Showing 3001 words to 6000 words out of 62917 words

Chapter 2 - AMJAD COMPLETED Complete Hausa Novels by DIJENSY.txt

DIJENSY   

14 Jan 2025

5785

karin kumallo,Fauzan ma na wasanshi a tsakar gida su kuwa Maryam da Nusaiba suna wanke kwanuka.Baba kuwa yana d'aki kwance yana jiyo hayaniyar yaran.


Kwan ! kwan! Suka jiyo bugun 'kofa daga waje,sallamar da akayi neh tasa suka sheda mey maganar.


"Kawu ina kwana".Yaran suka fad'a bayan an bud'e 'kofar ya shigo ciki.


" lafiya".Ya amsa.


"Ina Baban naku?" Ya tambaya.


"Yana ciki ". Suka amsa.Da sauri ya 'karasa d'akin,Mami kamar yadda tayi tsammani hannunsa ri'ke 'kulli-'kullin magunguna.


" Za'a sake kwankwad'a masa wasu kenan"Laila ta fad'a bayan ya shigesu.


"Idan ya jiyoki ba ruwana ,kiyi aikin dake gabanki atoh". Cewar Mami tana cigaba da sakin fanke.


" Fad'imatu!" Taji Kawu ya 'kwalo mata kira.A gigice ta tashi dan ta mugun razana tsoronta kar ko wani abu ne ya samu Baba amma tana zuwa taga ba haka ba."Jiya kin bashi maganin da Laila tazo ta amsa guna?"Yadda yake maganar cikeda tuhuma.


"Ehyi Kawu an bashi"


"Allah yasa dan naga jikin ba 'kwari ina 'ko'karin zaunar dashi ma abu ya gagara ko dama ya jima a hakan?"

"Jiyane de be samu ya iya zaman ba"


"Toh ga wani maganin na kawo yanzunnan za'a bashi yasha d'akko kofi a tsiyaya"


Da "Toh" ta amsa ,bayan da aka kawo kofin ya tsiyaye maganin,tallafo shi yayi da 'kyar tukun ya kafa masa.


"Ka daure kasha ko ka samu 'kwari"Kawu ya fad'a.Baba da ba yadda zeyi haka ya 'kwan'kwad'e.


Maidashi yayi ya kwantar se nishi yake d'an mi'kewar da yayi yasa yake jin wata wahalar."Sannu" shine abinda suke fad'a,da'kyar yake gid'a kai.


Canada


8:20am,dukansu sun hallara a dinning table suna breakfast chair na Amjad kuwa empty ba shi babu batunsa.


"Where is Amjad?" Dad ya tambaya yana kallon Shaheed.


"Uhh..in his room"Mom ta amsa cikin in'ina


"Sleeping right?"Yadda yayi maganar yasa dukansu sukai shiru , ta sunki da kanta 'kasa ba tare da ta sake cewa komai ba .


A fusace ya mi'ke daga kujerar ya dire spoon d'in hannunsa,ko ba'a fad'a ba Mom tasan d'akin Amjad ya nufa.Itama tashi tayi tabi bayansa tana 'ko'karin tsayar dashi.


" Honey stop! Honey listen to me"


Banza yayi da ita ya cigaba da tafiyarsa har ya 'karasa 'kofar d'akin dede zeyi knocking wayarsa tayi ringing.


Da alama kiran mey mahimmanci ne haka yasa ya sauka 'kasa.Dad'i taji ganin haka dan tasan da ya shiga d'akin rai ze 'baci kuwa.


Da kanta ta Shiga d'akin,ya 'kudundune da blanket se sharar bacci yake.


"Amjad,wake up it's almost 9am" Ta fad'a a hankali tana tapping shoulder d'insa.


A hankali ya motsa memakon taga ya bud'e idanunsa a'a se ya juya fuskarsa d'ayan side d'in.


"Amjad! Your dad is here"


"Uhmm" Ya fad'a a ciki-ciki.


"I said wake up"


"Mom please,30min more.."


"Amjad!" Ta kira da 'karfi.


Da'kyar ya tashi yana mirza idanuwansa da suka 'kan'kance tsabar bacci daya taru yana kunbure- kunbure.


