Showing 69001 words to 72000 words out of 108352 words

Chapter 24 - Alkawarin Zuciya by M Shakur Complet .txt

24 Dec 2024

5644

wanda yaganta yaga Yar fulani. Girgizakai kawai Dad yayi cikeda takaici yawuce dakin Aliyu Yar takardan daya rubutamai address yakalla to ai yasan gidan nan gidan Alhaji Muhammad shine Dr Mama data rasu, yasan sunada yarinya mace though baitaba ganinta ba cus yasan basu fadama yarinya Maman nada cancer though baisan sunanta ba, ajiyan zuciya yasauke sanan yafito Gwaggo yasa abayan mota yasa keken ta abaya sanan yashiga gaba yaja motan har zuwa gidan Baba.
Dayake gateman yaganesu budemusu gate yayi sanan yawuce ciki dasauri bin gidan da kallo Dad yayi ganin kaman ma shagalin biki akeyi ko minti daya ba’ayiba Baba dakanshi yafito hakan yasa Dad yasauko daga mota yana bashi hannu yace “Dr barka da zuwa” murmushi Dad yayi yace “mun same ku lpy ina zuwa tareda Gwaggo nake” yay maganan yana ciro keke sanan yazaga yafito da Gwaggo yadaura ta akai ganin tsohuwa yasa har kasa Baba ya tsugunna yace “ina kwana Gwaggo” washe baki yayi yace “lpy dan albarka ya aiki” dasauri Baba yace “Alhamdulillah kushigo yau gidan cike yake dayake ana shirye shiryen biki ne” dasauri Gwaggo tace “bikin wa” murmushi Baba yayi yana bude musu kofan flat dinshi dan a shiga da Gwaggo yace “na yarana” shiga da ita akayi, falon Baffa ne zaune sai Mom dan Ammi bata biyosu ba dan haryau bata shiri da Baffa, sai Anty Mariya afalon, shima Baffa na ganin Dad yace “aaa Doctor kaine” murmushi duk akayi aka shishiga gaisawa Anty Mariya taje takawo musu lemo sanan aka zazzauna akai shiru Gwaggo takalli Baba tace “kaine mahaifin Ummulkhairy” dasauri Baba yace “eh nine” Gwaggo zatai magana Dad ahankali yace “Gwaggo” shiru tayi sanan anatse Dad yakalli su Baba dake kallonshi yace “duk kun sani anan, sunana Abdullahi Abdulwahab Yola, ni likita ne, Gwaggo itace mahaifiyata, matata daya yanzu haka, tafarkon tarasu, yarana bakwai namiji daya sauran duk mata yanzu saura mata uku agida sauran sunyi aure, Yarona na farko sunanshi Aliyu Police ne shi dudda lawyer ne dan abinda yakaranta a school kenan he’s a barrister but he choose aikin police sabida mahaifiyanshi data rasu abinda taso yazama kenan, ASP Aliyu Hydar though Kwanan nan akama karamai girma” dasauri Baba yace “Allahu Akbar ai mu dukanmu nan munsan Aliyu, yanzu dama Aliyu danka ne kaga yanda duniya yake ko amini” Baffa yagayadamai kai sanan yashiga bama Gwaggo da Dad labarin abubuwan da Aliyu yana yarsu Gwaggo sai washe baki take kaman gonna auduga.
Anatse Dad yace “to Alhamdulilah akwai abinda yakawo mu gidan nan naku yau dasafen nan nida mahaifiyata” Dad yadanyi shiru sanan yace “d’ana Aliyu kwanankin baya yazo yasameni yasanar dani yanason Ummulkhairy amman ita tafiso sai tagama makaranta sanan yanemi aurenta…….” Nan yabama su Baba labarin komi har zuwa tafiyan kauyen datace sunyi da yanda Aliyu yadamu baigantaba har zuwa abinda ma yasa sukazo yau shine rashin lafiyan dayakeyi dakin shiru kakeji kaman ruwa yacinye kowa.
Anatse Baba da mamaki ta cinyeshi yakalli Anty Mariya yace “dalilin dayasa Khairy ke zuwa exam da nikabi da hijabi har kasa kenan”? Ahankali Anty Mariya tace “bansani ba gaskiya” shiru Baba yayi sanan ahankali yakalli Dad da Gwaggo ahankali “yashiga basu labarin rayuwansu daga farko har zuwa ranan da Khairy tasani har zuwa yau wanda bikinsu jibi ne ranan asabar yau alhamis…. Baba yakarashe da “Inaga Khairy takasa fadamai gaskiya ne saisa tamai karyan mun tafi kauye” fashewa da kuka sosai Gwaggo tayi afalon dasauri aka shiga bata hakuri, sauka tayi daga kan kekenta ahankali kowa na kallonta dukawa datashiga kokarin yi yasa kowa yamike tsaye ganin tsohuwa tukup tukup zata duka musu dawani irin sauri Baba yatashi yariketa yace “Gwaggo dan Allah karki duka mana” cikin kuka sosai tace “kuwa Allah kubama jikana Auren yarku, wlh sabida marigayiya batasan Aliyu na bane wlh Aliyu zai kulamata da Khairy, zai rikemata Khairy amana, dan Allah kuji tausayin Aliyu na kar wani abu yataimakeshi, Baban Zayyanu Dan darajan iyayenka kubama jikana yarku” jikin kowa yay sanyi babu wanda ya iya cewa wani abu, Dad da jikinshi yamutu da kyar yatashi Gwaggo dake kuka sosai ajikin Baba yakama yanadan murmushi yace “Gwaggo zoki zauna kiga” dakyar ya zaunar da ita sanan yakalli su Baba dakowa jikinshi yay sanyi zaiyi magana Baba yakama hannunshi yace “da ace babu zancen Zayn babu abinda zai hanani baku y’ata naga Aliyu nakuma yaba da tarbiya hankali da natsuwa irin na Aliyu, Aliyu yaro ne nagari nai kare yancin kowa, kuyakuri Dr, kuyakuri” dasauri Dr yace “dan Allah kudena cemin nayahakuri mutum baya wuce rabonshi inda Khairy ta Aliyu ce zai sameta cikin sauki, Allah ubangiji ya Sanya alheri, Allah kuma yabasu zaman lpy, bari nakai Gwaggo gida sai anjiman ku” har wajen suka rakosu Gwaggo na kuka sosai yasata amota jikin koCwa yay sanyi.
Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp


