Showing 51001 words to 54000 words out of 108352 words
Chapter 18 - Alkawarin Zuciya by M Shakur Complet .txt
dudda shi yasaketa, sosai Mami tabi tundaga hannun nata data rike Aliyu dashi da kallo harzuwa fuskan Aliyu dazata iya cewa bata taba sanin yanama murmushi hakaba sai yau, wani irin kallon yarinyar yakema yarinyar kaman zai hadiyeta, zama Gwaggo tayi akan kujera Khairy kuma tadan tsugunna agabanta sanan ahankali taja gyalen Khairy baya sunnar da kai Khairy tayi kasa murya chan kasa tace “ina yini Gwaggo” wani irin washe baki Gwaggo tayi tace “Allah nagode maka Aliyu wayyo Allah na, yarinya ga ladabi ga biyayya gakuma kunya kagama biyana Hydar, Allah ya tabbatar da Alkhairi, inane gidanku gobe zanzo na nemama jikana aurenki” dagota Aliyu yayi dasauri yana hararan Gwaggo yace “ni bazakije neman mini aure ba hakanan kisa ahanani” Mami yadan kalla sanan yadauke kai yace “ga Mami Pickle” ahankali batare data dagakai takalli Mami ba tace “ina yini Mami” kan Mami nakan waya batare data kalleta ba tace “lpy sannu” Khadija da Amal ne duk suka gaidata suna murmushi sanan yakalli Gwaggo yace “bari narakata sai indawo mutafi” dasauri Gwaggo takara tashi tana warware kullin zaninta tace “bari nabata kudin mota” dariya Aliyu yayi yace “direbanta na waje Gwaggo” “kai wlh makirin yaro ne Aliyu bakin ciki kake zan bata kudi kai bani baka, katon banza kawai andaiji kunya” dariya Khairy tayi kanta akasa, sanan Gwaggo takawo dubu daya tasamata a hannu tace “gashi asaiwa kanne tsaraba ki gaidamin da mamanki kinji” Gyadamata kai Khairy tayi tace “nagode Gwaggo” Aliyu ya harareta irin hararan makwaduwa dinan yace “muje” Meena tace “bye Anty Khairy” bye tamata sanan suka wuce Mami tabi Khairy da kallo tundaga kasa har sama daya tabbatar mata da Yar masu kudi ce, ga zinare a hannunta da kunne atampan jikinta kadai is worth 260k gashi kuma taji Aliyu nacewa direban ta na jiranta awaje, a ina Aliyu yasamo Yar masu kudi haka, iska tadan fuzar ahankali takara kallonsu yanda Aliyu ke kappa kappa da ita kaman Yar Kwai, jitayi zuciyanta namata zafi, “kinga Zainabu kiramin mijinki awayanki bani da kati atawa in gayamai danshi yasami mata ohhh ashedai zanga Auren Aliyu kafin na mutu iyye, kai Allah nagode maka Allah, kiramin imaza” akufule tace “nima banda katin” dasauri Meena tazo wajen tace “Gwaggo inada shi bari nakira” wai Gwaggo kaman zata zare, sabida murDna.
[6/20, 7:15 AM] +234 904 375 3898: 3️⃣8️⃣
Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.
wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp
This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️
Saida sukakai waje kaman zatamai kuka tace “Ya Aliyu maisa baka fadamin u are taking me to your family ba” yana kallon fuskanta yace “sabida nasan bazakije ba idan nagayamiki” kaman zata fashemai da kuka tace “kasa inatajin kunya” dan dariya kadan yayi cikeda tsokana yace “kinata rirrike musu d’a agabansu kina wani boyewa abayana kaman zaki cinyeni” dan dariya tayi akunyace tace “Allah bakada kirki” ”ahaka kike sona” yay maganan yana dagamata gira daya, turomai baki tayi tace “nadena daga yanzu” bakinta yakafe da idanu ganin kallon dayakema bakinta yasa taji wani irin kunya dasauri tajuya tai hanyar motansu bamata tsaya jiranshi ba tabude motan ta shiga, biyota yayi har wajen hakan yasa tasaukar da glass din motan kasa tana kallonshi, dukowa yayi yana kallon fuskanta kafin ahankali yace “thanks for the gift” gyadamai kai tayi tana juyarda kanta ganin kallon dayake mata, murya chan kasa ta yanda dagashi sai ita zasu iyajin maganan dasuke ko Adamu bazai iyaji ba yace “I love you so very much My kunya budurwa” hannu tasa ta tureshi yadan koma baya yace “stop it, Adamu muje” gwalo tamai yana kallonta yana murmushi suka wuce sanan tamai bye, bye shima yamata kafin yawuce motanshi zama yayi sanan yabude jakan data kawomai da tuntuni ke hannunshi yana kallon congratulations din da aka rubuta sanan yadaye ledan yabude kwalin agogon murmushi yayi sosai agogon is very classic he loves everything about it sanan yabude kwalin glasses din, murmushi yasakeyi shi kadai yasan yanda yakeson Ummulkhair danko ita bata saniba, maida komi yayi cikin jakan ya ijiye sanan yadauki wayanshi text yamata.
