Showing 126001 words to 129000 words out of 165076 words

Chapter 43 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74008

Haka kawai kallon da salon nasa ya saka tsigar jikin Hibbah tashi. Babu shiri tai azamar amsar kofin shayin tana maida kanta ƙasa ta duƙar. Shima ɗauke kansa yay ya maida ga aikin da ke gabansa. Lokaci-lokaci yana amsa wayar da ita kanta batasan da su wanene ba dan maganar ma a cuɗe suke yinta.
“Ciwonka ya daina zafi?”.
Ta faɗa cikin suɓutar baki daboda idonta daya sauka akan ƙafarsa dake harɗe ɗaya kan ɗaya tamkar wani jinin sarauta.
Duk da ya jita bai tanka ba. Hakan yasata ɗago ido ta ɗan dubesa. Ganin gaba ɗaya hankalinsa nakan system ɗin tai tunanin baiji ba, sai ta sake maimaitawa.
“Kin damu da ni har haka?”.
Ya faɗa batare da ya kalleta ba. Fuska ta ɓata, tare da kumbura baki ta cigaba da shan shayinta. “Daga tambaya”.
Kallonta ya ɗanyi ya ɗauke kansa. Yanda tai maganar kamar zatai kuka ne yaso bashi dariya. Amma sai ya gimtse abarsa yamaki cewa komai. Itama bata sake cewar ba harta kammala ta ajiye kofin zata miƙe. “A ina baba Saude take zanje wajenta”.
“Aiki zakimin nima anan”. Ya fa ɗa yana nuna mata gefensa. A marairaice ta ce, “Zanfa gaisheta ne”.
Maimakon ya bata amsa sai ya ɗakko lap-top da ke gefensa kalar pitch ya miƙa mata fuskarsa sam babu alamar wasa. Maganarsa ta dazun da yace mata rashin haƙurinta ya hanata zuwa wajen su Ummi ne ya sata zama a inda ya nuna matan. Koda ta kunna sai taci karo da hoton yayunta a screen ɗin harda yaya Isma'il. Babu shiri ta saki tattausan murmushi tana dubansa. “Nagode sosai ALLAH ya shiryeka kabar ƙwamushe kuɗaɗen mutane”.
Harara ya zabga mata yana sake tsuƙe fuska. A zuciyarsa kuwa kokawa yake da dariyar dake taho masa yana mamakin shegen kauɗinta. Wato tsoron jiya harya barta ta dawo normal. “Idan kikai wasa yau babu accaunt ɗin dazai kwana da ko naira acikin yayunki har Isma'il ɗin naki ma”.
“Wayyo, dan ALLAH kayi haƙuri wlhy wasa nake maka fa. Ai kaima kaga yanzu ka zama ɗan uwanmu ko”.
Hararar ta ya sakeyi ya ɗauke kansa. Itama sai bata sake magana ba ta ɗauke kanta tana murmushi. Dan idan yay harara ita dariya yake bata. Sai da ta kammala dai-daita komai sannan ta dubesa. “Mizanyi to?”.
Batare da yayi magana ba ya jawo takardun gefensa ya miƙa mata, sai kuma ya ɗan matso har jikinsu na haɗuwa. matsawa ta ɗanyi kaɗan, komai baiceba ya fara nuna mata abinda zatayi.
“Ni dai dan ALLAH karka sakani satar kuɗ...”
Bata ƙarasa ba yasa yatsa ya ɗalli laɓɓanta. “Idan wannan baki bai daina damuna ba sai na cinyesa ALLAH”.
Hannu tasa ta dafe bakin hawaye na ciko idanunta dan taji zafi. Shiko ya ɗauke kansa da cigaba da nuna mata ɗin kamar bai ganta ba. Sam ta manta da gargaɗinsa, yana gama faɗa cikin marairaicewa ta sake faɗin, “ALLAH bana son cutar kow.....”