"Ya tashi " Ta fad'a bayan ta sakko 'kasa.


"Better" Daga haka ya koma d'aki.


Sanda Amjad ya sauko Dad ya bar dinning d'in,hankalinsa kwance yayi breakfast d'insa kowa ya tashi ya barshi.A zuciyarsa yana jin dad'in tafiyar da Dad zeyi zuwa Paris yasan zey samu ya sarara ba takura zeyi abinda yake so.


kano


Wajajen 2:30pm Laila ta gama shirinta cikin uniform d'in islamiyya,fuskarta ba wani makeup amma hakan be hana kyawunta fitowa ba,eyelashes nata zara-zara da girarta me matu'kar had'uwa very thick ga curve ,lips nata dede ga dogon hanci ,ganshinta kuwa tayi parking ,ko powder bata sa ba amma farar fatanta bebar haskakawa ba(kwatancen laila zey ja lokaci shiyasa kawai aka d'anyi description kad'an)


Yawanci kullum tana riga su shiryawa shiyasa wasu lokutan bata jiransu.


"Maryam!" Ta 'kwala mata kira.


"Kinsan ba jiranku zanyi ba kuna gani uku ya kusa zanyi tafiyata idan bakuyi sauri kun shirya ba"


"Yanzu fa zamu shirya"


"Banga alamar hakan ba ai" Ta bita da harara."Seki je ki kirasu Nusaiban"


Basu suka fito daga gida ba se 2:54pm,se dungure musu kai take tana balbalesu da masifa.Daba ace Mami ce ta takura su tafi tare ba da bata jira su ba.


Canada


4pm Dad ya tafi zuwa Paris, Shaheed da Zakia se Mom suka raka shi har airport banda Amjad da yana gida duniya tai dad'i Dad is not home dukda kuwa ya sake ja masa kunne akan zuwa party da 'kin yin sallah akan lokaci.


★★★★


*How is the chapter?? Want hear from you, more comment more updates.Love you all💋*


*Vote★*
*Comment📝*
*Share💭*


*Dijensy*❤































🌼🌼 🌼🌼




💦 💦




*AMJAD*




💦 💦






🌼🌼 🌼🌼




*WRITTEN BY DIJENSY*


*WATTPAD:@dijensy*


*DEDICATED TO FATIMA² FWEND★*





🅿 0⃣2⃣
Canada


8:30pm,suna dining Mom,Zakia da Shaheed kowa kawai de cin abincinsa yake wannan kusan duk ranar da Dad yayi tafiya haka sike saboda yana da wasa da dariya cikin familyn nashi amma dukda haka Amjad besa ya dena ganin tsananta masa da Dad yake ba,shi a ganinsa ya takura masa.


Suna zaunen ne Amjad ya sakko ,ya ma'kala earphones a kunne se bin wa'kar yake hankalinsa kwance yaja kujera ya zauna.Gabad'aya kallo suka bishi dashi dan sun gano dalilin farincikinsa,jin kallon ya isheshi yace.


"Sorry guys ,I forgot to say hi to you is that it?"


Kai kawai Shaheed ya girgiza ya tashi,Zakia kam ta'be baki tayi ta cigaba da cin abincinta.


"Amjad you're happy Dad is not here right"Mom ta fad'a.


"Ahn?" Ya zare earpiece d'aya dan beji mey tace ba.


"I said you're happy Dad is not here right?"


"Why should I not, he's always harassing me ,am glad now he's not home no more harrasing I wish he could stay there for 6month"
Ya 'kare maganar a ciki-ciki


"Because you want to enjoy parting hanging around with silly boys like you " Zakia na gama fad'a tayi sauri ta gudu d'aki dan idan ta tsaya seya daki bakinta.


"Mom did you heard that? I can't tolerate nonsense!"


"Come on eat forget about what she just said,she's sad Dad is not home"


'Kwafa yayi ya cigaba da cin abincin tare da 'karo volume d'in wa'kar.Kowa d'akinsa ya wuce ,Amjad like always ya kunna laptop sede yau video call ya shiga yi da farko da wani friend d'inshi Sam ya fara bayan ya gama labarta masa Dad yayi tafiya kuma ya soma yi da wata beb.