“I love my gifts wholeheartedly, Nagode Miss Khairy, Aliyu’s Pickle❤️” ijiye wayan yayi amota yawuce yafita dan zuwa daukosu Gwaggo su wuce sitafi gida.
Harsuka gama exam aka basu one week break yakare bataje gidansu tasan zata koma but batajin she’s ready ba, tana bala’in jin dadin zama da Mom, ga Batool ga Zara’u she’s not alone anan bataso takoma gidansu tadawo all alone kuma.
Ita gidan nan har mantawa da Ammi take bamatason abinda zaisa Mom ta tuna ta aikata side din gaida Ammi wani zubin ko Mom ta turata waje zataje tadade sanan tadawo tace taje. Itada Aliyu ko soyayyan su kawai gaba takeci, yau one eeek kenan basu hadu ba sabida yabi Abban shi suje lagos yin wani aiki amman cikin satin nan da aka shiga yace mata zai dawo.
Fadowa kanta Batool tayi wuraren 9 nasafe tace “ba dole ki kasa tashi ba yarinya baki barina bacci sabida wani soyayya da Aliyu” tureta Khairy tayi tace “Wlh zansa yayi arresting naki idan baki dena damuna ba kema banaki soyayyan kike da Umar ba” dariya Batool tayi tace “wai this week ma baxaki je school ba” “lectures is not yet serious leave me alone Batool please I am sleepy” tai maganan tanajan bargo zata rufe kanta back fizge bargon Batool tayi hakan yasa tawani tazo ihu Batool tayi tafice dagudu itama tabiyota tace “wlh saikin sani” dariya Batool keyi tana gudu tana sauka daga stairs itama tana binta Mom dake zaune afalon sama tace “kuyi jakanci da kyau wlh duk wacce tafadi cikinku bazan bata magani ba” kaman badasu Mom keyi ba sukai falo Batool na dariya tana gudu tace “ko banza natadake gashinan ma ina sAki morning workout” kulewa Khairy tayi tayo kanta ganin tana neman kamota yasa Batool tai wani uban ihu tabude kofa tafice waje Khairy tabita aguje itama sukai hanyar bayan gidansu suna guje guje kaman yara Khairy taki hakura Batool taki dena mata dariya tana gudu sukai backyard da akai shanya na zannuwan gado da labulaye a igiyoyin hakan yasa abin yazaman musu kaman hide and sick, dazaran Khairy taga alamun mutum zata daga kayan da aka shanya saitaga babu Batool saitai tsaki, hango alamun mutum datayi abayan wani thick zanin gado yasa ahankali sadaf sadaf taje wajen saida taje daidai wajen sanan tasa hannunta takama hannun Batool din gam tana wani irin murna tana dariya tace “ubanwa nakama, nikike tsokana ko wlh yau saikin sani Batool” tawani finciko hannunta, jin ko alamun motsi hannun da tarike baiyiba yasa taji wani kalan tsoro daidai nan Batool tabude tsakiyan wani zanin gado da aka shanya tafito dukta jike takalli Khairy tace “ke dawa kike magana gani nan fa” danjuyowa Khairy tayi takalli Batool data fito ta tsaya ruwa yajijjika kanta da rigan baccin jikinta sanan ahankali tajuyo da kanta kalli gabanta sanan gently hannunta harwani irin rawa yake tashiga sakin hannun