Showing 33001 words to 36000 words out of 108352 words
Chapter 12 - Alkawarin Zuciya by M Shakur Complet .txt
taji takasaci jikinta yamata wani irin sanyi kodan ita kadai ke yin breakfast dinne oho, tashi tayi tawuce sama tana kallon su Manaf da still ke bacci ta shiga dakinta dan shiryawa.
Shiryawa tayi tsaf cikin wani black abaya mai bala’in kyau tai rolling gyalen akanta ko kadan batai kwalliya ba but she looks kaman wata Somalian queen, jakanta tadauka sanan tafito, dakin Mama tabude takalli Baba dake karatu har lokacin tace “Baba natafi” saida ya idasa Ayan sanan yadago kudi yaciro yamika mata karba tayi tana murmushi tace “thank u Baba, kacema Mama natafi idan ta tashi bye” murmushi Baba yayi yace “to yarinyar Mama” maida kofan tayi tarufe yasauke ijiyan zuciya Noo yagaji Khairy deserve to know Maman ta is sick, he’s tired of hiding it from her, bari Maryam ta tashi zai gayamata is time sufadi ma Khairy, Khairy is grown up she can handle it.
Fitowa tsakar gida tayi tana tafiya ahankali hakanan jikinta kawai yamata sanyi yasaki tarasa mesa kawai she’s feeling sad and week ma yanzun nan, karasawa wajen motanta tayi Adamu na shiga itama tana shiga baya daidai sunajin horn mai gadinsu na budewa, motar Baffan ne ke shigowa gidan Hafiz ke tuki, sai motar Ammi biyeda su da driver ke parking sai kuma motan Mom, bude kofan motar tayi tafito tana murmushi da saurin ta tai wajen motan Baffa, daidai lokacin Baffa na bude baya yana fitowa yana mata murmushi yace “yan makarantan bokoko” dariya tadanyi tace “Baffa ina kwana, Ya Hafiz Baban Baby ina kwana, Laaaa Ya Hassan da Ya Hussain harda ku akazo yau” kafinma suyi magana Baba yace “wuce tafi school karki latti” yanuna mata motarta da Adamu yatada yana jiranta shiga motan tayi tana waving Mom dake saukowa daga motanta dan har yanzu motan Ammi bama abude ba kuma bamata iya ganin cikin banda driver shima ta glass din gaba taganshi dan motan tinted ne, jan motan Adamu yayi suka tafi nai gadi yamaida gate din gidan yarufe daidai lokacin Baba da Manaf suka fito.
Ahankali aka bude kofar motar Ammi, wani clean white kafane ya sauko dake sanye cikin wani hadadden sandals na Prada black, nails na kumban kafan are so fresh and white, gently yakarasa saukowa daga cikin motan yana yatsine fuska yana gyara bakin sun glasses na idanunshi na kampanin rayban, yana sanye cikin milk color yadi dayay dinkin jumper dashi daya bala’in amsan jikinshi, yanada tsayi dan wajen gabaki dayansu yafisu tsawo babu wanda baya ganin kanshi, yanada cika dakuma fadin kirji, kana ganinshi kaga Ammi kaman tai kaki ta tofar saisa yafi kannenshi kyau dansu Hafiz da Baffa suke kaman, yanada wani irin black very very dark saje dake kyalli kaman na bature, lips dinshi is so pinkish, gashin kanshi a kwance suna shinning, hannunshi ya daura agogo Rolex akai, ita kanta Ammi anytime ta kalleshi she feels proud da Allah yabata Zayn as her son, Zayn is definition na handsome guy, kyakkyawan namiji da babu macen data isa tamai yanga, ganin Baba yataho wajensu yasa ahankali yakai hannunshi yazare eye glasses na idanunshi yadan sunnar da kanshi kasa Baba nazuwa cikeda mamaki yakama hannun Baffa yace “d’ana Zayn nake gani haka” murmushi daga Baffa har Ammi da Mom sukayi, Baffa yace “da asuban nan yashigo gida” anatse Zayn yace “ina kwana Abba”? Hannu Baba yabashi ahankali yasa nashi hannun cikin na Baba, daidai sukaji muryan Maheer yana ihu. “Babaaa” Dawani irin sauri Baba yasaki hannun Zayn yay ciki Baffa da kowama suka bishi sama sukayi, dakin Mama Baba yashiga yatarar da Mu’az yarike Mama dake aman jini sosai tai lakur babu karfi kodaya ajikinta, wajenta Baba yayi yakamata daga hannun Mu’az yadau tissue yana share mata bakin ganin tadena aman, shigowa dakin Mom tayi takalli Baba tace “Alhaji bari mu chanza mata kaya” girgiza