"Hi Rosie" Ya kirata fuskarsa d'auke da murmushi.


"How you doing ?"


"Am ohk" Ta amsa.


"But you don't seems to be ok" Ya amsa cikin sanyin murya.


Cikeda iyayi irin tasu ta turawa tayi rolling eyes tare da sauke numfashi kafin tace."Am just having a hard time here in London am tired I need to come back to Canada " Ta 'kare maganar tana sa'kale gashinta bayan kunne.


"I knew it,you won't like staying there how could that even be so possible I know you missed me"


"Yeah I do,and you?"


"Do you have to ask ?"


Murmushi kawkawai yi ba tare da tace komai ba."Now what's your decision are you going to stay there or you have changed your mind?"


"Well,you know I can't live without you,why will you even expect me to stay there? It's not that easy" Ta 'kare maganar kamar zatai kuka.


"It's all over now,everything is gonna be ok"


"Yeah"


"Amjad"Ta kira sunanshi.


"Huh?"


"I'am sorry,i'am sorry for hurting you so bad for living without even saying goodbye".


"Shh! Stop apologizing, I know you won't left me it's just that you need to have some space at that time, I was also wrong to treated you like that,i'am also sorry"


Kai kawai take gid'awa dan a yanzun kuka yaci 'karfinta se gogewa take amma ya'ki 'karewa.


"Please stop crying everything is fine"


"Yeah I know,I just can't hold it"


"You can ,look at me "


A hankali ta d'ago kamar yana gabanta kuwa idanuwan sunyi jazir ga kumburi da sukai fuskar ma tayi red.


"I love you"Ya fad'a.


Wani farinciki taji ya shiga zuciyarta kukan ma ta nemeshi ta rasa duk da kuwa ba yaune first time daya fad'a mata hakan ba, kawai de tayi missing words d'in daga bakinsa.


" I love you too" Tayi 'ko'karin amsa wa,tuni ta mance da komai suka shiga hirarsu ta masoya.


Rosie, tare sukai makaranta da Amjad tun suna teens da farko friendship suke ba ala'kar soyayya amma daga baya soyayya mey 'karfi ta shiga tsakaninsu.Watarana suka samu sa'bani sakamakon wani saurayi daya ganta dashi,ko explaining be bari tayi masa ba ya hau fishi da ita hakan yasa tayi zuciya ta koma wajen mahaifiyarta da zama wadda take a London ,Amjad se ji yayi ta tafi ,1month da faruwar hakan du zaman ya isheta tayi missing d'inshi idan ta kirashi baya picking se yanzun taci sa'a ya nemeta.


Kano,9:15pm


Mami ce zaune kusa da Baba se fifita take masa,ga abinci a gefe ya kasa ko loma d'aya.


"Ina yaran?"Ya tambaya murya a dashe.


" Sun kwanta bacci".


"Taso su" Ya fad'a.


"A taso su" Ta nanata taji banbara'kwai dan shine me hanawa a tashi wani yana bacci.


Tashi tayi jiki a sanyaye ta shiga d'akin yaran d'aya bayan d'aya ta tashesu ,Nusaiba da nauyin bacci se rife ido take.


"Laila kuje babanku yana kiran ku"


"Kira?"


"Eh kuje yanzu"


Su biyu suna biye da ita a baya banda Nusaiba da tana ganin fitarsu ta koma baccin ta.Suna shiga suka zauna bisa shinfi'darsa.


"Au Nusaiba komawa baccin tayi?" Mami ta fad'a bayan data lura bata gun ,tashi tayi da niyyar kiranta Baba yace ta rabu da ita.


"Laila,Maryam" Ya kira sunansu.


"Na'am Baba" A tare suka amsa.


"Ina so ku kasance masu biyayya ga mahaifiyarku da 'yan uwana duk da nasan kuna yi amma zanso ace kun dad'a a kai" Dukansu jikinsu yayi sanyi jin irin kalamansa.


"Koda ace bana duniya kada ku d'auka cewa baku da mey fad'a kuji ,yayyina d'aya sike dani a gunku suma iyayenku neh kunji koh ?"