data rike Adan tsorace jitayi an kama hannun nata gam kafin tai motsi taji anwani fincikota zanin gadon yawani damke fuskanta da jikinta taji wani irin sanyi sabida lema lema dake jikin zanin gadon igiyan, sai chan taji an yaye zanin gadon ankara fizgota tashigo wajen wani irin mugun faduwa gabanta yayi ganin Ya Zayn dagashi saiwani gajeren towel fari a waist dinshi yana gaban pipe din dake supplying ruwa to his flat daya fito ya kunna dan baisan waya kashe ba, wani irin faduwa gabanta yashiga yi dan ita bata taba ganin namiji hakaba bakaya kwata kwara kosu Yayyinta bata ganin su haka, kauda kanta tayi gefe dasauri bakinta har rawa yake tace “uhmmmm so…..sor….” Kasa karasa maganan tayi ganin Batool datayi tayaye zanin gadon ta shigo wajen da sauri itama ganin Zayn yasa atsorace tace “Ya Zayn laaaaaa yaushe kadawo good morning” wani mugun kallo yamata sanan yakalli Khairy from head to toe tana sanye dawani pink gown na bacci mai gajeren hannu daya tsayamata iya guwiwa kanta babu dan kwali sai lafiyayyen kitson dake kanta, ga lema lema ajikin rigan na makalewa da zanin gadon yayi ajikinta lokacin daya fizgota big boobs dinta tsaye warrr babu any bra aciki ko vex, jitayi wani kunya ya shige ta ga tsigan jikinta natashi at the same time dayasa taji jikinta yadan soma rawa. Cikin wani irin kakkausan murya yace “idan kinsan bazaki natsu ba kibar gidan nan, I hate mutum mara natsuwa, bar nan wajDen!”
Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.
wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp
This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️
Sakin hannunta yayi dawani irin sauri tajuya gabanta nafaduwa dum dum Batool sai hadiye dariyanta take ganin yanda duk Khairy ta birkice sanan suka wuce suka shiga flat dinsu, suna shiga Batool tafada kan kujera tana dariya tana kallon Khairy datai kuriii jikinta har lokacin bai dawo daidai ba, kallonsu Mom data fito daga kitchen tayi tace “ya akayi” cikeda dariya Batool tace “Mom Khairy taje takankame Ya Zayn tadauka nine saura kiris yamaketa bakiga yanda dukta rude” hararan Batool Mom tayi tace “wlh daya makemin mu danama mai godiya, yara daga tashinku kunbi gida kuna guje guje ko kayan bacci baku cireba ku wuce kuje kuyi wanka kuchanza kaya kafin na sassaba muku” Khairy tafara gaba kafin Batool tabita abaya, hartahau stairs sanan tajuyo takalli Mom tace “Mom yaushe Ya Zayn yadawo”? Batare da Mom takalleta ba tace “around 2 nadare ya shigo gidan nan kuna bacci lokacin” wani irin tsalle Batool tayi tace “yanzun nan bai wanka zanje nasame shi Mom yabani kudin ankon Na’ima” “kinfi kusa” Mom tai maganan tana shiga kitchen abinta itakuma Batool tajuya tai dakinsu, shiga tayi ganin babu Khairy afalon yasa tafada kan gado tana jiranta tafito daga wankan.