kai Mama tayi ahankali tana rike Baba gam batare datai magana ba, kallonta yayi sanan yakalli Mom yace “abarshi tukunna” karasowa gaban gadon Baffa yayi yaja kujera yazauna yana kallon Mama dabata iya bude idanunta da kyau yace “Maryam mutafi asibiti”? Girgizamai kai tayi ahankali, ajiyan zuciya yasauke yay shiru, shigowa ciki Ammi itama tayi tasami gefen gadon tazauna ahankali tana kallon Mama murya chan kasa tace “kina bukatan wani abu Maryam mezaki ci?” Girgizama Ammi kai tayi hakan yasa itama tai shiru, ahankali Baffa yajuya yakalli Zayn daya tsaya chak abakin kofa shima yana kallon Mama sanan Baffa yajuyo da kanshi ya kalli Mama yace “Maryam ga Zayn dakika ce nakira miki yazo” dan yunkurowa kadan tayi da duka karfinta, dasauri Baffa ganin haka yasa yace “Zayn come” karasowa gaban gadon Zayn yayi ahankali sanan gently ya tsugunnawa gaban gadon yana kallon Mama dake kallonshi kallon dakasan baa hayyacinta takeba yace “Mama I am here” hannunta daya tacire daga jikin Baba data rikeshi gam gam jin haka yasa Baba yatayata , kama hannun Zayn tayi hawaye yazubomata daga idanunta sanan kadan tabude bakinta dasauri Zayn da zuciyanshi ta katse yace “Mama I am here mekike so tell me” yakai kunenshi saitin bakinta, magana tashigamai a kunne wanda harta Baba dayake rikeda ita baiji abinda ta Fadima Zayn ba sanan takoma jikin Baba ta kankame shi, Maheer dataga yana kuka sosai mara sauti abakin kofan ta kalla hannu tamikamai ahankali yataso yazo kawai kankameta yayi yahau kuka sosai ahankali yace “Mama dan Allah kiwarke, Mama please karki mutu kibarmu” motsi sosai bakin Mama yafara hakan yasa Baba ya janye Maheer daga jikinta kankame Baba tasake yi takama hannunshi tarike gam gam kaman dats the only thing dake mata dadi sanan cikin wata kalan murya dabata fita da kyau dan hakoranta sun datse tace “Baffa, Ammi, Mom, dukanku yarana ina rokonku gafara ku yafeni idan nataba bata muku, idan Ummulkhair…..” wani kalan nishi tayi tana kuka sosai dabayama fitowa sosai tace “kuce mata nace tayakuri tayafema Maman ta, i hide everything sabida nasan idanda tasan banda lpy bazata dauki abin da kyau ba, Baban Manaf” tai maganan tana kankame Baba tace “ka kulamin da Khairy dan Allah, Baffa nabaku amanan Khairy da duka yarana, Khairy is fragile, and innocent please ku rikemin yarinyata amana ita nafiji araina, zanbar duniyan nan amman Khairy ce araina sabida ita kadaice diyata mace yayyinta maza ne” ajiyan zuciya Mama tasake saukewa sanan ahankali tace “idan narasu Khairy taki kwantar da hankalinta kabata Littafin nan danabaka ka ijiye mata Baban Manaf” gyadamata kai Baba yayi ahankali hawaye na taruwa a idanunshi Baffa ya bubbugamai kafa alamun karyay kuka, ahankali Mama tace “Baffa kamishi aure dazaran na rasu banson yarana su rasa uwa, Manaf kurike Matar da mahaifinku zai aura kaman ni kada kubata ciwon kai” gyadamata kai Manaf yayi, Ammi kallon Mu’az yayi dake bakin kofa tayi ya tsugunna idanunshi sunyi jajir tace “zo wajen mahaifiyar ka Mu’az” mikewa yayi tsaye da kyar shigowa yayi zuwa wajen gadon kawai yadaura kanshi kan gado yadaura hannunshi kan nata dan that’s what Maheer da Manaf duk sukayi, yanda tazo tana nishi yasa Baffa ya gyadama Baba kai ahankali Baba yasoma karanto mata kalman shahada, saukar da kanshi kasa Zayn yayi, ahankali Mama ta amshi kalman shahadan karfe 12:03 daidai tacika da imani daidai lokacin Khairy ta tashi daga kan kujera sun gama lectures zasu fita jitayi kafafunta sunyi sanyi kawai tai baya zata fadi kaman tai paralyze Rabi dake bayanta ta tareta tace “ke Khairy are u okay” ? rike Rabi tayi tana taba kirjinta tace “gabana fadi yakeyi sosai kafana ba karfi” zaunar da ita Rabi tayi tace “kinyi breakfast kuwa”? Girgiza kai tayi hakan yasa Rabi da sauran kawayenta sukai dariya tace “yunwa ce muje kici abUinci”.
