Showing 102001 words to 105000 words out of 165076 words

Chapter 35 - TAKUN SAKA COMPLETE DOCUMENT Romantic Book.txt

05 Nov 2024

74042

mata hawayen gefe guda yana cigaba da kallon fuskar tata. Ɗayan hannun kuma ya karasa fincike murfin goran ruwan ya kai bakinta. Abinda ya tokare maƙoshinta ne ya sata fara shan ruwan ko zai wuce. Tasha kusan kaso ɗaya bisa uku kafin ta janye kanta. Komai baice mataba ya janye shima tare da mikewa. Ya kai hannu ya kamo nata hanun. Dole ta miƙe tsaye dan kulawar daya batan kawai yasa zuciyarta ɗan yin sanyi taji kamar daya da ga cikin su Yaya Abubakar ne.
A doguwar kujera ya kaita ya zaunar. Hannun nata ya saki ya nufi hanyar bedroom ɗinsa. Hibbah ta bisa da kallo zuciyarta na ayyano mata wata kamanceceniya data rasa a ina take son gano ta. Ta yi zurfi a tunani barci ya fara fisgar jijiyoyin idonta. Duk yanda taso hana kanta hakan ya gagara. Cikin kanƙanin lokaci jikinta duk ya saki, dole ta zame ta kwanta a kujerar batare data shiryama hakan ba.
Duk abinda take yana kallonta ta cikin ƙofa. Yana ganin ta zube kwance ya fito. Wata Wadrobe dake a gefe an shirya littatafai a ciki ya nufa. Key ya ɗauka a kasan wani littafi ya saka jikin kwabar sai ga shi ya buɗe alamar ƙofa. Yasa hannu ya juya katakon ƙofa ta bayyana. Dawowa yay ya leƙa kasa. Ya tabbatar baba saude hankalinta baya a wajen sanann ya ɗauka Hibbah gaba dayanta yabi ta ƙofar da tai ƙasa yabi ta barauniyar hanyar data fiddashi ta backyard ɗin gidan. Da sauri Habib da ke tsaye cikin parking space ya buɗe masa ƙofar motar. A bayan ya sata, shima ya shiga. Habib ya zauna a mazaunin driver suka fice a gidan bayan maigadi ya wangale musu gate.............✍




*_Kuyi haƙuri, yau gaba ɗaya na ɗauka Sunday ce ashe monday muke🥲🙏🏻🙌🏻_*








TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*


*_NAJI DADI SHINE GARI......_*


*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*


_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_


*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*


*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*


*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*


*SABBIN LABARAI*


*SABUWAR SHEKARA*


*SABON NISHADI*


*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*


*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*


*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.


*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_


*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_


*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_


*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_


*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*


6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*


09134848107


Littafi daya


1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).


