Showing 6001 words to 9000 words out of 62917 words

Chapter 3 - AMJAD COMPLETED Complete Hausa Novels by DIJENSY.txt

DIJENSY   

14 Jan 2025

5783

Hausa sukan tsinci wani abun kuma shima Dad yana 'ko'kari yaga sun koya.


"Where is he?"


"Who?"


"Sam"


"He just left"


"Amjad you have to be careful,this should be the last time ,don't let that happen again,Shaheed is your bro why do you like hurting him?


" Ok,ok it won't happen again "


"I hope so"


Har zata wuce ta tuna ta dawo."Your uncle is gone,you should call your Dad"


"He died, When?"


"Last night"


Kai ya jinjina tare da d'age gira."may Allah grant him Janna".


"Ameen".


Kano


Haka ranar Suka wuni duk cikinsu ba wanda yasa abu a bakinsa se Fauzan da be mallaki hankalinsa ba.Laila dan tsabar kuka har zazza'bi ne ya rife ta gashi ta'ki cin komai shiyasa ta galabaita tana kwance 'kuryar d'aki ,tunanin tsahon rayuwar da suka d'auke tare da mahaifinsu tayi -tayi da 'karshen maganar da yai musu.


Ko 'yan islamiyyarsu da suka zo gaisuwa da 'kyar ta samu ta iya fitowa tsakar gida,data lura da Mami taga yadda ta sake ramewa fiye da da.


2weeks later


11:23pm


Dad kwana biyu da dawowarsa Canada gobe zasi je Nigeria dukansu, shirye-shiryen tafiya suke yi ,d'akin Zakia Mom ta shiga dan dubawa ko ta gama nasu shirin dan jirgin safe ne dasu .Kamar yadda tayi tsammani taga ta gama shirya kayanta,koda ta duba Amjad shi video call d'inshi yake da Rosie.


Ganin shigowarta yasa ya katse kiran sukai sallama.


"Amjad,what are you doing you didn't park your things?"


"Are we really travelling?"Ya tambaya cikeda rainin wayo.


" Yes,you should have park your things our flight is 7am"


"What!" Ya mi'ke tsaye.


"I don't wanna go anymore"


"And you must,it's necessary put this in your head better park your sh*t now!"


"Mom!"Bata saurareshi ba tayi ficewarta ta barshi.


"F*ck up!"Ya daki cloth set dake jingine.


" Nigeria Nigeria ,hot! hot ! hot and that fucking little sh*t(mosquito๐Ÿ˜‚),damn it! Shi kad'ai yake masife-masifensa kafin daga bisani ya bud'e cloth set d'in.


Kano


Yau su Laila suka koma makaranta ita da Maryam suko Nusaiba da Fauzan ana yin kwana ba'kwai washegari suka koma,suma su Laila saboda 'yan gaisuwa yasa Mami tace su bari yau.


Laila tayi mugun ramewa seda akai da gaske ta dena zama da yunwa ,fuskarta har yanzu da nuna damuwa a tattare da ita.


"Kun fito kenan?"


"Eh Mami" Suka amsa ta.


"Toh se kun dawo"Daga haka suka tafi.


โ˜…โ˜…โ˜…


Amjad bayan daya gama jera kayan daya ke bu'kata ya suri jacket a hankali ya salalla'ba ya fice daga d'akin, a sitting room ma da sand'a ya bud'e 'kofa ya fice.Wayarsa ya d'akko a aljihu ya danna was Sam kira yake fad'a masa ya fito dama sun had'a appointment.Mintina 'kalilan ya 'karaso daga can nesa yayi parking motarsa yadda bame jinsu,cikin sassarfa ya 'karasa wajen beyi wata-wata ba ya bud'e 'kofar ya shige abinsa.


"Man,where are we going?" Sam ya tambaya.


"Rosie"


"Then let's go to club first, later I drop you to Rosie's home"


"No,it's getting late it's 12am already"


"Come on we are not gonna spend much time there"


"Alright, then
get going"


A wani haukace ya suresu kafin daga bisani ya seseta tu'kin,Amjad ko jikinsa inde wannan ne ya saba.