[6/16, 7:56 PM] +234 701 275 3212: 2️⃣5️⃣
Almost good 10min na silent ne yacika dakin, at this point Baba jiyayi kaman shima yamutum ne dan he could feel yanda hannayenta suka sassandare ajikinshi kasa koda motsi yayi hakan yasa Baffa yay taking over, daga Baba tsaye yayi, ahankali Baba yasauke kanshi kasa yana kallonta in disbelief, yadade ahaka sanan yakai hannunshi ya kulle mata idanu kafin yaja bargon yarufeta saikawai yazauna akasa dabas baimasan mema zaiyi ba dan he’s still in shock idan ya kalli su Manaf daduk suke kuka saiyaji zuciyanshi yakara tsinkewa, kafadanshi Baffa yakama ya matsa hakan yasa ya fuzar da iska kafin ahankali yasa hannunshi yakamo su Manaf daya bayan daya duka yarikesu ajikinshi kam kam, juyawa Baffa yayi yakalli Hafiz dashima yay mutuwan zaune hakama su Hassan ahankali yace “Hafiz jeka dauko Khairy daga makaranta”
Tashi Hafiz yayi ahankali yafice daga dakin tafiya yake but jiyake kaman iska ke kadashi yana tuna all memories dinshi da Mama shikenan daba danta data haifa ba balle kuma yaranta yaya zasuji.
A famfon gaban flower ya tsaya saida ya wanke fuskanshi tass sanan yakarasa wajen mota shiga yayi yatada motan yana kallon yanda mai gadi ke budemai gate he just wish yanada karfin sanar da su, amman ina motarshi yaja yafita daga gidan zuwa school din su Khairy, har gaban department dinsu yaje accounting yay parking yakai kusan good 20min zaune acikin motan baida courage na facing Khairy, da kyar ya iya gyara mood dinshi sanan yakashe motan yafito yamaida yarufe yana kallon ko’ina kafin ya shiga ciki, Khairy nabashi labarin how popular she is a school so yasan ganinta bazai tabamai wahala ba, wasu yammata guda uku dasuka sauko daga bene yatare yace “hello ladies dan Allah kunga Khairy” daya daga cikinsu ce tace “yanzun nan muka rabu da ita ga ajinsu chan wanchan floor din suna lectures” thanks yace musu sanan yawuce sama zuwa gaban class din excuse yay taking hakan yasa lecturer yafito dan yana ganinshi yasan Wanan baimai kala da dalibin makarantan nan ba, dawowa cikin ajin lecturer yayi yace “Ummulkhair” dasauri Khairy dake zaune ta kwantarda kanta kan table takalli lecturer tace “yes sir” waje yanuna mata yace “ana nemanki” tashi tayi ahankali tana daukan jakanta tafito tana tafiya kadan kadan dan sosai kafafunta basuda karfi ganin Ya Hafiz yasa tabude baki cikeda mamaki takarasa gabanshi da sauri tace “Ya Hafiz mekazo yi a school dinmu”? Hararan ko’ina yayi yay gaba abinshi tana binshi da sauri yace “me zanyi a school dinan naku Baffa yace nakawo ki” dasauri tace “Allah sarki Baffa yana ina tare kukazo kenan” “yana gida” yafadi kai tsaye batare daya juyo ya kalleta ba daidai suna karasa sauka kasa tana binshi abaya tace “Ya Hafiz wani laifin nayi ne wanan da dazu dasafen nan nabar Baffa agida mekuma nayi” juyowa yayi yakalleta daidai yabude mota yay murmushi yace “yarinya laifi dayawa” zare idanu tayi cikeda tsoro tace “hala saisa gabana keta faduwa wlh” tada motan yayi tashigo ganin duktai wani irin yasa yace “common babu abinda kikayi so relax” murmushi tayi dasauri tana sauke ijiyan zuciya but dudda haka she’s not just feeling ok hakan yasa tai shiru kaman ba itaba danda tacikashi da surutu shima shiru yamata baice mata komi ba ahaka har suka shigo layinsu, tundaga nesa take hango tulin mutane ata kofar gidansu maza na alwala hakan yasa ta gyara zama tace “Ya Hafiz maiya faru a anguwan mu”? Hango