*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽


#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥










*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*






*_Typing📲_*








*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*




*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*


https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS




*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*


https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw


_________________________


*_Chapter Thirty Two_*


..........A ɗan firgice Hibba ta farka da ga gajeran barcin da Master ya sakata na dole. Waige-waige ta shigayi cikin ruɗanin ganinta a sabon waje. Yayinda wani irin tsoro da tsantsar firgici ke bayyana akan fuskarta. “Na shiga uku wa kuma ya kawoni nan?”.
Ta faɗa muryarta na rawa alamar son yin kuka........
“Hi aunty queen!”.
Da sauri ta juyo tana kallon Habib mai maganar da maɗaukakin mamaki, sai kuma ta ɗan sauke ajiyar zuciya koba komai taga wanda ta sani, duk da suma ɗin ba wai abin yarda bane.
“Barka da yamma aunty queen”. Aka sake faɗa ta ɗayan gefenta. Khalid ne yay maganar dan haka ta ɗan hararesa. Ta buɗe baki zatai magana Master ya fito ta wata ƙofa waya manne a kunnensa. Ga kofin baƙin shayi a hannunsa. Baiko kalli kowa a cikinsu ba ya kai zaune bisa kujerar dake kallonsu yana ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya.
Yayinda yake amsa wayar cikin rashin sakewa da ƙasaita. Hararar gefen ido Hibbah tai masa tana gulmarsa a cikin rai. Ta dubi su Habib da suka nutsu a tsaye. “Ni ku bani abinci yunwa nakeji aka satoni nan”.
Cikin gumtse dariya Khalid yace, “Mi zaki ci to?”.
“Komai ma”.
Barin wajen yayi. Babu jimawa sai gashi ya dawo da damammiyar madara da kwalin cornflakes. Yaja ƙaramin stool gabanta yana faɗin, “Gashi auntynmu”.
Komai batace ba. Sai dai babu musu ta zuba cornflakes ɗin batare data kalli inda Master yake ba, har zata kai baki kuma sai ta dakata. Ta ɗan saci kallonsa tana faɗin, “Khalid inji dai ba'a saka ka barbaɗa wani abun mutuwa ba ko?”.
Idanu ya ɗan waro waje. “Abin mutuwa kuma Aunty Queen? Wazai saka miki abin mutuwa?”.
“To na sani, tunda agabana ranar akace a bani maganin feshin ƙwari nasha”.
Habib da Khalid suka dubi juna suna satar kallon Master daya gama wayar yana daƙilarta ne kawai alamar akwai abinda yakeyi, duk da yana jinsu yayi kamar baisan dasu a wajen ba. Cikin danne abinda ke taso musu Khalid yace, “A'a babu abinda aka saka miki aunty. D......”
“Zaku wuce abinda ke gabanku ne? Ko zaku zauna surutu?”.
Ya faɗa batare da ya ɗago ya dubesu ba. Kafinma ya rufe baki sun bar wajen. Hibbah ta taɓe baki da cigaba da shan cornflakes nata dan yunwar takeji da gaske. Cigaba da abinda yakeyi yayi harta kammala bai dubeta ba. Sai da ta mike tana ɗan dafe kai ne ya bita da kallo.
“Ina ne kitchen?”.
Ta tambaya cikin kwantar da murya dan ita tayi alƙawarin daina tsiwa har sai ta gano wanene shi.
Da yatsa ya nuna mata yana miƙewa. Ficewa yay da ga falon yana sake ɗaura wayar a kunnemsa alamar wani kiran yayi. Gaba Hibbah tai itama inda ya nuna mata. Bata wani jima ba ta fito tana gyara hijjab ɗin jikinta da batasan ta yanda akai ta sakashi ba, balle inda ta samoshi. Sake komawa tai kan doguwar kujerar ta kwanta ranta fal tunanin dalilin da yasa aka kawota nan ɗin kuma?. Harga ALLAH hatsabibancinsa na bata mamaki. Mutum ne da sam baka taɓa gane ina ya dosa balle manufarsa. A ɗan zaman da tai da su sosai ta fahimci wasu halaye na mutanen kirki tattare da shi. Sai hakan ke yawan raba mata hankali daga ɗabi'unsa na zahiri da kowa ya sani. (Zan dai sake nutsuwa na fahimci guy ɗin nan).