Tai saurin sake dafe bakin batare data ƙarasaba ganin yanda ya juyo. Kanta ta shiga girgiza masa idanunta na cika da ƙwalla. Lap-top ɗin da ke akan cinyarsa ya ajiye tare da juyowa gaba ɗaya. Babu shiri ta miƙe zumbur tana ajiye tata gefe tare da takardun zata gudu yasa ƙafa ya harɗota. Gaba ɗayanta ta faɗa saman cinyarsa. Ya cije baki saboda ciwonsa. Cikin daburcewa ta shiga son tashi a jikin nasa tana faɗin. “Dan ALLAH kayi haƙuri ALLAH bazan sake ba”.
Bakin da ke maganar ya zubama lumsassun idanunsa da ke cike da mura. Sai yatsun hannunsa da ya tallafo ƙugunta har zuwa saman cikinta da yake ɗan motsawa. Zata sake yunƙurawa ta tashi ya sake nutsa hannunsa a saman cikinta dole ta koma ta sake zama tamkar zatai kuka. Kunyar duniya ta baibayeta tamkar zata halaka ta. Narkakken kallon da yake mata ya sata kai hannu zata rufe idonta dan rumtsewar ma ji take kamar bazai hanata ganin idanun nasa dake da matuƙar kaifi a gareta ba. Tana gab da kaisa saman fuskar tata ya riƙe. Da ƙarfi ta matse idanun da sake shagwaɓe fuska. “Nace fa kayi haƙuri”.
Hannunta daya riƙo ya murza cikin nasa da wani salon da yasa jininta tsinkewa a lokaci guda. ya sake kusanto da fuskarsa gab da tata yana sake marairaice idanunsa “Ni idan akai min laifi sai na rama ai”.
Ya faɗa cikin wata irin murya data saka Hibbah buɗe idanu ta kallesa babu shiri. Ganin fuskarsa gab da tata tai saurin sake maida idanun ta rumtse tana motsa baki alamar maganace a ciki babu damar faɗa. Fuskar tasa ya sake kusantawa da tata yana busa mata numfashinsa. Ji take tamkar ta fasa kuka dan yanayine da bata taɓa fuskanta ba a rayuwarta na kusanci da namiji irin haka. Tana ƙoƙarin buɗe idonta da son roƙonsa taji saukar laɓɓansa saman nata a bazata. Wata irin zaburar data bashi damar sake nutsata cikin ƙirjinsa ya rungume tayi. Tsabar rikicewar datai bama tasan ta saƙalo hanunta a wuyansa ba tana mintsini. Wata zazzafar ajiyar zuciya yaja yana sake narkewa bugun zuciyarsa na ƙara ƙarfi dan shima wannan shine karon farko a rayuwarsa daya tsinci kansa a irin wannan yanayin mai wahalar fassara da mantawa, daga shi har ita jikinsu rawa yakeyi, duk yanda yaso ganin yay control ɗin kansa ya barta ya kasa, sai ma sake ƙaimi yakeyi da canja salon tafiyar tasu zuwa wani abu daban.
Firgici ya saka Hibbah fara jujjuya kanta hawaye na zirara, duk mintsinin da take masa baisa yajita ba balle ta samu kubutar da take fata da ga garesa, sai ma yazam tamkar ƙara masa ƙaimi take da mintsinin.
Samun damar ɗaura hannunta da tai saman ciwonsa ta ɗan danna ya sashi janye jikinsa yana jan wani bahagon numfashi. Ba ƙaramin shiga tai cikin matsanancin firgici ba ganin yanda gaba ɗaya kamanninsa suka sauya mata lokaci ƙanƙani. Tai ƙoƙarin fisge jikinta da son tashi ya sake riƙota. “Na roƙeka dan ALLAH ka bari banaso, ka tausaya min karka ci amanata. Inason na cikama mahaifiyata burinta na tun farko akan auren Yaya Isma'i......”
Ruf ya sake rufe mata bakin batare data ƙarasa ba. A Kokawar son ƙwatar kanta da take cikin rawar jiki da firgici ne ta samu damar ɗayo mask ɗin face nashi, cikin zafin nama ya kai hannu domin hanata da ƙoƙarin jan kansa baya aka samu matsala ta zareta baki ɗaya, real face ɗinsa ta Isma'il ta bayyana kanta gareta............✍