gate din gidansu abude awangale gakuma mutane yasa taji kawai gabanta nafaduwa ba kakkautawa, shiga cikin gidan sukayi daga baki baki Hafiz yay parking dan compund din yacika da mutane wasu tsaitsaye wasu zazzaune hango mai gadinsu da Adamu direbanta na kuka yasa kawai taji wani karfi yazo mata tawani bude kofan taduro juye juye tafara tana juwa juwa tanabin all mazan da idanunta kan sauka akansu tana kallo, kaman daga nesa taji dodon kunenta yaji wani magana. “Itace diyar Hajiyar data rasu” kafafunta da tun dazu sukai sanyi jitayi karfi yazo mata acikinsu kawai tahau gudu tai flat dinsu dataga kofar abude tashiga uwa an jefota tanabi kowa na falon da kallo matan anguwansu ne makotansu sunci mayafai some da charbi a hannu, stairs tayi dawani kalan mahaukacin gudu kawai neman mutum daya take dan gidansu she wants to know what’s happening idanunta ma sun rufe zuciyanta na bugawa batama ganin gabanta bum! Taji sunci karo da mutum da sauri takoma baya sanan tazaro idanunta tadaga kanta takalli wanda ke gabanta kaman yanda shima yake kallonta, batasan wayeshi ba but she could see kamannin shi da Ammi wani kayatyaccen kamshi nafitowa daga jikinshi, ahankali bakinta ke motsi numfashinta na neman gagaranta yi sabida yanda kirjinta ke bugawa ba kakkautawa ahankali tace “I……ina…….ina….”? Idanunta ne suka sauka kan gawar dataga an shimfide anan falon sama da aka suturta, sai yanzu ma talura da mutanen dake falon saman, Baffa, Baba, Ammi, Mom, Ya Manaf, Ya Mu’az, Maheer, Ya Hassan da Hussain Mama ce kadai batagani, still numfashinta na bala’in katsewa tabi idanun kowada kallo barinma Maheer dake kallonta yana wani irin kuka harda majina da she just think that answers her question, gently tadaga kafanta tana wani kalan kyafkyafta idanuwanta tana dambe da numfashinta dake kokarin daukewa tana kokarin tai taking just a step forward kawai tajita blank tai baya straight, wani irin tareta yayi dawani irin sauri Baffa yataso yana kallon Zayn daya tareta yace “Zayn kwantar da ita akasa she’s asmatic, Manaf get me her inhaler” dakinta Manaf yashiga yafito da sabon inhaler dago kanta Baffa yayi yadaura akan kafanshi yakai inhaler bakinta yana bubbuga kumatunta da kyar ta shaka tai wani irin nishi tadawo Baffa takalla tashi tayi zaune kaman bata hayyacinta tace “Baffa ina Mama na”? Ganin Baffa yay shiru yakasa bata amsa yasa takalli Ya Manaf tace “Ya Manaf ina mama ya akayi banganta ba” saukar da kanshi kasa yayi, ahankali Baffa yace “Ummulkhair” wani irin gyadamaikai tayi jikinta ko’ina na ta rirrike Baffa, all this while Baffa has been mai taurin zuciyan but for the first time yaji Khairy kaman itace zata karyashi, dakewa yayi yace “listen to me Khairy, kinaji” gyadamai kai tayi jikinta har kafafunta bari suke ta rirrike Baffa wani irin zufa na keto mata agoshi, anatse yace “dukanmu anan da mazajen dakika gani a waje ke kawai ake jira domin inaso kima mahaifiyarki addu’a, Ummulkhair inaso kizama yarinya mai Imani da kaddara mai kyau ko mara kyau sanan kisani cewa kullu nafsin za’ikatul maut, i want you to calm down don’t shout and don’t cry kinga kinada Asma karkije kima kanki illa, Ummulkhairy Allah yayiwa…..” Baffa yadanyi shiru ganin yanda tazaro ta kwalalo manyan idanunta waje kaman zasu fado kasa yanda jikinta ke rawa zaka dauka ajikin injin markade take, daurewa Baffa yayi ahankali yace “Allah yayiwa mahaifiyar ki, Maman ki rasuwa Ummulkhairy”.