This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️




5️⃣2️⃣




Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp


This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️




Harsukakai gida kuka Gwaggo takeyi hakan yasa Dad yakai Gwaggo side dinta yace “dan Allah Gwaggo kidena kuka kar Aliyu yagane idan yaji sauki saimu fadamai gaskiya dan Allah Gwaggo” bakin zani takama ta warware ta fyace majina tace “Abdul nafi kowa sanin yanda Aliyu keson yarinyar nan tunda harkaga yadauki yarinyar nan dungurungum yakawomin, Allah kai zurfin cikin nan aiko kasan yana sonta tayaya zamu gayamai jibi ne bikin yarinyar nan eh”? Ahankali Baba yace “Gwaggo Aliyu zai hakura daga baya yaji sauki dakaina zan mishi bayanin komi kinji kema kiyakuri bari naje nadubo shi” gyadamai kai Gwaggo tayi tace “tom jeka” fita yayi daga dakin Meena dake uwardakan Gwaggo dataji komi komawa gadon Gwaggo tayi da gudu takwanta kaman kai bacci tana hadiye kukan datakeji Gwaggo tashigo dakin ganinta tana bacci yasa tace “Alhamdulilah nasan inda munafukan nan taji zata iya zuwa tafadimai” tai maganan tana daukan kwaryan maganinta tana dafa bango tafito falo tazauna kurban maganin tayi sanan tabuga tagumi ahankali saikuma tafashe da kuka wiwi.




