Showing 21001 words to 24000 words out of 165076 words

Chapter 8 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74002

ɗin. Tana ƙyalla ido a kansu ta kwasa da gudu garesu. Jikin Yaya Abubakar dake gaba ta faɗa tare da fashewa da kuka.
Shima rungumeta yay yana mai rintse idanunsa da suka kaɗa sukai jajur. Yaya Muhammad ya ƙaraso garesu da sassarfa shima. Dafa kanta da yayine ya sata barin jikin Yaya Abubakar ta rungumeshi shima. Cikin son danne nasa ɓacin ran ya saki murmushi yana ɗagota da shafa kanta. Hannu yasa ya shiga share mata hawaye. “Kukan ya isa haka nan, ba gamu tare da ke ba”. Ya ƙare maganar da sake sakar mata murmushi mai kwantar da hankali.
Yaya Abubakar da shima ke ƙoƙarin ganin ya shanye tasa da muwar ya ce, “Bara naje zanyi magana da su”.
Da sauri Hibbah ta riƙo hannunsa tana girgiza kanta. Cikin sanyin da basu santa da shi ba ta ce, “Yaya karka je. Ka barsu kawai babu abinda sukai min”.
“Karki damu, ba wani abu bane yanzu zan fito”. Yay maganar da zare hannunsa cikin nata yana shafa kanta. Kama hannunta Yaya Muhammad yay shima ya buɗe mota ya sakata, tare da ɗaukar goran ruwa ya miƙa mata. “Sha ruwa ki wanke fuskarki ina zuwa”.
Hibbah na ƙoƙarin dakatar da shi bai jira cewarta ba ya nufi cikin station ɗin shima. Jitai kamar ta fasa ihu, dan gani take kamar shigar tasu na nufi jami'an zasu riƙesu su sanarma duniyar ƴan ta'adda ɗinne su.
Ganin an shafe kusan mintuna a shirin tai yunƙurin bin bayansu, sai dai tana buɗe motar suna fitowa kowannensu ransa a ɓace. Ta sauke ajiyar zuciya da yin sagade tai tana kallonsu har suka ƙaraso. Yaya Muhammad ya sake kama hannunta ya sata a motar sannan ya zagaya ya shiga shima. Yayinda Yaya Abubakar ya zauna mazaunin driver.

Suna fara tafiya kiran Ammar ya shigo wayar Yaya Muhammad. Kamar bazai ɗaga ba sai kuma ya ɗaga ɗin. Da ga can Ammar ya fara magana cikin ɗacin murya. “Yaya kazo gida dan ALLAH akwai matsala. Hajiya mama da Abba na nan sun taru akan Ummi harda Junaid. Nayi magana kuma ta dakatar dani. Wlhy zanma Haƙilu (Abba) dukan mutuwa sai dai Ummi ta tsinemin. Har wannan shegiyar tsohuwar ba raga mata zanba dan mahaifina ta haifa ba ni ba.”
“Ammar!!”
Yaya Muhammad ya kirayi sunansa a tsawace jin zai yanke kiran shima jikinsa na matuƙar rawar ɓacin rai.
Tuni Ammar ya riga ya katse kiran baima jisa ba. Yaya Abubakar da duk yaji komai ya ƙara ƙarfin gudun motar, cikin ƙanƙanin lokaci sai gasu a ƙofar gidan. Tun a waje yay fakin, gaba ɗayansu suka fita da sauri zuwa ciki. Dan tun da ga waje suna jiyo kururuwa da ihun Hajiya Mama da Momy.
A harmutse suka iske gidan. Ammar da Junaid na kwasar uban dambe. Sai dai duk da kasancewar Junaid yaya ga Ammar hakan bai hana Ammar hayewa saman ruwan cikinsa yana duka ba tamkar ALLAH ya aikosa. Mahaifiyar Ammar ɗin da suke kira Momy taje ceton ɗanta Ammar ya bata mahangurɓa a muƙamuƙi. Tuni ta koma gefe jikinta na matuƙar rawa.
Abba da hajiya mama kuwa tuni suna a wani lungu maƙale dan su ne Ammar ya fara fafara Junaid ɗin ya maresa. Shine faɗan ya juye a tsakaninsu. Da ga cikin lungun Hajiya Mama keta fama kwaɗa ihu da kururuwar Ammar zai kashe mata jika. Yayinda Abba ke a rikice ga tsoro, yana son zuwa ɗakko waya ya kira ƴan sanda yana tsoron fita Ammar da ya juye musu kamar wani mayunwacin zaki ya gansa ya dawo kansa.
Ummi ce kawai akan Ammar tana ƙoƙarin janyesa tana kuka amma ta kasa, dan gaba ɗaya ya juye mata tamkar ba Ammar ɗinta ba. Ya koma ainahin sunansa na ALIYU ZAKI.