Fitowa Khairy tayi daure da towel dinta pink akirji ko kallon Batool din batayiba tawuce wajen wardrobe dinsu, tashi Batool tayi zaune tana kallonta tace “towai fushi kikedani danna tadaki daga bacci sorry to” juyowa tayi ta balla mata harara tace “ni gidanmu zan ma koma Wanan da wanchan Yayan naku yafaramin gorin gida daga ganina bazan dauka ba” dasauri Batool ta tashi dan idan akwai abinda ta tsana shine taji Khairy tace zata tafi gidansu, dasauri ta tsaya kusada Khairy dake shafa mai ahankali tace “ke dalla don’t mind Ya Zayn, wlh Ya Zayn nada bala’in kirki barshi dai da iyaji da kanshi amman yanada kirki kinga duk wulakanci Ammi baya biyemata wlh, Bakiga yana shigowa nan ya gaida Mom ba dudda Ammi bataso shi baruwan shi kuma yana sonmu, yana bani kudi koban tambayeshi ba hakama Zara’u, har dakinshi tana zuwa taitamai surutu wlh baida wulakanci, dan Allah karki kara cewa zaki tafi” kwafa tayi tajuya mata baya tanasa bra sanan tajuyo binta da kallo Batool tayi tace “ke Khairy ai wanan Bra yamiki kadan, kinada nono wlh Khairy kaman muyi musanye” dan tsaki tayi tadau riganta tana sawa, Batool cikeda tsokana tace “iyye su Ya Aliyu zai more” dawani irin sauri tajuyo zata dakamata duka ihu Batool tayi tawuce dagudu tafada bayi, dan murmushi tayi tana kallon kanta a madubi saikuma akunyace tamake kafada tace “ni bazan ma taba bari yaganni bama rigaba balle ma yaganni” karasa shiryawa tayi abinta cikin wani plain dogon rigan atampa ja batare data daura dan kwali ba tafito zuwa saukowa tayi kasa Mom ce kadai tanashan tea a dinning dayaji kayan kamshi ganinta yasa tace “ko kefa jibi yanda kikai kyau” dan murmushi tayi Mom tace “oya zoki zauna kiyi breakfast” karasowa wajen tayi tace “Mom ni indomie zandafa” baki Mom ta tabe tace “Allah dai yay wadaran naka yabaci, nidai kinga tafiyata bari naje natado Baban ku daga bacci, yadan kwanta shima yazo yay kari” kitchen tawuce itakuma Mom tai sama abinta.
Wani karamin tukunya tadauko sanan tashiga store dinsu tadauko indomie daya da kwai guda daya tafito sanan ta tara ruwa tukunna gas don tadaura sanan tawanke kwan a tap tazo tasaka a ruwan pot din tarufe pot din sanan takoma store, albasa tadauka awajen, wani black wukan datagani ijiye tunkwal shikadai a store din tadauko tace “hala Mom ta manta da wukan nan a store ne baga wajen wukake duk suna nan ba” takalli cabinet din wukansu wucewa gaban tap tayi tadauraye wukan sanan tasa wukan ta yanke kan albasan sanan tabare albasan tass, kafin tasa wukan taraba albasan biyu ta ijiye rabi akasa sanan tadauki rabi daya tasa wukan tafara yankawa cirrrr wukan yawani irin yanketa a tafin hannu lafiyayyen yanka dayasa batasan lokacin data saki wani azababben ihu ba daga wukan har albasan nafadi akasa daidai lokacin Zayn na shigowa falon yana sanye da 3quater dawata faran riga, jin ihu acikin din Mom yasa yay kitchen din dasauri ganin Khairy tana yarfe hannunta da jini ke tsayaya ya diddiga ko’ina a kitchen din tana ihu tana kuka ga wuka da albasa akasan kitchen din yasa yay kitchen din da sauri hannunshi yasa ya karbe hannun nata data yanke dasauri yay tap da ita kunna tap din yayi ya tare hannun kasan ruwa wani kalan fashewa da kuka tayi zata kwace hannun amma yaki yana wanke jinin daidai lokacin daga Mom har Baffa dasukaji ihunta sun shigo kitchen din dasauri wukanda Mom tagani akasa yasa tai salati. “Innalillahi waya fito da wukan daga store” cire hannunta Zayn yayi daga tap but still jini zuba yake ganin haka yasa Baffa yace “kawo first aid kit dinan Wife” fita Mom tayi daga kitchen din, ahankali Zayn dake rikeda hannun yakalli fuskanta yanda take kuka da yanda har gumi yafeso agoshinta dan ita anytime she’s stress or in pain tuni zakaga gumi yaketo mata a goshi, yanda gumi yasa gashin gaban goshinta ya kwanta ga hawaye na gangarowa daga idanunta datake gogewa da bayan dayan normal hannunta idanunta duka suna kan hannun da jini kefitowa dagakai yasa yaji beat din heart dinshi na raguwa, ahankali kaman wanda