Ta ayyana a zuciyarta cikin yarda da kai. Cigaba tai da tunane-tunanenta har ta fara jiyo hayaniyar su Adam da batasan ta ina suka fita ba. Jin hayaniyar tasu na cigaba da tashi sama-sama ya sata miƙewa dan zaman shirun baya mata daɗi, ga jikinta duk babu ƙarfi kanta kuma na mata ciwo kaɗan-kaɗan. Ta riga ta saba da baba Saude acan da Sharifat. Duk da ba sanin ko'ina tai ba haka ta fito compound inda take jiyosu. Girman gidan ya bata matuƙar mamaki, an wadatashi kuma da abubuwa kai kace ba a cikin gurguwar ƙasarnan tamu bane ba.
Tsaye tai tana kallon su Habib da ke faman buga basket ball. Haka kawai taji wani nishaɗi har fuskarta na bayyana murmushi. Ta shagala sosai a kallonsu ta hango wata ƙyaƙyƙyawar mage na fitowa da ga ɗakin maigadi. Tana son mage, tsoronta da yaya Usman keyi a gida ya saka Ummi ta hanata ajiyewa. Magen ta nufa tana faɗin, “Woow Cutie”. Tai maganar tana kaiwa duƙe ta ɗauka magen.
Master da ke kallonta da ga can inda yake ta gaban ruwan da aka ƙawata na swimming pool ya ɗan yamutse fuska ganin ta ɗaga magen ta rungume a jikinta tana murmushi tamkar ta samu ɗa. Sam shi bai wani damu da mage ba amma ba tsoronta yake ba, baya son dai sam ta taɓa masa jiki. Ɗauke kansa yay ya cigaba da danna wayarsa.
Hibbah ba lura da Master tayi ba, dan haka ta cigaba da hidimarta da mage cikin nishaɗi. Lokaci-lokaci takan ɗaga kai ta kalli su Salis. Wani ɗan zare ta ɗauka tana ɗagawa sama magen na tsalle zata kamo. Hakan yasaka Hibbah ƙyalƙyalewa da dariya tana tafiya da baya-baya magen na binta da son kama zaren.
Tana gab da isa inda Master yake Idris ya farga. Zungurin Musbahu da ke kusa da shi yayi. Musbahu ya ɗan waro ido dan ganin abinda ke shirin faruwa. Yay saurin ɗaga hannu zai fargar da Hibbah da ke gab da zuwa inda Master yake Idris ya rufe masa baki.
“Kai malam waye ya saka. Barta dan ALLAH, wlhy ni so nake babban yaya ya amsheta matsayin matar gaske bawai ta wucin gadi ba. Dan sun matuƙar dacewa.”
Musbahu da ya gamsu da bayanin Idris ya jinjina kansa yana janye hannunsa. “Ashe bani kaɗai nake da fatan nan ba.”
“Sosai kuwa”
Cewar Idris cikin bada tabbaci.
A ɓangaren Hibbah kam gab take da kaiwa ga Master da gaba ɗaya hankalinsa nakan wayar dan abu mai muhimmanci yakeyi a ciki. Khalid da sai yanzu idanunsa ya kai shima ya ɗan zaro ido. Da sauri ya ɗaga mata hannu da faɗin, “Aunty Queen bayanki”.
Tsorata Hibbah tayi, dan duk zatonta wani abun cutarwa ne, musamman ganin yanda Khalid ɗin yayi maganar. Tai ƙoƙarin juyawa da sauri sai dai ta rigada tazo gab da shi, ga magen ta ɗane ƙafarta saboda kama zaren da tasamu damar yi. Uban tsalle ta doka da ƴar ƙarar tsoratan data fargar da Master. Cikin zafin nama ya riƙo hannunta ganin tayi baya zata kai ƙasa, sai ko gata gaba ɗaya a kansa.
Hawar masa ƙafa da magen tayi ne shima ya sakashi saurin ɗaga ƙafarsa, ga Hibbah ɗare-ɗare a cinyarsa. Yanda yayi ɗinne kuma ya sake firgitata ta duƙunƙunesa gaba ɗaya har yana sakin wayarsa a ƙasa babu shiri. Cikin sauri su Idris suka shiga jan hannun juna suna barin wajen ransu fari tas..
Master ya sake rumtse idanunsa da ƙarfi jin yanda Hibbah keta sake cusa kanta a ƙirjinsa da dabaibayesa. Ga mage da kamar ance ta nane musu sai tsale-tsallenta take. Dole ya miƙe gaba ɗayansa dan bayason magen na taɓa masa jiki. Hibbah ta fasa ƙara da son sake ruƙosa jin zata faɗi ƙasa, sai dai abisa tsautsayi ta riga tayi baya da yawa, idan kuma takai ƙasa tabbas zata cutu. Magen ya yakice a jikinsa yana ƙoƙarin kai ɗayan hannunsa ya riƙo nata ganin gaba ɗayanta zata sulmiya cikin ruwan ne.
Maimakon ta riƙe hannun sai ta damƙe rigarsa gaba ɗayansu suka antaya a cikin ruwan ji kake tanjamm😬😱.