_______________________


Hi team no makeup
Ina kanawa mutanena🗣️
Shin Ina masoyan mg's ina ma'abota ado da kwalliya kusaurara kuji dame nazomuku 💃
Nasan dayawa kunsiya kayanmu Kuma kunshaida yadda suke gyaranjiki cikin lokaci kalilan Koda iyasabulun kikayi anfani dashi sekinyaba balle kankat wato beauty kit dinmu toh inamaitabbatar muku cewa ynx kayanmu ankaramasu kayayyaki Wanda zasu Kara gyara fata fiye da tsammanin Mai tunani within 2weeks zakicanza kiga duk inda kikayi se anbiki d👀 domin ynd fatanki zaikoma Shar kamar madara bawanda zemiki kallo daya yadauke idanunshi😃😍
Hajiyata shin menene matsalanki, pimples ne?
Spot? sunburn,acne, stretch marks, knuckle, wrinkles, Black head,ko kinshafa Maine yabatamiki jiki
Inamai shaidamiki cewa ynx ne lokacin dayakamata kiyake dukkan wadannan kema kidinga fita sakayau abunki baruwanki da kunshe fuska ko kice sekinyi makeup hjy fita zar abunki kinuna ainihin natural beauty dinki😍domin kayanmu gbdynsu organic ne babuna bleaching zssu sa ki haskaka fatarki tayi ta kyalli kamar madubi ze fiddomiki d ainihin natural beauty dinki ne😘kunaji barin fadamuku wani Abu billah wannan prdcts damuke dashi ynx Koda kudinki seda rabanki domin duk sunzarce nabaya ankaramasu abubuwa dayawa masu matukar anfani agyaran fata🤗Ina Wanda basasan shafa Mai koda sabulun kawai kike anfani dashi inamai tabbatar Miki zkg ynd jikinki zekoma luwai luwai😘
Soap:3k
Beauty kit:12k
Chat:08062991549
07066210195
Call :07046881166
08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
amare inakara shaidamuku duk wacce tayi anfani d kayanmu Bata bukatar gyaranjiki sedai ra'ayi🥰
Masoya kunanan kauna yanda nakwashe aljihu domin nafarantamuku kuyi achieving goal dinku pls Nima kunanan kauna kufarantamin😪🤠aljihuna yafarfado hilis karnakoma kauyenmu🥲
Yar shawarmannan duk nasaba😤 hilis kugarzayo arabani da kaya🤝
Nd guest what🤩
Duk Wanda yy siya 10k zuwa sama zesamu Karin gift😃
Pamper your skin🧖‍♀️
Shine like a bride👰🏻
Glow🧚🏻‍♀️.


