Showing 18001 words to 21000 words out of 61405 words
masa man kai🥵🥵🥵🥵
Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜.
Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃
Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥
Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉.
Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥
Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din
+234 809 699 9490
Bissalam❤️❤️
You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance
https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj
🥀🥀🥀🥀🥀
Aasmaa
🥀🥀🥀🥀🥀
Written by
Mrs A.M
Free book neh 🥰
Page 13
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Cikin muryar kuka tace “Yaya zaka aure ni da gaske Yaya, Mami zata yadda…”
Zame hannun sa yai daga cikin nata fuskar sa dauke da murmushi yace “uhmm ke dai wannan ba hurumin ki bane, in har kin amince so nake nan da wata biyu ayi mana aure Kanwataa..”
Da sauri tasa hannu ta rufe fuskar ta tana jin wani madaukakakin farin ciki a zuciyar ta.
Murmushi yai ynxu har hakoran sa suka bayyana, mikewa yai yana zura hannu a aljihun sa yace “so nake kuna gama WAEC ayi mana aure yadda baxa ki sakè kwanciya a asibiti ba kar zuciyar ki ta buga”.
A ynxu kuwa ya yadda cewa Yayan nasu ba wasa yake ba don haka ta mike tana rufe rabin fuskar ta, cikin rawar murya tace Yaya amma Meena fah..
Hade rai yayi yace “kika ce kina so na bayan kuma bakya kishi na, ynxu tambayar kishiyar ki kike”.
Duk da maganar ta mata zafi amma haka tayi murmushi cikin sanyin ta dama already ai tasan cewa Meena zai aura ynxu ne dai kawai daya ce mata zai aure ta sai kuma taji tana kishin Meena din sosai.
Ya fahimci halin data shiga don haka yace “Yusrah ban miki alkawarin cewa baxan sake aure ba ko da na auri Meena din kuwa, amma abinda nake so ki sa a ranki shine duk wacce zan aura baxan taba wulakanta kiba in sha Allah sbd ke din kina da kima da daraja a idona”.
Hawayen daya zubo mata tasa hannu ta goge, ba abinda take fada a ran ta sai Alhamdulillah.
Sai da ya tabbatar ta ci abinci kuma doctor ya sake duba ta sannan ya tafi.
Haka kurin bayan ya gama sauraran maganar Yusrah din da Waleeda yaji ba abinda zai yiwa Alhaji ya biya sa duk hidimar daya masa a rayuwa amma zai iya auran yar sa ko dan sbd ya ceci rayuwar ta.
Shi dama ba wai son Meena yake ba, don mahaifiyar sa kawai zai aure ta amma ko kadan baya son ta, yarinyar bata da kunya kuma yasan yadda take bin maza yasha ganin ta a gaban motar maza ko sun rungume juna ko suna kiss, da farko Mami yake sanar wa yana fada mata shi dai gaskia a fasa auren baya son ta bata da tarbiyya amma Mami din take nuna masa bacin ran ta shiyasa kawai ya kyale su.
Yana isa gida bai tsaya ko Ina ba sai gurin Alhaji ya fada masa dukkan kudirin sa na son auren Yusrah kuma cikin lokaci kan kani.
Fuskar Alhaji Washe da fara’a yace “Alhamdulillah Ya Rabbi, amma wani hanzari ba gudu ba Abdallah kana tunanin Mamin ku zata amince”.
Murmushi yayi yana shafa gemun sa yace “in sha Allah Abba”.
Gyada Kai Alhaji yayi yace “toh shikenan kaje tukun ku fara magana da ita, duk abinda tace sai ka fada min nidai Ina Jin kunyar na tunkare ta da maganar kar ta yi tunanin ko IKO da fin karfi nake son mata”.
Mike wa Abdallah yai ya nufi part din Mamin, so yake ayi komai a gama kawai asa ranar auren.
A dakin ta ya same ta don haka ya samu guri ya zauna bai tsaya kwana kwana ba ya fada mata abinda ya kawo sa da kuma maganar da sukai da Alhaji.
