya akan gadon ya sake ranƙwafowa kanta. Murfin gorar ruwan mai ɗan sanyi ya ɓalle ya shiga tsiyaya mata a saitin wuyanta duk da akwai hijjab a jikinta har yanzu dan basu cire mata ba. Yanda yake kwarara ruwanne ya sashi tsalle har saman fuskarta zuwa ƙirjinta da kan gadon.
Tai wata irin zabura da jawo numfashinta da ƙarfi ya iso har cikin hancinta. Duk da wani irin nauyi da jikinta yay mata hakan bai hanata ɗago hannunta ba ta shiga ƙoƙarin sharce ruwan da har yanzu yake kwarara matan.
Ɗayan hannunta ta kai cikin lalube da rashin ƙarfin jikinta da nufin ture ruwan da ke sakko matan. Sai dai hannun nata bai kai ba, sai kafarsa data ɗan shafo kaɗan ta ajiyesa yaraf tana ƙoƙarin son buɗe idanunta da sukai matuƙar nauyi.
Dakatawa yay da tsiyaya mata ruwan jin ta fara magana a fisge. “Y... y... ya... ya... Mu.... ham.... mad... kar... Kar...ku ɗaura zasu kashe ku”. Ta shiga faɗa a rarrabe cikin ƙoƙarin fisgar numfashi da yunƙurin son tashi. Sai dai kuma luuu ta koma yaraf bisa gadon dan sam babu wani ƙarfi tare da ita. Hasalima abin bai gama sakinta ba baki ɗaya.
Fahimtar hakan da yayi ne ya sakashi jan tsaki da cillar da goran ruwan yana sauke kafarsa ya miƙe tsaye sosai. Kallonsa ya kai ga agogon hannunsa yana sake tsuƙe fuska.
Tunanin mi yayi oho masa, sai kawai ya ja bargo aɗan fusace ya lullu ɓa mata, tare da sake ranƙwafowa ya kama hijjab ɗin jikinta yaja da ƙarfi ya farkesa. jansa yay baya ya fita da ga wuyanta. Da ga haka ya ɗauka ledan da ya shigo da ita ya fice ransa fal takaici.
Bedroom ɗinsa ya wuce, duk da yana jiyo hayaniyar yaran nasa da ke cigaba da kallon ball da ciye-ciyen abinda ya kawo musun suna zabga gardamar da sukafi ƙwarewa akai.


★★★★


Su Ummi sun isa katafaren sabon gidan da su Yaya Muhammad sukai matukar ƙoƙari wajen ginasa. Dan babu abinda su Hajiya Mardiyya ke ambato sai masha ALLAH. Ƙwarai da gaske matasan samarin na Ummi sun nuna ƙwazon da za'a yaba musu ƙwarai da gaske. Dan komai yayi cif a talauce ba'a sarauce ba. Sashen Ammar ne kawai ba'a karasa ba daga linta aka barsa.
Kai tsaye sashen Ummi da ke a farko suka shiga. Inda nanma dai su Hajiya Nafisa keta sakama yaran albarka dan komai yayi a asashen tamkar bana dattijuwa Ummi ba. Akwai ɗakin Ammar da na Hibbah a sashen Ummin. Sai bedroom ɗinta dana baƙi guda biyu. Ga babban falukanta biyu da kitchen da dining babba da ke ɗauke da dogon dining table na family baki ɗaya. A kallo ma zaka san sashen Ummin yafi kowanne sashe girma a gidan, sai dai nasu kawai upstairs ne su kuma. Itama kuma catai bataso shiyyasa akai mata nata flat da ya kayatu da zamani.
Suna shirin fara gabatar da salloli dan mazan sun fice sai ga kuloli ana shigowa da su. Cikin mamaki Ummi ke tambayar da ga ina?. Matasan samari biyu da ke shigo da kulolin suka bata amsa kai tsaye da faɗin. Isma'il ne ya turosu.
Rasama mi Ummi zatace akan wannan yaro ɗan albarka tayi, sai kawai ta saki murmushi zuciyarta na ƙara jin matukar ƙaunarsa har cikin jini............✍





*_Amin afuwa da jina shiru. Ciwo me ya kadani a bazata._*






TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*








*_Typing📲_*








*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*


https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS




*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*


https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw




_________________________




*_Chapter Twenty Four_*


............Kusan karfe tara na dare amare suka fara isowa. Sheikh Aliyu Abdul-Ra'uff Maina ne ya fara isowa da tawagarsa. A bisa al'adarsa na kai duk ƴaƴansa gidan aurensu kuma. Ba wani gayya bace yayo. Mota uku ce kawai ta ƴan uwansa mata sai ɗaya mazan ƴan uwansa sai ɗaya shi da Amarya Maimunatu da ke jikinsa tana faman kukan rabuwa da gida tamkar kowacce amaryar ƙwarai.
Ya fara damƙata a hannun Ummi matsayin uwa kafin ya damkama Yaya Muhammad da musu addu'ar zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba, harma da sauran angunan da amarensu. Da ga haka yay musu sallama ya taho ransa fal kewar ɗiyarsa data kasance ta ƙarshe a cikin ƴaƴansa da ya aurar.
Tamkar jira suna barin ƙofar gidan gayyar abokan su yaya Umar ƴan ɗaukar sauran amaren uku suka iso anguwar suma. Dama su su Yaya Umar ɗin duk suna nan gida basuje ba. Suna can gefe sun kulle kansu suna tattauna batun Hibbah dan sam hankalinsu baya a kwance. Yaya Abubakar ma tun ɗazun baya gidan da alama shima dai duk akan Hibbah ɗinne.
Sosai gidan ya kacame da hayaniya. Suma sauran amare duk sai da aka kawosu sashen Ummi aka damƙasu gareta kafin a mimmiƙasu sashen su. Waɗanda bazasu kwana ba suka firfito domin a maidasu. Aka bar masu kwanan nan da ƙawayen amare.
Hayaniyar mutane yasa Ummi bata maida hankali akan rashin ganin Hibbah da akace tana tare da su Zahidah ba. Gaba ɗaya hankalinta ya ɗauke. Har takai gidan ya koma tsit batasan kai kawo da ƙulle-ƙullen da ƴaƴanta keta faman yiba akan autar tasu.