Yanda ruwan ya bada ƙara yasa su Habib fitowa kusan duk a guje sukayo wajen pool ɗin har maigadi. Sam Master bai iya ruwa ba. Hasalima bai cika son ganin babban ruwa ba, kona swimming pool ɗin idan ya zauna wajen saboda son sanyi baya yarda yay masa kallon daya haura sakanni yake ɗauke ido. Idanko damina tazo duk wani rashin jinsa nutsuwa yake saboda rashin sakewa, ko yaya ruwa ya dakesa sai yaji a jikinsa dan sai yayi ciwo.
Hankalin su Habib ya tashi saboda sanin bai iya ruwaba. Gashi basu da damar cewa zasu shiga ruwan saboda Hibbah dake tare da shi. Cikin ƙanƙanin lokaci Master ya shaƙi ruwa, sai dai kuma ƙoƙarin son ceto Hibbah yake a zatonsa bata iya ruwanba itama. Duk yanda yaso hakan ta kasance ya gagara, dan harya fara galabaita. Hibbah kuwa tanata ƙoƙarin ganin taje gaɓa dan itama dai bawai ta iya swimming ɗin bane ba, amma ta fisa dan ta kuɓutar da kanta batare data fita hayyacinta ba. Ruɗewar data lura su Zaidu sunyi ne ya sata saurin waigawa bayanta tana ƙoƙarin sharce ruwan fuskarta. Idanu ta zaro matuƙa, dan Master harya fara yin ƙasa.
Da sauri ta koma bayan inda yake. Tasa hannu ta toshe hancinta tai ƙasa wai zata ɗagosa. Ina yafi ƙarfinta, amma tsabar ƙarfin hali tanata kici-kici cikin rawar jiki na tsoro, dan ta fahimci bai iya ruwa ba. Da ƙyar ta samu da taimakon su Habib data miƙoma hannunsa suka kama ta ɗagoshi, sai faman cije baki take dan ya mata nauyi a jiki, tana turawa suna ja har suka ɗagosa gaba ɗaya.
Ganin kamar bashi da rai yasa Hibbah fashe musu da kuka, dan gaba ɗaya kanta ta bama laifin. Ruɗewar da tai yasata fara danna ƙirjinsa kamar yanda taga Musbahu nayi. Amma babu alamar ruwan daya shaƙa zai fita.
Adam yay saurin faɗin, “Aunty Queen taimakon gaggawa ta baki Please”.
Ruɗewa ta sakata ranƙwafawa kansa ta ɗaura bakinta kan nasa, yayinda ta toshe masa hanci da yatsunta biyu, bada wani tunani ba ta shiga bashi taimakon gaggawa. Ganin taja numfashinsa na farko babu wani alama yasata jawowa a karo na biyu da iya ƙarfinta tana matse ido.
Gaba dayansa ya yunƙuro saboda tahowar numfashinsa mai haɗe da tari da ruwan daya shaƙa. Hannayensa duk biyu sukai sama, tana ƙoƙarin dagowa ya sake rungumota ta dawo kan ƙirjinsa. Tsam ya matseta yana cigaba da tarin ruwan daya shaƙa na fita.
Nannauyar ajiyar zuciya su Khalid duka shiga saukewa na godiya ga ALLAH. dan da gaske sun shiga tashin hankali. Sai mutsu-mutsu Hibbah take nason ƙwace jikinta amma ta kasa koda motsi. Sai da tarin ya lafa masa ne ya ɗan janye hanun daya dabaibayeta yana buɗe idanu da ƙyar. Cikin sauri ta miƙe a kansa duk kunya da takaici sun dabaibayeta. Ya ɗan kalleta ya maida idanunsa da sukai jaa ya lumshe.