"Toh Baba" Maryam ta amsa.Ita kuwa Laila kuka ne yake nema ya ku'buce mata zuciyarta tayi matu'kar karaya.


"Laila kece babba a cikin yarana,'kannanki sune masu koyi dake ,kece abokiyar shawarar mahaifiyar ki .." Tari ne ya katsesa ya kasa cigaba da magana.


"Sannu Baba" Ruwan dake cikin jug Mami ta tsiyaya a cup ta bashi yasha kad'an.


"Kuyi ha'kuri" Suka ji ya fad'a.


Shiru d'akin bame magana har kusan 10min,ganin haka Mami tace su koma su kwanta. Laila tana fita daga d'akin ta koma gefen 'kofa tayi zaman dirshan Maryam ta shiga d'aki ta barta duk da ita ma ba barci ta koma ba.


"Sannu" Ta jiyo muryar Mami tana fad'a dan tarinsa ya tsananta.Zuciyarta sai dukan uku-uku take da tayi yun'kurin shiga d'akin seta kasa wani tsoro take ji yana sake shigarta.


"Baba" Take ta ambata a hankali.


Ganin yadda Mami ta fito a kid'ime yasa tayi saurin mi'kewa a firgice."Laila zanje na kira kawun ku"


Bata jira jin abinda zata ce ba ta fita daga gida ,Laila da sauri ta shiga d'akin ta tarar dashi yana ta numfarfashi.


"Baba" Ta zauna tare da ri'ko hannunsa ta had'a da nata tafin,hawaye ne kawai yake 'kwaranya a fuskarta ta rasa ina zata sa kanta itade tunda take bata ta'ba shiga tashin hankali kamar wannan ba.


Sunkui da kai tayi ta dafe goshinta da hannunsa had'e da nata,Maryam ce ta shigo itama ganin yanayin da Laila ta shiga tasa kuka."Ina Mami ta tafi?"


Ta kasa ko amsa mata har yanzu kanta a sunkuye yake,10min later sega Mami ta dawo tare da Kawu Yunusa.'Karasowa yayi inda yake ya du'ka a sanyaye.


"Mustafa" Ya kira sunansa.


Laila se lokacin ta d'ago ta dubi Baba tana jira ya amsa.Hannunsa data ri'ke taji yayi nauyi."Baba" Ta kira a raunane.Ta kira yafi sau uku amma shiru,kawu ne ya ri'ko hannunsa daga bisani kuma ya maida.


"Innalillahi wainna ialihi raji'un" Abinda ya furta kenan.


"Fad'imatu sede mi ha'kuri amma Yunusa Allah ya d'auki abinsa"


Jitai kunnuwanta ya toshe idanunta kuwa sun soma dena gani ko kukan ma ta dena ,tana kallo Mami tai zaman dirshan take ta soma kuka.Innalillahi wainna ilaihirraji'un.


Maryam ma kukan nata ne ya sake 'karuwa,Nusaiba daga d'aki tajiyo su kamar a mafarki ,zinbir ta tashi tayo waje.Wajen Mami tazo ta 'kan'kameta tasa kuka ganin Mami na kuka da Maryam.


"Kawu a tafi asibiti bafa mutuwa yayi ba" Suka jiyo muryar Laila, ba wanda ya tanka mata dan sunga zafin mutuwa ne ya doke ta.


Washegari


Duk cikinsu ba wanda ya iya bacci har gari ya waye,a jiyan dama Kawu ya kira wasu 'yan uwa ya sanar musu da rasuwar saboda haka da asuba suka fara zuwa.


Laila ba ita ta tabbatar da Baba ya rasu ba seda taga gida ya cika da jama'a,nan ta dasa nata kukan ta shige d'aki.Lokacin da aka zo fita da gawarshi seda kawu ya korata ita a lalle seta bisu an kaishi da ita.


'Yan uwan Mami sukai ta rarrashin yaran suna basu ha'kuri.