Ahankali Dad yashiga side din, ganin Aliyun na bacci yasa yadan sauke ijiyan zuciya sanan yajuya zai fita daga dakin kaman daga sama yaji Aliyu yakira sunanshi. “Dad”juyowa Dad yayi ahankali wearing a smile a face nashi sanan yakarasa gaban gadon yace “kai Aliyu ashema nasan mahaifinta nine Dr Maman Ummulkhair kafin tarasu” ganin yanda Dad kemai murmushi yasa ahankali yaji wani karfi yazomai da karfinshi ya yunkura yatashi zaune yana jingina da gado, murmushi Dad yayi yace “ance jibi zata dawo daga kauyen wai rasuwa aka musu saisa suka tsaya, Babanta da Yayyinta kadai ne agida ita da Amaryan Baban nachan kauye, kana damun kanka ne for nothing, danaji haka shine nace okay bayan sun dawo kaima lokacin kaji sauki garau basai muje dakai a nemo aurenta ba, so get on ur feet yarona” dan murmushi yama Dad ahankali yace “thank you Dad” murmushi Dad yamai ya shafa fuskanshi yace “bari naje nadan kwanta tunda yau bazanje aiki ba” gyadama Dad kai yayi ahankali yawuce yafita wani dan karfine yaji yazomai ahankali yatashi yana dafa bango dan har yanzu kanshi na sassarawa yashiga bayi alwala yayi sanan yafito dadduma ya shimfida yayi salla sanan yakoma kan gadon yasake kwanciya yana lumshe idanu.
Wuraren 1 aka bude kofan dakinshi lokacin yanakan dadduma ya idar da salla, Meena ce tashigo dauke da tray da mug na coffee kekai dakuma sandwich agefe karasowa gabanshi tayi akan dadduman ijiye tray din tayi sanan tazauna ahankali tace “Ya Aliyu namaka coffee” muryanta dayaji yasa yakalleta dasauri ganin yanda idanunta sukai jaa yasa ahankali yace “what happen?” Girgizamai kai tayi dasauri sanan tace “bakomi sha coffee please kaci abinci kaga kai kadai gareni” tai maganan hawaye na zubomata gyara zama yayi yana kallonta dan murmushi yayi da kyar sabida yanda kanshi keciwo yace “are u like this sabida banda lafiya”? Girgizamai kai tayi dasauri tana kokarin danne kukanta amman takasa tafashe da kuka sosai dayasa yarike hannuwanta yace “menene Amina?” Kallonshi tayi cikin kuka da bakinciki tace “Ya Aliyu Ummulkhairy ta yaudareka jibi ne bikinta” wani irin daran kaman karan kararrawa yaji zuciyanshi nayi dasauri yakalleta dan baigane inda ta dosa ba, ahankali tace “dazu naji maganganun su Dad da Gwaggo dake kuka sosai afalo bayan sun dawo daga gidan su Khairy, babu inda Ummulkhairy taje tana gidansu bikinta za’ayi ranan Saturday dinan jibi dawani Yayanta Zayyanu inji Gwaggo dan tun dazu sambatu takeyi tana kiran sunanshi, Ya Aliyu I am very very sad for u kaman in kashe kaina nakeji sabida nasan yanda kakeson Khairy, su Dad basuso su fadama wai saika warke amman Bikin Ummulkhairy ranan satur……..” “stop it!” Aliyu yadaka mata wani mummunan tsawa dasaida takoma baya dasauri, runtse idanunshi yayi batare daya budesuba yace “leave this room Meena” dawani kalan sauri Meena ta tashi tafice tana goge hawayen datakeyi, Aliyu yakai kusan minti ashirin zaune inda yake he’s trying yafadama kanshi maganan da Meena tagayamai karyane na Baban shine gaske, kunnenshi keeps hearing bikin Khairy jibi ne Ya Aliyu, wani irin mikewa tsaye yayi kaman zaki car keys dinshi dake kan gado da wayanshi yadauka yawani fice kanshi nasarawa amman bayamaji tsabagen fitinannen kishinn dayakeji azuciyanshi, motanshi yashiga gateman nabudemai yaja motan feee yawuce, gudun dayake akan hanya zaka dauka yazare ne cikin ikon Allah yakawo har kofan gidansu Khairy awani irin hankali yay parking yana kallon kofar gidan dayaga anyi pentin shi gate din gidan a bude ana shiga dasu kanopi da kujeru cikin compound din ana jerawa hannunshi ahankali yadaga yadaura kan kirjinshi dayaji yanamai zafi sosai kaman an zuba garwashi akai, wani irin rawa da bari jikinshi yafara yana kalle kalle baimasan maiyakeyi ba, wani irin bude kofan motan yayi marfin kaman zai balle sanan yasauko daga motan, duk wanda zaiga Aliyu zaisan baya cikin hayyacin shi, shiga gidan yayi yana kalle kalle ko’ina, dayake mai gadi baya wurin yana wajen masu saka kanopi yana tayasu aiki yasa Aliyu yawuce ciki yana kallon banner dasuke kokarin makalawa abango an rubuta #KhaZy saikuma a tsakiya ansa Ummulkhairy weds Zayn! Jiyayi gabaki daya kwakwalwan shi yafara boiling babbabaaa, bayamaji da kyau chak bakumaya gani da kyau ya tsaya kaman wanda yasami tabin kwakwalwa yawani irin kwalamata kira babu ko shakka ko tsoro atattare dashi. “Ummulkhairrrrrrr!” Wani irin amsawa gidan yayi da su kansu masu aikin saida kowa ya tsaya chak suka juyo suna kallonshi.