D’ora wa yai da cewa “don Allah Mami Kar ki hanani auren Yusrah don tana matsayin yarinyar Mummy, kinga kin bani umarnin auren Meena duk da bana so amma haka na hakura don na faranta miki plz Mami kar ki ce a’a”
Shiru tai Tana goge gumin daya ke zubo mata, ya zata yi da Bilkisu shine damuwar ta, ita ai ba butulu bace da zata ki amincewa da auren Yusrah, duk da mahaifiyar yarinyar ta kasance kishiyar ta kuma wacce bata ji dadin ta ba da farkon auren amma ita yarinyar tana da hankali sosai tunda kusan ma tarbiyyar Mamin ce kwana ne kawai bata yi a part din Mamin.
Ganin yadda tayi shiru yasa shi fadin “Mami….”
Murmushi tayi tace “tashi kaje zuwa da safe zan samu Baban namu muyi magana”.
Ba dan ransa yaso ba ya tashi ya fice yana addu’ar Allah yasa Mami ta amince.
********
Washe gari da wuri na tashi na tafi restaurant don Ina son a bani hutu ko na sati biyu ne yadda zan kula da Umma sosai.
Oga Kona ba dan ran sa yana so ba ya amince sai dai kawai sbd tace mahaifiyar tace ta karye kuma tun da Aasmaa din ta fara aiki a restaurant dinsu bata fashi, ko bata da lafiya tana zuwa da wuri tayi aikin daya samu sai ta koma gida.
A kwanakin da baxa ta zo ba yasan sai sun jigata, tunda yawancin manyan mutane suna zuwa ne don abincin Aasmaa din, wasu kuma son ta suke da fasikanci in taki amincewa sai suyi ta zaryar zuwa restaurant din suna cin abinci don kawai su ganta.
Ai bama su ba shi kansa zai yi missing abincin ta, kullum kafin ya tafi gida sai ya cika cikin sa shiyasa in yaje gida baya cin abinci, tun matar sa na Jin haushi har itama ta ware tun da wani lokacin da kanta take kiran sa ta ce tana son Aasmaa ta mata abu kaza zata ci in zai dawo ya taho mata da shi.
******
A cikin sati daya aka sa bikin Abdallah da Yusrah wata 1 da sati 3.
Irin murnar da Yusrah ta dinga yi bata baki ne, kullum bata da aiki sai turawa Yayan nata text na godia kala kala da kuma nuna masa irin yadda yake da matsayi a zuciyar ta.
Sai da kuwa ynxu wasan buya take yi da Mami da Abdallah din kansa, kunyar su take ji sosai shiyasa kullum tana daki a zaune sai dai su Sultan da Sultana da suka saba da zuwan Yusrah din ne suke zuwa part din Mummyn ynxu tunda ita ta bar zuwa part din su.
Sai murna suke yi Yayan su zai auri yayar tasu.
Mummy ita kam duk kunya ce ta Kama ta don haka ranar da aka sa bikin ta je part din Mami tayi mata godiya sosai ta kuma bata hakuri akan dukkan abubuwan data mata a da.
Murmushi kawai Mamin ta keyi tana ce mata bkm ynxu ai komai ya riga ya wuce an zama daya.
Ita Mami duk bata cikin nutsuwar ta don irin bala’in da Bilkisu tazo tayi mata a cikin gidan, ba irin cin mutuncin da bata mata ba har ita kanta Meena din dake kuka tace dama can ai Mamin ba son ta take ba kawai munafurci ne.
A gaban Abdallah ta fadi haka tun da yaga zuwan Auntyn tasa dama ya shigo palon don yasan cewa baxa ayi mai dadi ba, ai kuwa dai Meena ta daku a hannun sa don zage karfin sa yayi ga dinga kwallo da ita cikin zafin zuciya yana cewa dama shi can ba son ta yake ba don bata cikin matan da yake so in banda darajar Mami ma mai zai yi da ballagaza irin ta mai rabawa gayu a titi.