Kuka Hibba ta fashe da shi ganin yanda Yaya Ammar kema Junaid dukan mutuwa. Sai jini ke fita ta hancinsa da baki amma yaƙi sakinsa. Da ƙyar Yaya Muhammad da Yaya Abubakar suka iya haɗuwa wajen ɗagasa da ga kan Junaid ɗin. A hakanma sai famar turjewa yake yana nuna Junaid cikin gargaɗi.
“Duk iskanci da kukejin kun iya da rashin mutunci muma mun iyasa. Ba tsoronku bane yasa muke barinku kuna taka mana mahaifiya yanda kuka gadama. Son yin biyayya a gareta da ga taka mana birkin da take na barinku kawai ke dakatar damu. Amma idan har kun isa wani ya sake nuna nata ɗan yatsa a gidan nan ya gani in ban karya shi ba na tauna ƙashin. Wlhy hatta waccan annamimiyar tsohuwar bazan bari ba, sai na ida ƙille ƙafafun nata ta koma gurguwa ta gaske.......”
Kuka sosai Ummi keyi tana kiran sunan Ammar amma yaƙi yin shiru. Su Yaya Muhammad suka turashi sashen nasu da ƙyar suma rayukansu duk a jagule.
A dai-dai wannan lokacin ɗaya da ga cikin ƴammatan gidan ta dawo. Horn tayi mai ƙarfi kamar yanda suka saba. Da sauri mai-gadi dake maƙale yana kallon duk abinda ke faruwa da ga windown ɗakinsa shima ya fito domin buɗe mata gate ɗin. Sai dai shima har cikin ransa yaji matuƙar daɗin dukan nan da Ammar yayma Junaid. Dan duk wani cin zarfi da akema mahaifiyar su Ammar ɗin a gidan akan idonsu ne tun da ƙuruciya.
A guje Ameera ta danno motarta cikin gidan kamar yanda ta saba. Sai dai hango su Abba akan Junaid da ke kwance kamar ya mutu ya sata saurin taka birki tamkar ba'a cikin gida ta ke ba. Fitowa tai da sauri. Ta zaro idanu sosai cikin ƙaraji na rashin tarbiyya take tambayar miya samu Junaid ɗin?.
Abba yay saurin ɗago Junaid ɗin da numfashinsa ke fita da ƙyar yana faɗin, “Kinga maza buɗe mana motarki mu kaisa asibiti shine mafi muhimmanci yanzu. Sauran bayani ƙyaji da ga baya dan anzo gabar da yaƙin duniya na uku zai fara tashi a gidan nan.”
Zata ƙara magana Hajiya mama ta katseta a tsawace. Baki ta murguɗa mata da yin fari da idanu sannan ta nufi motar tata Abba da mai-gadi biye da ita ɗauke da Junaid da gaba ɗaya jini yayma fuskarsa faca-faca...........✍






*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥












*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*





*_Typing📲_*






*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*


https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share


*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*


https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb


_________________________

*_Ina miƙa sakon ta'aziyya ga ɗaukacin musulmi musamman hausawa na rashin uba kuma jigo, Haziƙi, gwarzo, abin alfaharinmu Sheikh Dr Ahmad bamba. Ya rabbi ka gafarta masa. Ka yafe masa kurakuransa da iyayenmu baki ɗaya. Munyi rashi irin wanda cike gurbinsa abune mai matuƙar wahala a duniyar musulinci. ALLAH ka yafema wannan jarumin dattijan ƙwarai😭🙏🏻_*


__________________________


*_MG's SKINCARE_*


*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻


*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*


*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻


*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*


*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*


*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*


_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.


Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift




_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_




________________________






*_Chapter Ten_*


...........Ummi na shigowa falon ta wankama Ammar mari. Lokaci guda falon ya ɗauki tsitt. Hibbah ta zazzaro manyan idanunta waje, jikinta na rawa, dan abinda bai taɓa faruwa ba a tsawon sanin da taima Umminsu. Duk iya ɓacin ran da zata nuna idan sukai mata laifi iyakarta da su faɗa da nasiha tun basu kai haka ba.
Ba Hibbah kawai ba, hatta Yaya Muhammad da Yaya Abubakar sai da wutar kansu ta ɗauke. Hakama Yaya Umar da Yaya Usman da ke ƙoƙarin shigowa falon saboda kiransu da mai-gadi yayi ya sanar musu abinda ke faruwa tun sanda Ammar ke jibgar Junaid. Sai dai suna shigowa gidan motar Ameera na fita zuwa asibiti kai Junaid. Tare kuma suka tafi gaba ɗaya gidan, har da Hajiya mama dake fama da ƙafarta.
Ƙananun duka Ummi ta cigaba da kaima Ammar, hawaye masu zafi suna gangaro mata a kumatu. Ammar dake tsaye ƙiƙam tun marinsa da tai kallonta kawai yakeyi shima hawayen na sakko masa na tausayinta. Yayinda wani murmushi mai ɗaci ke bayyana saman fuskarsa. Ummi ta jawosa ta rungume jikinta tana magana cikin rawar murya, “Miyasa zakai haka Aliyu? Miyasa? Ba nace duk abinda zaku gani ba kuyi kamar baku gani ba.”
Da gudu Hibbah ta zo ta rungume Ummin da Yaya Ammar itama. Gefe Yaya Muhammad ya kauda kansa yana ƙoƙarin ɗauke hawayen da suka ciko idanunsa. Yaya Abubakar ma idanunsa sun kaɗa sunyi jajur. Yaya Umar yafi kowa zuciya a cikinsu, yayinda Yaya Usman duk ya fisu sanyi shi da Yaya Muhammad. A wani irin fusace ya juya zai fita a falon Yaya Usman da yasan halin kayansa yay azamar riƙo hannunsa.
“Sake ni!”
Ya faɗa cikin kaushin muryar da ya maido hankalin kowa kansu. Girgiza masa kai Usman ya shiga yi alamar bazai barsa ba. Dan yasan dama badan Ummi da ke dakatar da su ba babu shakka da tuni Umar yayma Abba dukan mutuwa a gidan harma da Hajiya mamar kanta... Da ƙarfi Yaya Umar ya fisgi hannunsa da ga cikin na Usman. Hakan yasa Ummi azamar sakin Ammar tasha gabansa.
Cikin idonsa ta kalla batare da tace masa komai ba. A take yay ƙasa da kansa yana lumshe idanu da cije leɓensa da ƙarfi tamkar zai huda shi. Murmushi tayi tana kamo hannunsa cikin nata. Gaba ɗaya ƴaƴanta tasan lagonsu da hanyar sauke fushinsu. Shiyyasa a kowane lokaci take samun nasarar ladabtar da kowa cikin salon da ya dace. Babu wanda ta sake yima magana a cikinsu, sai kamo hannun Hibbah dake sharar hawaye har yanzu tai tana bin jikinta da kallo tamkar mai neman wani abu.
Da sauri Hibbah ta ce, “Ummi basuyimin komaiba fa, babu abinda ya faru ki kwantar da hankalinki”.
“Ai sun sakaki a tarkon da za'ayi miki ne!”.
Yaya Abubakar ya faɗa a tsawace cikin faɗan da kowa baisan yana da shi ba. Dan shima bai cika hayaniya ba sosai, amma yafi Usman da Muhammad zafi a wasu lokutan.
Ya riƙe ƙugunsa da hanunsa ɗaya, ɗayan yana murza goshinsa cike da damuwa. Yanda ya ke ɗan kaikawo yasa su fahintar akwai matsala kenan. Ummi da dama yin komai ta ke cike da ƙarfin hali ta kafesa da ido.
Zaune Yaya Abubakar ya kai saboda jin zai faɗi, dan shi kaɗai yasan a wane irin damuwa ya ke game da halin da Hibbah ta ke ciki. Gaba ɗaya ƙuruciya ta hanata fahimtar ramin da ta jefa kanta a ciki mai haɗari ne.........
“Abubakar mike faruwa?”
Ummi ta katsesa tana takowa gabansa. Idanunsa da ke jajir ya ɗago yana kallonta, ya ɗan furzar da zazzafar iska yana girgiza kansa. “Ummi tabbas akwai matsala, rawar kanta ta kaita ga jefamu cikin ramin da sam ita bazata fahimci haɗarinsa ba....”