Ummulkhairy na zaune dasu Batool da Anty Mariya da Besty afalon sama ana mata lalle akafa daya dan yanzu aka fara, cikin besty yafito tai kyau sosai kaman daga sama taji muryan Aliyu harcikin kashin zuciyanta taji yanda yakirata dawani irin sauri ta zabura tamike tsaye zumbur tana kalle kalle tama manta lalle ake mata hakan yasa daga mai lallen harsu Besty sukace “ke lpy”.
“Ummulkhairrrrrrrree!” Aliyu yasake kiranta akaro nabiyu da gidan ya mugun amsa danko su Anty Mariya saida sukaji dan kaman yay using microphone it was so audible, dawani irin gudu Ummulkhairy tajuya tai stairs su Anty Mariya da Batool suka biyota dasauri, wani irin bude kofan falo tayi tafito ido da Aliyu tayi da Aliyu dake tsaye tsakar gidansu idanunshi sunyi jajir kaman jini wallahi, fuskan Aliyu dakenan fari kal yau fuskanshi yay ja shima, wani irin zufa naketomai akowani bangare na fuskanshi.
Fuskanshi kadai tagani taji zuciyanta ya tsinke she saw his pain and agony Wanan kuma shine abinda yasa she avoided him takasa fadimai, ahankali tadaga kafa zata tafi wajenshi Besty tarike hannunta, muryanta nadan rawa tace “Besty, Anty Mariya dan Allah kubari naganshi nagayamai gaskiya please, kar wanda yabiyoni lemme talk to Ya Aliyu” karbe hannunta tayi sanan ahankali tashiga sauka daga stairs din tana wani irin kallonshi kaman yanda yake kallonta suma ma’aikatan kowa yacigaba da aikinshi ganin anma San mutumin sunsan juna tunda ga amaryan tafito taganshi, yanda taga Aliyu kaman zaki yasa takasa karasawa gabanshi, dan nesadashi ta tsaya ayanda taganshi kaman zai Chaka mata wuka yake murya chan chan kasa dake mugun rawa tace “Y……Ya Aliy……” bata karasa maganan ba jin wani fizgo hannunta dayayi kaman zaki kawai yashiga janta dawani irin sauri kaman jirgin sama su Mom Anty Mariya dasu maigadi damasu aiki suka biyosu amman ina! Kafin suma fito waje Aliyu yajefata amota yaja motan da arnen gudu ma’aikatan nabin motan dagudu, arude Anty Mariya datafito har waje ba hijabi ba mayafi takalli su Batool da Besty arude tace “kubani wayaZna nakira Baban ku Aliyu yasace Khairy Innalillahi wa innailaihi raji’un”.
Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp


This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️










[6/29, 8:41 PM] +234 816 788 8825: 5️⃣3️⃣


Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp


This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️




Dawani irin gudu Batool tayi cikin gida hankalinta abala’in tashe tadauko both wayanta dana Anty Mariya tana zuwa Anty Mariya data bala’in rude hankalinta atashe tabama wuyanta dasauri tashiga kokarin kiran Baba, itama Batool a bala’in rude ko’ina najikinta na kyarma tashiga kiran Mom dinta amman wayan Mom baya shiga hankali tashe tama rasa yanda zatayi ta danna ma Ammi kira, Ammi na zaune a falonta tana surfafa ma Zayn bala’i kan auren nan yay shiru kawai yanajinta danshi yafi kowa murnan Wanan news din, kawai kallonta yake yay shiru danshi kanshi bala’in uwarshi yafi karfinshi, ganin wayanta na ringing yasa cikeda masifa tadauki wayan takara akunne tace “ubanme kike kirana ko Gulman kine yatashi” arude cikin kuka sosai Batool tace “Ammi ina Mom Ya Aliyu yazo yasace Khairy yatafi da ita” wani irin kallon wayan Ammi tayi da taciro daga kunne takalla danta tabbatar Batool ne hakan yasa ta maida wayan kunnenta tace “waye kuma Aliyu?” Cikin kuka tace “Ammi saurayin Khairy ne baisan an musu aure da Ya Zayn ba shine yazo yanzu yasaceta please kifadama Abba da Mom mun shiga uku” takatse wayan wani irin ajiye wayan Ammi tayi sanan tashiga tafi da hannu tana kallon Zayn dake kallonta tace “kagani ba kai aka rainama wayau, yarinya itama basonka takeba kai kananan kanamin Yar murya kana bani hakuri nabar batun nan gashinan takira saurayinta Aliyu yazo har gida yadauketa sun gudu shashasha kawai rago” wani irin kallon Ammi Zayn yayi dan baima gane metake nufi da maganan ba Aliyu kawai yasan yagane amaganan ahankali yace “Ammi what are you saying”? cikin bala’in fushi tamai dakuwa tace “kaci ubanka da what are you saying, Zayn wai anya nina haifeka kuwa? Ubanka yakama yahada maka auren da bakasan dashi ba gashinan har gida saurayinta Aliyu yazo yadauketa sun gudu inji Batool” wani irin mikewa tsaye Aliyu yayi yana kallon Ammi dakemai wani mugun kallo tace “idan nabari kazauna da Ummulkhairy amatsayin mata shegiya uwata tahaifeni Zay……” kafin takarasa kiranshi Zayn yawani irin juya dagudu yafita daga dakin Ammi takwalamai kira amman ina bamayaji sabida yanda zuciyanshi ke tafarfasa kaman zai sume, cikin ikon Allah yakai gidan daidai daga Baba, Baffa su Ya Manaf duk suna kaiwa gidan kana ganin kowa kasan hankalinshi atashe yake atare duk suka shiga falo ita Anty Mariya tana zaune tana kuka daga ita har Batool, Besty damai lalle ne ma sukai zuru zuru kowa cikeda damuwa.








Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.


wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp


This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️
Ahankali Baba yace “maiya faru”? Kasa amsashi duk sukayi Besty ce tace “Baba dukanmu muna zaune a falon sama, mai lallen nanma bamata dade da zuwa ba an fara mata lalle kenan akafa daya mukaji muryan Aliyun yawani irin kwalamata kira arude Khairy tashiga sauka muka biyota, Baba yana tsakar gida tsaye wlh kaga idanunshi zaka rantse jini ne aciki, bakaramin tsoronshi naji ba Khairy zata tafi nakama hannunta, tace mana dan Allah mubarta taje tamai bayanin komi, shine tawuce tana zuwa gabanshi kafinma tayi magana yaja hannunta…… “ wani irin runtse idanu Zayn yayi yay baya kaman zai fadi dasauri Manaf yatare shi yace “Zayn” dan bude idanu kadan yayi yakalli Manaf sanan ya fuzar da iska, Besty tace “dukan mu nan har masu aikin kanopi saida muka bishi amman babu wanda ya iya cimmishi yasata amota yatafi” tarushe da kuka dakin yay shiru, awani irin zuciye Zayn yaciro wayanshi zuciyanshi na tafarfasa yace “I will inform the police” yashiga kokarin dialing wata number, jiyayi an karbe wayan daga hannunshi hakan yasa yadago kanshi dasauri yaga Baba ne, katse kiran Baba yayi sanan yabubbuga kafadanshi anatse yace “I know you are hurt Zayn amman nobody is involving police in this case, nasan Aliyu Zayn na yarda da tarbiyan Aliyu dudda ba d’ana bane Aliyu bazai taba, I mean it Aliyu bazai taba cutar da Ummulkhairy ba, rabuwa da masoyi nada ciwo kota wani kala kona mutuwa ne kona aurene, I know fushi yake, kuma zuciya ce tadebeshi har yazo nan yatafi da Ummulkhairy, zai dawo da ita kayakuri babu abinda zai sami Ummulkhairy, lokacin dabai Santa baba yataimaketa yadawo da ita gida lami lafiya balle yanzu, dukanku kuyakuri” yakalli su Mom yace “kudena kuka lemme call his father”.


Dad na zaune kan dadduma dan yamakara yanzu Mami tazo tadatashi sallame sallan shi kenan yaga wayanshi na ringing, mika hannu yayi ahankali tadauki wayan Ammi dake hadamai shayi a mug tajuyo tadan kalleshi ganin Baba ne abin bakaramin mamaki yabashi ba ahankali yace “tomekuma yafaru lpy suke kirana ko wani abun ne?” Dad yama kanshi tambayoyin kafin ahankali yay picking call din yakai kunne, zumbur din da Mami taga yayi yasa tasaki tea datake hadamai tazo wajen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login