[6/16, 7:56 PM] +234 701 275 3212: 2️⃣6️⃣
Wani kalan shuuuuu taji kunenta nayi, itadai tasan taji koke koke, taji maganan Baba, su Ya Mu’az har maganan Ammi tasan taji sama sama kafin chan kuma taga tabude idanunta tana kallon kowa dake kanta, kala batace musu ba rarrafe ta shigayi har zuwa gaban gawan zama tayi dirshan tana kallon farin likafanin hannu tamika zatakai tabude saikuma tai shiru kafin ahankali tasa hannunta taja likafanin kasa fuskan Mama ya bayyana tai wani haske ga alamun murmushi tanayi wani kuri tayi da idanu kaman tahaukace sai kawai idanunta aukahau mata yana kaman Mama murmushi take mata dariya tayi sanan tajuyo ta kalli Maheer dake kuka tace “Ya Maheer dena kuka kaji zoka gani ga Mama nan namin murmushi, Mama bata mutu ba bacci take wlh gashinan zoka gani” babu zuciyan wanda bai tsinkeba adakin ahankali takai bakinta saitin fuskan murya chan kasa tace “Mama Mama, world best tashi kiji, Mama ai bacci kikeyi ko” tasake shiru, ganin ko motsi Mama batayi yasa tai tagumi tana kallonMama tace “zan jira harsai kin tashi kinmin magana” ahankali Baba yataho yazauna kusada ita dasauri tajuyo takalleshi kaman mai karantan wani abu akan fuskanshi, kafadan Khairy yakamo sanan ahankali yace “Ummulkhairy mamanki has been bathling with cancer for so long, blood cancer bataso kisani cus tasan abinda zakiyi kenan idan kikaji she has few days left, u will not take it likely, saisa taboyemiki all this while mamanki has been sick, seriously sick amman taki yarda kisani duk ciwon da mamanki keyi taganki she will pretend she is fine” hawaye masu bala’in dumi ne suka zubo mata dasauri tasa hannu tashare, ahankali Baba yace “karki sakawa Maman ki hakan nan Khairy inhar she’s your world best, kimata addu’a tasan tabar ya tagari aduniyan nan muje mukaita makwancinta, your mum is tired she need rest, go and pray for your mum” ahankali Khairy tasake matsawa kusada Mama she can’t believe Mama ne nan kasa addu’an tayi sai kuka ahankali tace “Mama dan Allah dagaske wai kin rasu?”, zuwa yayyinta sukayi kawai rungumeta ahankali Manaf yace “Mama tarasu Khairy pray for her” Ahankali tace “Mama Allah yajikanki Allah ya gafarta miki, Mama why did u leave me, shikenan bazan kara ganin ki ba, Mama maisa baki bari na rokeki kiyafemin ba, kullum ina cikin batamiki rai inta rashin ji, Mama Tayaya zan cigaba da rayuwa baki aciki Mama Innalillahi wa Innailaihi raji’un” tashi Baba yayi ahankali hakama Baffa dasu Ya Hassan da Hafiz dakuma Zayn zasu dauki Mama dan kaita waje salla, wani Zabura tayi zata tashi dasauri Manaf yariketa, Mom yabama ita tana wani kalan nishi hannu Mom tasa takarbi inhaler ta tace “Khairy Khairy” kaman zata haukace haka takeji da kyar ta iya kallon Mom tace “Mom na shiga uku, Mom Mama tarasu Innalillahi wa innailaihi raji’un, Mom wlh wlh ko….” kawai maganan yakakare takara suma, ruwa Mom tashafa mata a fuska tanamata addu’a, tafarfado ta sume tai having Asma attack haka tadingayi ahaka har akama Mama salla aka tafi da ita, Khairy bamatasan inda kanta yakeba tana jikin Mom, jikinta yay wani mahaukacin zafi dayasa Mom takalli Ammi dake zaune tanajan charbi tace “Hajiya kira Alhaji Dr yazo jikinta yay zafi dayawa, kuma suman nan datakeyi yay yawa” dan jim Ammi tayi sanan tadauki wayanta takira Baffa ta sanar dashi.
Bayan magrib Baba yashigo gidan tareda Baffa gaisawa yayi da matan dake falo dakemai gaisuwa sanan suka taho sama tundaga stairs yake kallon Khairy dake kwance akasa gatanan gatanan ne kawai baa cewa komi, tsugunnawa Baba yayi agabanta ahankali yadagota sharaf ta taso Mom yakalla yace “tayi salla kuwa”? Girgizamai kai