Duk da hibbah a tsorace take da yanayin Yaya Abubakar ɗin, tai saurin katsesa ta hanyar faɗin, “Yayanmu wlhy babu abinda ya faru fa. Kawai dai sun sakani na bibiyar musu masu power bike ɗin nan dana sanar maka ne. Amma da ga haka basuyi min koma.........”
Tsawar da ta sakata kasa ƙarasa zancen ya daka mata. Ta maƙale a jikin bango jikinta na rawa saboda bata taɓa gamo da fushinsa irin haka ba. Shima tsaye ya miƙe yana nunata jikinsa har rawa yake ga idanunsa sunyi jajur. “Idan bakimin shiru ba wlhy sai na ɓallaki a gidan nan yau. Bance miki ki jirani a inda kike nazo na sameki ba? Su masu power rider ɗin da kike tunanin ba komai ba to sune tawagar ɓarawon nan da ake nema ruwa a jallo mai suna *Master!*, shine ya wawashi maƙudan kuɗaɗe jiya a asusun matar gwamna. Kowace hukuma ta jami'an tsaron jiharnan an basu awa ashirin da huɗu ne domin kawosa a mace ko a raye. Ba jihar nan da ƙasarnan kawai ba, hatta duniya baki ɗaya idonsu akan wannan mutumin yake. Amma shine k kika jefa kanki cikin abinda bakisan mafarinsa ba. Su waɗan nan jami'an da suka ɗaukeki zasuyi amfani da ke ne kawai su sami cikar burinsu, sunansu ya sake fiwowa a idon duniya. Kece zakiyi aikin amma sune zasu fito matsayin masu aikin. A tunaninki shi ɗin mahaukaci ne, kosu suna son matsalar tasa ta ƙare ne da wuri? Kuɗaɗen shigar da suke samu su dakata. Kafin yau an sha yimasa tarkuna da sukafi wannan haɗari amma bai kamu ba. Da ga ƙarshe kuma duk wanda yay masa tarkon ana nemansa ne a rasa ma baki ɗaya, ya ɓatar da shi. Wannan yasa a duk lokacin da ya aikata laifin manyan ke makalewa su saka ƙananun ma'aikata yin aikin, da ga ƙarshe suke nuna sunyi aikin ma duniya, wanda yay aikin kuma rayuwarsa ta faɗa a haɗarin da babu wanda zai sakejin yanda akayi, kuma basa wani ɗaukar matakin bashi kariya ko cetosa. Shekarunki goma sha takwas kacal da wasu wattani a duniya Muhibbat! Bama ki gama karatun gina rayuwar taki ba amma kika jefa kanki a wannan haɗarin saboda kunnen ƙashinki. Wannn kunnen babu wanda ya isa ya faɗa masa yaji sa”.
Ya ƙare maganar da takawa inda take maƙure a bango jikinta na rawa ya damƙi kunnenta da ƙarfi yana murzawa cikin yatsun hannunsa. Rawa jikinta ya farayi tana girgiza masa kanta saboda zafi.
Sakin kunnen nata yay yana dungure mata kai, yayinda sauran yayun nata da Ummi keta faman ambaton (innalillahi wa-inna ilaihirraji'un) a zukatansu. Yaya Abubakar ya cigaba da faɗin, “Ba wanann kaɗai bace damuwar Ummi, tunda har basu sami nasarar kamashi ba zargi zasu ɗarsa akanta itama. Dan zasu raba hankalinsu ne yanzu akan tunanin ko shine ya shirya komai wajen yin amfani da ita. Dan duk harin da jami'an tsaro ke kai masa ba'a taɓa cin nasara kamar nata ba da ya gudana cikin kanƙanin lokaci. Yanzu da zarar sun fitar da bayanai wa media cewar sun haresa, harin da kuma aka samu ci gaba a cikinsa fiye da na baya, to kowacce hukumar jami'an tsaro sai sun bibiyi yanda hakan ta kasance ta karƙashin ƙasa, walau jami'anmu nan gida kona ƙetare da ke nanuke cikin case ɗin kamar yanda suka saba mana kutse a cikin ayyukan daya shafi ƙasashenmu. Mu kuma bamu isa muyi koda tari akan nasu ba. A ƙarshe kowa ya bincika ita zai gano. Duk kuma zasu kasance wajen bibiyarta da mu kammu ba tsira zamuyi ba. Shima da ta aikata komai dominsa ba barinta zaiyi ba na sani.
“Ya ALLAH!”.
Ummi da ke neman faɗuwa ta faɗa tana fashewa da kuka. Da sauri sukai kanta gaba ɗaya suna ƙwala mata kira. A wani irin sarƙe numfashinta ya fara fita, ta fara tari.
Rikicewa suka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login