Kawu Yunusa ne ya samu ya kira Dad a waya ya sanar masa da rasuwar d'an uwan nasu.Yaji mutuwar sosai,Mami tana zaune aka kawo mata wayar sukai wa juna gaisuwa daga bisani sukai sallama,zuwa Nigeria ya kamashi gashi yayi tafiya dan a yanzun ya shiga busy akan aikinsa sosai.


Canada, 4pm


Yau Sam ya kawo ziyara wajen Amjad,Sam d'aya daga ciki abokansa ne na yarinta tare sike rashin jinsu da yawo he is one of his craziest friend.


Da Sam da Shaheed duka suna d'akin Amjad wai zasu gwada wrestling Amjad ne rep Sam da Shaheed sune players duk sun 'kwa'be rigar jikinsu.


Wani rectangular plane katako suka d'ora kan kujeru biyu at each end.Amjad ya tsaya daga gefe suna jira ya busa 'kusur.Fittt! Suka soma,kowa burinsa ya d'aga wani ya danfara a kan fence d'in,daga yadda 'kirar Sam take za'a gano cewa yafi Shaheed 'karfi.Chancharas ya d'aga Shaheed ,se wutsul -wutsul yake Amjad yana ta dariya hadda ri'ke ciki.Yana ji yana gani ya damfarasa akai hatta katakon seda ya ragargaje kujerun kwa suka fad'i ,Shaheed ko motsi da'kyar yake ya ri'ke 'kwan'kwaso se juyi yake.


"I caught that on camera" Amjad ya fad'a.


"Dude are you alright?" Sam ya tambaya yana dariya.


"Aghh,Mom!" Ya 'kwala mata kira.


Ba dad'ewa kuwa sega ta ta shigo,hannu ta d'ora a baki tana waro ido."Oh my god ,what did they do to you Shaheed ?"Ta 'karasa inda yake ta rasa ma ta ina zata soma taimaka masa ya mi'ke.


"Guys this is crazy,look at him he's hurt"


"Mom he's gonna be ok" Cewar Amjad.


Da'kyar ya samu ya mi'ke suna had'a ido dashi suka she'ke da dariya.


"Shut up! This is not funny,Amjad this is nonsense behave yourself don't let that happen again" Tana gama fad'ar haka ta fice, Shaheed yana biye da ita se dafe baya yake ,bayan yayi jazir.


Ganin Mom bata ji dad'in abinda sukai ba ya tsagaita da dariyar.


Seda ta daddana masa ice block shima tana yi tana dungure masa kai,da be kula su ba da hakan be faru ba.


"Don't ever try this again,this is stupid"


Shide ya sunkuyar da kai a zuciyarsa yana tsara ramuwar da zeyi musu shima,gashi sunyi video zasi yad'a shi.


Landline na sitting room da yayi ringing yasa ta mi'ke dan amsa kiran.


"Innalillahi wainna ilaihirraji'un"Ta furta bayan Dad ya sanar mata da rasuwan.


" Sorry for your lost,I felt sorry for his family may his soul rest in peace
May Allah grant him jannatul Firdausi.


"Ameen" Dad ya amsa daga d'ayan 'bangaren.


"Mom,what happened?" Zakia ta tambaya dede lokacin ta dawo daga school taji tana wayar.


"Your uncle, he's gone"


"Uncle mustafa?"


"Yes"


"Uhh,may his soul rest in peace, I will call Dad"


"Yes you have to, am gonna call his wife Fatima"


A take ta kirata aka ci sa'a wayar tana kusa,cikin harshen hausa ta soma mata gaisuwa.


"Allah yaji 'kanshi yasa ya huta"


"Ameen,nagode" Mami ta amsa murya a sanyaye.


"InshaAllah muna nan zuwa ,ki gaida yara a basu ha'kuri"


"Zasi ji,nagode "


Amjad da tunda ta fara wayar da Mami ya jingina a bango ya wani folding arms yana jiran ta gama wayar dan ba jin abinda take fad'a yake ba,when it comes to Mom wajen hausa to bafa ya tsintar komai amma idan Zakia ce ko Shaheed toh yakan tsinci kad'an shima da 'kyar.Rashin iya hausarshi ya samo asali ne dalilin boarding school da yayi,sukuwa sauran Suna gida duk sanda Dad da Mom suka juya magana da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login