Ganin ya saki Hibbahr su Salis da duk sukai ƙasa da kai tunda ya kawo numfashi duk sukayo kansa. Sune suka taimaka masa ya tashi zaune. Zasu kamashi ya mike ya girgiza musu kai alamar zai iya. Baya duk sukaja. Shi kuma yabi Hibbah dake jike da ruwa ta nufi hanyar falo da sassarfa da kallo. Mikewa yay da ƙyar yana dafe kansa da ke juya masa. Shima ya nufi falon su Habib suka take masa baya sunata jera masa sannu. Har cikin ransu kuma ganin laifinsu suke dan sun bada gudunmawa a wannan accident ɗin.
A falon suka iske Hibbah sai rawar sanyi take har haƙoranta na haɗuwa. Duk tausayi ta basu, tayi tsumu-tsumu tamkar an tsamo ɓera a ruwa😹👐🏻. Shi kansa ta bashi tausayi, duk da bayajin ƙarfin nasa jikin shima gabanta ya ƙarasa. Babu zato Hibbah da duk kunya ta dabaibaye saboda yanda kayan suka manne mata a jiki sai ji kawai tai anyi sama da ita.
Da sauri ta harɗo hannayenta a wuyansa saboda wani Masifaffen kunya daya rufeta tashi a karo na farko tun zuwanta gidansa. Ta tura kanta akan ƙirjinsa da riga ta manne shima yanata ɗigar da ruwa.
Ƙin ɗagowa tai har sai da taji ya direta ta ɗan buɗe ido. Da sauri ta kalla inda ya kawotan shima ta kallesa. kafin ta ɗaga baki tai magana ya kammala dai-daita ruwan ɗumin ya saki ruwan shower ɗin ya sauka a kansu. Wani irin bahagon ajiyar zuciya Hibbah ta saki jin ruwan akansu. Ta rumtse idanunta da sauri tana juya masa baya ganin zai cire riga abinsa hankali kwance.
Juyawar tatace ta bashi damar cire duka kayan jikinsa ya bar boxer kawai ruwan na ratsa masa jiki kozai samu nutsuwar abinda yakeji na ƙutsa masa cikin ƙashi. Sai da yaji ya ɗan fara samun nutsuwa ne ya kashe gaba ɗaya, batare da yace komaiba yaja bathrobe ya saka. Tun kafin ya fita a toilet ɗin ya fara sakin atishawa a jajjere.
Ajiyar zuciya Hibbah ta kuma saki jin ya rufe mata ƙofar hawaye na gangaro mata. Gaba ɗaya kallon komai take tamkar a mafarki yau itace a banɗaki daya da namiji.
Jin sanyin na neman dawo mata a jikine ya sata zuwa ta sama ƙofar key ta fara zame nata kayan. Dan dole ne idan tana bukatar zaman lafiya tayi yanda ruwan zai ratsata ta kuma rabu da kayan gaba ɗaya. Hatta da gashin kanta ji take kamar ta kwashe ta yar.
Sai da taji tamkar fatarta zata ɗaye dan saukar ruwan dumin nan sannan ta kashe tana sauke numfashi da atishawa itama. Towel ya rage a toilet ɗin gashi guntu, bata da zaɓin daya wuce ɗauka ta sakama jikinta, ta sake jan karami ta naɗe kanta tana sakin atishawa da kallon facemask ɗin daya cire a fuskarsa. mask ɗin ta ɗauka tana jin takaicin kanta na juyawar da tai da tabbas saita ga face nashi yau. Jin atishawa zata halakata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login