_________________________




TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*








*_Chapter Thirty Nine_*


...........Duk da ba sanin mitake tattaunawa da zuciyarta yayi ba yaji a ransa yau ƙila har ALLAH ya isa sai tai masa. Tama nutsu ta tabbatar da shiɗin Isma'ill ɗinne ko wanine daban hakan ya gagara saboda rashin man kanta. Komai bai iya yace ba, yasa bargon kawai ya share mata hawayen da har yanzu sun kasa tsayawan. Wayarsa ya sake ɗauka dai-dai shigowar sabon saƙo. Yasan Abdull ne dan haka bai tsaya ɓata lokaci ba ya buɗe saƙon. Duk da dai sai da Abdull ɗin ya gama masa sheri irin nasa ya rubuto masa dukkan abinda ya buƙata baibi takansa ba. Kwantar da kanta yay bisa filo a ransa yanajin haushin ya akaima baiyi tunanin yin duk hakan ba, duk da dai ba fitowa fili yay wajen gayama Abdull ɗin ba, shegen bin ƙwanƙoninsu ne kawai irin na likitoci zaisa ya fahimta. Toilet ɗin ya sake komawa yay duk yanda ya rubuto masa sannan ya dawo wajen Hibbah.
Da ƙyar ya samu ta tashi tana faman masa raki. Nokewar farko da tai saboda babu kaya a jikinta ya sashi ɗaukar rigarsa dake gefe ya saka mata. Koda ya mikar da ita azaba ta sata faɗa masa jiki ta fashe da kuka.
Kansa ya ɗan girgiza da ɗaukarta dukanta kawai dan shi kansa wajen hutawar yake bukata. Ga tausayinta fal ransa dan shi bayason ganin mutum a damuwa dalilin sa. A banɗakin ma ba tsira yayiba. dan harda cizo ya sake sha. Ummi da su Yaya Abubakar kam sunsha kira matuƙa. Da ƙyar ya samu ya taimaka mata tayi yanda Abdull ɗin ya rubuto masa. Koda ya tambayeta batun wanka bata tankaba. Dan dama tunda suka shigo bata yarda tako kalli yatsan hannunsa ba idonta a rufe suke. Sai da yaja mata gargaɗi a kausashe sannan tayi, shi ya sake taimaka mata suka fito. Ya zaunar da ita a gefen gadon yasa karamin towel ya rage mata ruwan kanta. Gudun kar lokacin salla ya cigaba da shigewa ya sashi ɗakko mata wata doguwar rigan a kanyan da batasan a ina ya samoba. Shiya taimaka mata ta saka nan ma. Ya saka mata hijjab ɗin da faɗin, “Tashi kiyi salla”.
Wani irin bugawa ƙirjinta yayi a karo na biyu, saboda jin da muryar da yay magana sak na yaya Isma'il. Sai dai ta dake matuƙa na hana kanta dubansa ta tada sallan cikin layin rashin ƙwarin jiki har yanzu tana hawayen. Sauƙinta ma ta ɗanji daɗin taimakon ruwan zafin da yay mata duk da sai da ya haɗa da mazurai.
Sallar ma dai haka tayita harta kammala tana kuka. Yayinda shi kuma yake kimtsa gadon cikin mamakin abinda ya ci karo da shi. Bai daice komai ba ya naɗe zanin gadon ya hau duba wani a ɗakin kozai samu. Sai dai babu. Dole ya fito zuwa ɗayan ɗakin dake a sashen. Zanin gadon dake ajiye na gadon ɗakin ya dauka ya koma. Da kansa ya shinfiɗa cike da karfin hali. Gamawar tasa tayi dai-dai da kammalawar Hibbah sai dai ta kasa tashi a wajen.
Duk da ya fahimci ta idar baiyi magana ba. sai ma zama da yay a bakin gadon ta gefen ta yana latsa waya. Massege ya turama Habib akan ya kawo masa abinci ya ajiye a falo. Wayar ya ajiye yana maida hankalinsa gareta. “Kin idar?”.
Kanta kawai ta jinjina masa tana share hawayen da suka ziraro mata. Duk da ya fahimci kukan take baice komai ba ya miƙe ya fita a ɗakin. Yasha mamakin iske abincin da yasa Habib ɗin ya kawo harma da wanda baiceba. Dan harda magunguna a leda. Tambarin jikin ledar maganin ne ya sashi shan jinin jikinsa. A fili ya furta “Abdull”. Aljihun wandonsa ya ɗan laluba domin cirar wayar sai ya tuna ya barta a bedroom. Dan haka ya ɗauka abincin kawai ya koma. A inda ya barta anan ya sameta, sai dai yanzu ma ta sake haɗe kai da gwiwa.