★★★★


A can gidan ɓangaren su Abba kam dole aka kwashi Junaid zuwa asibiti, yayinda ran Abba ke a ɓace a jagule matuƙa. Babu abinda zuciyarsa ke kitsa masa sai ɗaukar alwashi kala-kala akan Ummi da zuci'arta. Musamman Hibbah da yakeji zai iya dasa wuƙa a maƙoshinta a halin da yake ciki. Dan tabbas kuwa yaga *ɗan hakkin da ka raina shike tsone maka idanu* har yaushe ma aka samu cikin Hibbah aka haifeta da zata iya ruguza masa shirinsa na tsahon shekara da shekaru?. Bama ita ba, hatta da Master ɗin ya ɗauki alwashin bazai bari ba. Dan da'alama Hibbah da su Ummi ɗinne suka sashi wargaza zancen auren.
Irin waɗan nan tunane-tunanen yaketa faman yi da kaikawo a ɗakinsa tun barin su momy da Junaid zuwa asibiti. Sai hayaniyar ƴan biki da har yau suketa gutsiri tsoma yake faman jiyowa. Wayarsa ya ɗauka ya shiga neman number A.G amma sai taƙi shiga saboda network. Cike da haushi ya wurgata saman gadon yana dafe kai. Tsabar ruɗanin da yake ciki ko salla baiyi ba gaba ɗaya yinin yau. Babu azhar, la'asar, magrib balle isha'i. Bai kumayi tunanin yinsu ba har dare ya raba ya cigaba da ƙullawa da kwancewa batare da ya samo wata mafitaba akan al'amarin.


Da ga wajen amare kuwa su Amlah kuka sunsha shi har sun godema ALLAH. Su kansu babu irin kalar tsinuwa da zagin da basu rakito sun sauke akan Ummi ba. Ga ƙawayensu na tayasu da tunzurawa. Tashin hankalin dukan da Isma'il yayma Junaid ne ya ɗauke hankalinsu zuwa can suma sukabi su Momy asibiti dan suna tsananin son ɗan uwan nasu ɗaya namiji tilo a cikinsu.
To har dai gari yay tsit alamar rabawar dare babu wanda ya dawo da ga asibitin. Hakama sauran ƴan biki babu wanda ya farga da rashin su Ummi balle tunanin rashin kawo amare har yanzun.


*_WASHE GARI_*


Sassanyar iskar sanyin asuba, da sabo da tashi sallar asubar ne ya saka Hibbah farkawa da ga nannauyan barcin da ya dunƙule rayuwarta tun daren jiya bayan master ya maidota hankalinta da ga sumarwa. Da ƙyar ta iya buɗe idanun da sukai mata matuƙar nauyi. Ta kai hannu bisa kanta da ya sara mata tana ambaton, “Wash ALLAH Ummi kaina”.
Jin shiru babu alamar Ummi a kusa da ita ya sakata ƙoƙarin ganin ta tashi duk da azabar da kan nata ke mata ga jiri-jiri hajijiya-hajijiya na ɗibar idanunta da taketa kokawar ganin ta buɗesu ko kaɗanne.
Da ƙyar ta iya tashi zaunen cikin lalube ta jingina jikinta da fuskar gadon. Tsahon mintuna kusan goma taja a zaune haka duk da kuwa kunnuwanta na jiyo mata salla a mabanbanta masallatan da takejin tamkar bana anguwarsu ba. Sai da yanayin nata ya ɗan dai-daita ta sake shiga kokawar buɗe idanun tana ambaton sunayen ALLAH.
Dishi-dishi take ganin ɗakin da ya kasance baƙo a gareta, har ganin nata yaɗan dai-daita. (Tabbas wannan ba ɗakinta bane, ba kuma ɗakin Umminta bane, to inane?) ta ayyana a zuciyarta tana sake bin ɗakin da kallo cikin ƙarfin hali. (Sabon gidan mu) zuciyarta ta sake ayyano mata duk da bataji gamsuwa ba a cikin ranta.
Kokawar son tunano abinda ya faru jiya ta shigayi da zuciyarta. Cikin amincin ALLAH kuwa komai ya shiga dawo mata dalla-dalla. Ƙirjinta yay wata azabar bugawa ta zabura da niyyar dira a gadon sai dai rashin ƙarfin jiki ya dakatar da ita ga hakan. “Innalillahi wa-inna'ilairraji'un inane nan? Wanene na shiga motarsa?”.
Ta faɗa a fili jikinta na rawa. Sakkowa tai a gadon cikin dabara, tai ƙoƙarin kunna wutar ɗakin mai haske. A take kuwa ko ina ya gauraye kasancewar akwai wutar. Da bin bango ta nufi ƙofar data gani, sai dai koda ta murza a kulle take. A take wani tsoro ya sake dirar mata a rai. ta zame a hankali tai ƙasa zuciyarta na wani irin tsitstsinkewa. (Idan har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login