wani abu ke controlling yakai hannun saitin bakinshi kafin ahankali yadaura bakinshi kan hannun wajen yankan yanashan jinin yana kallon fuskanta, wani irin sanyi taji bakinshi yayi akan yankan kaman yadaura ice akai shiru yadena mata zafin dayake dawani irin sauri takalleshi tana ware manyan idanunta duk wani hawaye datakeyi ya tsaya chak Baffa dake bayansu tsaye ya tsaya chak yana kallonsu daidai nan kuma Mom tashigo dagudu tace “gashinan Zayn” firgigit! Kaman wanda yadawo hayyacin shi, bakinshi yazare dagakan ciwon, sanan yana rikeda hannun nata yakarbi spirit din da Mom kebashi yazuba mata akan hannun wani kalan ihu tayi dasauri yashiga hura mata hannun da iskan bakinshi hakan yasa tai shiru, auduga yakarba daga hannun Mom yadaura kan hannun sanan yasa plasta akai kafin ahankali yakalli Baffa yace “Abba akaita tayi tatanus injection” Dawani irin sauri Khairy tace “Baffa no dan Allah dan Allah Baffa kar Amin allura” dan dariya Baffa tayi yace “Khairy Khairy, ai Khairy tun tana yarinya batasan allura wuce kije ki zauna wai mema tazo yi a kitchen din” Mom tace “wai indomie zataci ga abincin normal mutane amman Khairy indomie zataci wuce tafi nadafa miki, wukan nan sabida yanda nasan kaifinshi yasa naboyeshi a store ko ya akayi tafito dashi oho” Mom tai maganan tana daukan wukan itakuma ahankali tawuce tafita hannun namata zafi, Baffa yakalli Zayn dayadan saci kallonta yace “let’s go Son, yaushe kashigo” dan murmushi yayi yace “yanzun nan nazo gaida Mom ne shine naji yarinyar chan na ihu kaman bera”
Juyowa dasauri Khairy tayi jin ita yake kwatantawa da bera, mugun kallo Baffa yamai yace “karka kara kwatantamin y’a da bera” zama tayi a dinning ahankali Baffa da Zayn suka wuce falo suka zauna akan kujera.
Baffa yace “yanzu tunda kagama komi yaushe zaka fara company and start managing everything, I want to retire nima nahuta” anatse yace “Abba bari nadan huta” atsanake Baffa yace “I am giving you just 2 weeks to rest Zayn am I clear” gyadama Baffa kai yayi cikeda girmamawa, saikuma chan yamike tsaye ahankali yace “bari naje wajen Ammi” gyadamai kai Baffa yayi yace “okay yaushe zakaje gaida Baffan naka” dan ware idanu Khairy tayi jin ana maganan gidansu, ahankali Zayn yace “anjima da yamma” ganin yanda Khairy ke kallonsu yasa yace “zakije” dasauri ta gyadamai kai tana murmushi kallon Zayn Baffa yayi yace “to kaje da Khairy idan zaka tafi” dasauri daga Zayn din har Khairy suka kalli juna dan bata taba tunanin Baffa saice Zayn yaje da ita ba ita tazaci kawai zaice taje idan ta shirya Adamu yatafi da ita, wani kalan mugun kallo Zayn yamata sanan yawuce yafita daga dakin.
[6/20, 10:24 PM] +234 810 499 3160: DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFIN NAN BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA
Dakin Ammin shi yawuce, tana zaune as usual cikin shiga na alfarma kaman matan shugaban kasan Nigeria waya a kunnenta tana waya, kan stool na gabanta kuma fruits ne yankakku da spoon aciki da alamu sha take sai wayan ya tsayar da ita, zama yayi kusada ita sanan yadauki bowl na fruit din nata yafara sha abinshi wayanshi yaciro yana dubawa miss calls yagani like 9 daga number daya shiru yayi yanaji ranshi na baci baisan ya akayi Faisal yabama that Aisha girl number shi ba, bayan yabar Abuja lokacin da Mama tarasu daya koma baima sauka agidan ba hotel yakoma da zama dan he’s tired of yanda yarinyar keep stalking him school gida kaman zata haukace akanshi, he just had sex with once which he paid which infact ma bashi yama nemeta ba, Wanan halin datakeyi yasa kwata kwata bayama neman yaran naija, all babes dinshi achan turawa ne cus sunsan menene sex for fun not sex for attachment, dan tsaki yaja ganin tasake kiranshi ya ijiye wayan Ammi datagama call tace “kai lafiya kana neman fasa wayanka” ahankali yace “Ammi damuna wata mayyan yarinya take ne wlh” dan murmushi Ammi tayi tace “kai haka kakema yammata wulakanci ahaka zaka sami matan kayi aure, danni wlh tasaka zanyi agaba Kwanan