Komai baice mata ba har sai da ya haɗa mata abincin, cikin dakewarsa, dan ya fahimci lallaɓawar bazatai masaba, Hibbah bahaguwar mutumce kuma zuma ce sai da wuta. yace, “Tashi kici abinci”.
Ɗagowa tai, dan muryarsa kawai razanata takeyi a halin yanzun. batare da ta yarda ta kallesa ba cikin rawar muryar kuka tace, “Na ƙoshi, dan ALLAH ka kaini wajen Ummi na, inason na ganta”.
Maimakon ya amsa mata sai ya miƙa mata kofin tea kawai. Ganin taƙi amsa, tamaƙi ɗagowa ta dubesa ya kamo hannunta ya ɗaura kan kofin. “Baki gaji ba kenan mu koma a ƙara”.
Da dauri ta amshi kifin jin abinda yace, yay gajeren murmushi yana ɗauke kansa daga kallonta. Uziri ke garesa na fita, gashi babu dama baima san yanda zaiyi da ita ba. Tsoro da yunwar da takeji ga zazzaɓi yasata shanye tea ɗin akan lokaci ta ajiye kofin, komai baiceba anan ma ya ɗauka ledar maganin ya duba. Ƴar takardar da yaci karo da ita a cikin maganin ya warware ya fara karantawa. Yanda duk za'a sha maganin ne a ciki, sai ƴar tsokanar da yay masa a ƙasa wadda ta sashi sake tabbatar da zarginsa akan Abdull ɗin yana kusa da shi. Ajiyewa yay ya ciri maganin ya bama Hibbah. Babu musu ta amsa ta sha.
“Wai nikam baza'a kalleni ba?”.
Yay maganar yana ƙoƙarin ɗago haɓarta ganin taƙi yarda koda kuskure ta dubesa. Idanunta ta rumtse hawaye suka ziraro. “Kuka dai, kuka dai babu hutu?. Bakisan yanzu ke kin girma ba ne? Kin tashi da ga autar Ummi, shalelen su yaya Muhammad. Nanda ƙanƙanin lokaci za'a fara kiranki Mamy insha ALLAH ”.
Sake fashewa tai da kukan tana ture masa hannu da juya kanta gefe, sai hakan ya bashi dariya. Amma yay ƙoƙarin gimtsewa da faɗin. “ALLAH ya baki haƙuri tashi muje ki kwanta”. Yay maganar Yana miƙar da ita. Koda ya kwantar da ita a saman gadon shima sai ya kwanta a gefenta tare da ɗan ranƙwafowa yay mata runfa da jikinsa. Hannu yasa yana share hawayen da take zirarwa har yanzun. “Bana son kukan nan Muhibbat, kinga yana ƙara miki zazzaɓi da ciwon kai, yaya Isma'il yayi laifi. amma a yafe masa shalelen Yaya Ammar....”
Cikin dasashshiyar muryarta ta katsesa da faɗin, “ALLAH ya kiyaye, kai ba Yaya Isma'il bane. Gara ma ka daina wannan ɓoye-ɓoyen fuskar da yaudarar mutane kana jefa rayuwarsu a haɗari kai kazo ka kwana lafiya”.
Murmushi kawai yayi batare da ya amsata ba da sumbatar laɓɓanta ya rungumeta a jikinsa dan kansa ciwo yake masa. Tun tana jan ajiyar zuciyar kukan da take har barci ɓarawo ya saceta. Shima dai barcin ke son ɗibarsa saboda maganin da yasha. Cikin ƙanƙanin lokaci duk suka tafi duniyar barcin.


Barci sukai sosai har magrib ma ta ɗan gota. kiran wayarsa da akai ne ya farkar da shi harda ma Hibbah, sai dai ita tayi luf bata nuna ta tashin ba harya janyeta a jikinsa ya ɗauka wayar. “Barka da yamma sir”.
Ya faɗa cikin muryar barci lokacin da yake kai wayar saman kunnensa. Jin abinda wanda ya kira sir ɗin ya faɗa da ga can ya sashi miƙewa da sauri yana kallon agogon ɗakin. Kansa ya ɗan dafe ganin yanda lokacin yaja sosai harma anyi magrib. “I'm sorry sir kaina ke ciwo na ɗan kwanta ne bansan lokaci yaja ba haka”.
Amsar da aka sake bashi da ga can ta ɗan sakashi sakin ɓoyayyen murmushi da faɗin, “No sir insha ALLAH yanzun nan zan iso ɗin ka jirani, dan ina son baka gaba ɗaya bayanan kawai kafin na ida tattara sauran gobe idan ALLAH ya kaimu.”
Idanu Hibbah da maganganun nasa suka bama mamaki ta ɗan buɗe

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login