Da kyar Mami ta kwaci Meena a hannun Abdallah tana masa fada akan me yasa zai mata irin wannan dukan, shiru kawai yayi yana numfashi yana jifan Meena da Hajiya Bilkisu din da wani mugun kallo.
Haka suka koma gidan su bayan a take a gurin tayi wa Mami transfer din kudin zancen da aka kai wa Meena a cewar ta yar ta tafi karfin Abdallah ynxu kuma.
Shi ya dinga rarrashin Mamin tasu ganin tana kuka sosai, bata taba zaton Hajiya Bilkisu zata mata irin wannan cin fuskar ba, bama ita Bilkisu din ba yar ta Meena wacce zata aura wa dan ce take kiran ta Munafuka, ashe gaskiyar Maman tane data ce ita sam tarbiyyar Meena din bata mata ba dama sbd kawai taga sun dage ne shiyasa bata taba maganar ba.
********
Wanki nake a nutse na kayan baccin mu ni da Umma, cikin sati dayan nan da bana fita ko Ina har wani fresh na sake yi.
Ba abinda nake sai kula da Umma sbd hannun ta, Ynxu ma tana daki bacci ne ya dauke ta shine ba fito na yi wankin.
Hankali na baya kan wankin da nake yi tunanin yadda zanyi da Alhaji Inuwa nake yi, kwana biyun nan ya matsa min sosai kullum sai yazo shi da gaske yake aure ne ya kawo sa.
Alhaji Inuwa babban mutum ne don Autar sace ma sa’a ta ita ma kuma tuni tayi aure ta haifa, Ina zai kai ni ai ya mun tsufa baxai iya biyamin bukatu naba.
Ajiyar zuciya na sauke Ina dauraye Kayan duk rai na ba dadi.
Sallama naji ta namiji kuma kamar muryar wannan mara kunyar yaron, da sauri na juyo don ganin waye kuwa……
Plz kuyi hakuri da jina da kukayi shiru bani da lafiya ne amma ynxu Alhamdulillah naji sauke🥰
Ngd sosai My fans da yadda kuka nuna kulawar ku a gare ni Allah ya bar mu tare har a Aljanna 😘😘
Mrs A.M
09066728387
Salamu alaikum💃💃💃💃
Kuna ina mata masu daraja wadan da suke son su gigita Oga a tsotse masa man kai🥵🥵🥵🥵
Ga dama ta samu ku garzayo gurin Innar Nawaz domin ta tsuma amarya da uwar gida, sai dai Kiji ana gidan dadi na na baki kyaurar Nigeria gaba dayan ta😎😎😜.
Muna siyar da tsumin tabajeee🥵🥵🥵, Zumar kiba kiyi bulbul gwanin sha’awa ko Ina ya cicciko ki dinga juyi kina rausaya ana tana hankalin mai house😎💃💃
Muna gumba Kala Kala da gari wanda ake sha da madara ko nono, da akwai ragumi da akala daga Jin sunan kun san cewa ba’a magana kawai a ozar room🥵🔥🔥🔥🔥
Bafa anan muka tsaya ba muna da dan matsi, wato gangariya ne ko hannun ki baxai shiga ba sbd yadda zaki matse kina kamo Oga😉😉.
Kun san ita mace yar kamshi ce, a ko yaushe mu an san mu sa tsafta da kamshi, muna siyar da turare Kala Kala masu kamshi da dadi wanda zasu kwantar da hankalin Oga ya dinga manne miki yana lalubar ki😉😉🔥🔥
Domin samun wannan Kaya masu sauki ku tuntubi wannan number din
+234 809 699 9490
Bissalam❤️❤️
You should read "Aasmaa" on #wattpad #romance
https://www.wattpad.com/story/329112037?utm_source=ios&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=DijahAM&wp_originator=V1PLaustqUbJzsXd6Subht8nHXyopa29268W8RAoajngqkxEg2myYkKSL8%2BgemhwRtCBFS0idZMmpBlNdLrJFDkBvLIngq8aYPr%2FYKDw7NXYIN%2BZSJnKcMsdvHLZJFHj
🥀🥀🥀🥀🥀
Aasmaa
🥀🥀🥀🥀🥀
Written by
Mrs Elhajj
Assalamu alaikum My fans fatan kuna cikin koshin lafiya, kowa yasan ni da *MRS AM* toh an samu sabani da akwai yar uwata writer da take amfani da *MRS AM* itama mutane suna rasa gane wace ita wace ni.
Ni Marubuciyar
*NOOR*
*TASWIRAR KADDARA*
*ELHAJJ*
*ASMAA……*
Zan chanja suna na daga *Mrs A.M zuwa MRS ELHAJJ*
Domin magana da ni kai tsaye
09066728387
Free book neh 🥰
Page 14
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Tsaye yake yana sanye da three quarter light brown sai riga mai dogon hannu wacce ta matse sa black colour, yayi kyau sosai har ya gaji ga wani aski da aka masa wanda ya matukar haskaka fuskar tasa.
Da sauri na Kawar da kai na Ina tabe baki, wanki na na cigaba da yi cikin kwanciyar hankali duk kuwa da cewa kirjina banda bugawa ba abinda yake yi.
Abdallah bayan ta yabi da kallo idon sa na sauka akan mazaunan ta yadda suka baje akan kujerar sai da yaji tsigar jikin sa ta tashi.
Da sauri ya juyar da kan sa yana bin gidan kallo, tabe baki yai ya kalli Apple Watch dinsa dake hannun sa na dama.
Tsaki ya saki yana taka wo a hankali, yau Umma zata sake ganin likita shiyasa ya zo dan ya Kai ta hospital din a duba hannun.
A bayan ta ya tsaya yace “keee!”
Da sauri na juyo Ina kallon sa yadda ya zuba min manyan sexy eyes dinsa sai da gabana ya fadi, yatsina fuska nai Ina motsi da baki a nutse nace “wa kake cewa haka…”
Kawar da kan sa yai yace “Ina Umma…”
Juyar da kai na nima nai ina boye Bra dita da nake wanke wa a cikin ruwan nace “me zaka mata…”
Ba tare da ya kalle ta ba yace “ina ruwan ki….”
Ynxu kam mikewa nai ina dan jan rigata yadda baza ta dinga lafe mun ba na nufi daki ina cewa “in ka koyi girmama na gaba da kai sai ka min magana mara kunya kawai….”
Shi dai Abdallah bin mazaunan ta yai da kallo kawai yadda suke juyawa yasa shi lumshe ido yana Jin kaikayi a wuyan sa.
Ajiyar zuciya ya sauke kawai shima ya nufi kofar daya ga ta shiga ya daga labulen ya leka.
Daga Murya yayi yace Ummaaa….
Da sauri na d’ago Ina kallon sa yadda y ke ziro jikin sa yana Kara fadin Umman, mike wa nai da sauri Ina cewa kana da hankali kuwa zaka fado mana daki kai tsaye haka…
Ko kallon ta bai yi ba ya sake bude baki zai sake kiran Umman ta daga labulen dake tsakanin palon ta fito jikin ta sanye da Hijab.
Murmushi ta sakar masa tace “babana kai ne da ranar nan”.
Shima Murmushin yayi yana sosai sunkuyar da kan sa yace “Ina wuni”.
Da fara’a sosai tace “lafiya qalau babana ya mutanen gidan”.
Dan sosa girar sa yayi da key din hannun sa yace “duk Alhamdulillah”.
Gyada Kai tayi tace “Maa sha Allah”.
A nutse yace “dama zamu koma yau ne a sake duba hannun”.
Murmushi tayi tace “Allah yayi maka albarka ni na manta ma, bara na dan kintsa ko”.
Kallon Aasmaa tai wacce take zaune ta zira hijab ta hade girar sama da ta kasa tana danna waya.
Murmushi Umma tayi tana kallo ta tace “ki shirya ko Aasmaa sai muje tare”.
Daga Kai kawai nayi na mike na shige ciki.
Shima koma wa yai tsakar gidan ya tsaya yana danna wayar sa.
Ni da Umman muka fito a tare Ina rufe dakin da key, kallon Umma nayi nace Umma “amma fa su Yaya da Maryam sun ce zasu zo yau gashi kuma zamu fita”.
“Toh ai sai a bawa Sani mai shigo key din ko, in sun zo sai su karba”.
Daga kai nayi kawai Ina riko mata jakar ta.
Fita yai muka mara masa baya, shi da Umma sukai gaba ni kuma na tsaya na kulle gidan sannan na mika wa Sani key din.
Tafiya nake a nutse ina dan gyara zaman hijab dina har na fito daga layin, idona ne ya sauka akan wata lafiyayyar mota baka sai daukar ido take tana kwalli kamar wacce aka shafawa mai.
Fito wa yai daga motar yana kallo na a dake yace ke naje jira fa.
Tabe baki nai kamar ban ji mai yace ba na nufi motar, hannu nasa na bude baya zan zauna Umma tace “toh shi driver din ki ne da zaki zauna a baya shi yana tuka ki”.
Kamar zanyi kuka nace “Umma kawai sai na zauna a gefen sa salon ya sake rai na ni.
Tsaki Umma tai tace “matsa na sauka ni Aasmaa na koma gaba, yaron nan bashi ne ya kade ni ba amma dubi yadda yake tsaye akan lafiya ta har kudin asibitun shi ya biya amma kike son wulakanta sa Aasmaa”.
Da sauri na sauka Ina cewa “yi hakuri Umma bara na shiga gaban”.
Motar shiru ba Wanda yake magana har muka isa asibitin, tun daga wajen zaka fahimci na kudi ne.
Ni dai nawa ido har muka shiga aka duba muka fito, a hanyar mu ta koma wa ne wayar sa ta shiga ringing.
Kasancewar wayar tana tsakiyar mu yasa na dan juya a nutse na kalli wayar, haka kurin gaba na ya fadi ganin anyi saving da Wife da emoji na heart a gaba.
Shima juyo wa yai ya dauki wayar idon sa a cikin nata yana kallon ta, yadda ta bisa da ido sai abin ya dan basa mamaki amma ya waske yana sa wayar a speaker.
Cikin shagwaba Yusrah tace “Assalamu alaikum Yayana”.
Murmushi ya saki wanda hakan ya baiyana jerarrun hakoran sa yace “Waalaikumussalam Wifey”.
Lumshe ido Yusrah tai tana jin wani nishadi da farin ciki, gaba daya Yayan nata sauya mata yake yi haka kurin lokacin daya zo part din Mummy yace wai ta fito suyi zance, haka ta fito sai sussunkuyar da kai take cikin kunya a lokacin ne ya bata wayar sa yace tayi saving numbern ta da sunan da take so ya ringa kiran ta, har tasa baby sai taga kamar tayi rashin kunya kawai tasa wifey da heart a gaba ta gudu daki.
Tun lokacin ne ya dai na kiran ta da Yusrah sai dai Wifey wanda wannan sunan ba karamin farin ciki yake sata ba.
Teemah ita ma data zubar da Kayan yakin ta tun da Meena tayi wa Mami rashin kunya ta dawo ta jone da Yusrahn ce ta zunguri Yusrah din cikin mamakin wai yayan nasu ke kiran Yusrah da wifey.
Cikin rawar murya tace “uhmm dama dama su Teemah ne da Ya Waleeda suka ce wai zaka zo dinner din sbd asan yadda za’a tsara, da sauri ta ce ni dai nace ba ruwana baka so amma sun ce dole na tambaye ka”.
Dan lumshe ido yai yana kallon Aasmaa wacce ta mugun hade rai tana kallon titi, murmushi ya saki yana gyaran murya yace “uhmm ke kina so nazo neh”.
Waro ido Yusrah tayi tana rufe wa Teemah baki wacce take kokarin sakin Ihu, cikin inda inda tace “me zai hana Yayanaa”
Gyada kai yayi yace “an gama Wifey amma part din abinci kar kusa