Seda suka fara zuwa club kamar yadda Sam yace,nan suka had'u da abokanan shashancinsu sukai ta shirmensu,masu rawa nayi masu drinking nayi shide duk yadda yakai ga zuwa club ko sau d'aya be ta'ba shan wine ba rawa de za'ai iya son rai.


Basu suka fita ba se 1:30am,da'kyar ya samu ya janyo Sam suka fita dan already he's drunk suna fitowa kuwa ya soma she'ka amai,se tangali yake kamar sabon mahaukaci.Key ya kar'be daga hannunsa dan yasan a halin daya ke ciki baze iya tu'kasu ba.Direct gidansu Rosie yayi parking,bayan ya fito daga motar ya kirata a waya lokacin bacci take cikin magagi tayi picking.


"Hello" Muryarta 'kasa-'kasa.


"Am outside"


"Amjad,is that you?"


"Yeah"


"Seriously?"


"Don't you believed me? look outside the window"


Tashi tayi ta le'ko ta window d'in ta hango shi jingine da mota take ta saki murmushi, da sauri ta fito tana sanye da dogon wando wanda da kad'an ya wuce gwiwa se wata vest gashin kan a barbaje kan kafad'arta.Fuskarta d'auke da murmushi har ha'kwaranta suna bayyana.


Tana 'karasowa tai hugging d'insa ."Are you really travelling? "Ta fad'a bayan sunyi breaking hug d'in.


"Who told you?" Ya tambaya tare da furrowing eyes yana mey mamakin wanda ya fad'a mata.


Kallonta ta mayar kan Sam dake cikin mota yana shargar bacci."So he is the one"Ya fad'a bayan ya dawo da kallonsa gareta.


"Yeah"


"I won't take so long there"


"What about your family? are they gonna stay there for long"


"I think so"


Daga nan suka d'are kan mota hand in hand suka shiga hirarsu,se 2:14pm ya tafi gida Sam a haka ya 'karasa gida da rabin hankali.


Washegari


7am flight d'insu ya tashi ,kafin su 'karasa kowa ya gaji,Amjad tuni annurin fuskarsa ya d'auke ,driver Dad yayi kira a waya lokaci 'kalilan ya 'karaso.Yana jinsu suna 'yan maganganunsu ko tanka musu ya'ki yi har suka 'karasa mansion d'insu,Mom mamaki neh ya kamata ganin gidan tsaf.


"Honey how..?"


"Surprise right?" Cewar Dad d'auke da murmushi.


"Yeah"


Tun a jiya Dad yasa a gyara gidan dan yasha 'kura saboda tsahon lokacin da aka d'auka ba'a zauna ba.


D'akinsa ya wuce direct ga yunwa dayake ji amma bama ya sha'awar cin abincin.


Driver Dad yasa ya siyo musu abinci kafin siyi settling kuma,Shaheed, Zakia kowa ya shiga d'akinsa bayan sunci abincin shikuwa 'kinci yayi ya kwanta da yunwa.Da safe kuwa da wuri ya farka dan yunwa ,kitchen ya nufa direct Allah ya taimaka yaga fridge a cike da kayayyakin ci.Bowl ya d'auka ya had'a cornflakes stool yaja ya zauna ya soma sha.


"Son" Yaji Mom ta kira sunanshi sanda ta shigo kitchen.


"Morning" Ya gaisheta.


"Yunwa koh?" Seda ya d'an yi nazari tukun ya tuna mey hakan yake nufi.


"Uhmm" Ya amsa.


"I made you a toasted bread"Ta fad'a tana 'karasawa ta d'akko masa.


Se lokacin ya kalli clock d'in dake ma'kale a kitchen d'in yaga 8:34am.Su kuwa tun tuni sunyi breakfast d'insu ma,da sauri yaci ya koma d'aki yayo alwala ya tada sallah.


Se around 11am ya fito bayan yayi shower baccinsa ya koma,yana sakkowa 'kasa ya tarar dasu duka a sitting room.


" Morning Dad"Ya gaishesa.


"Morning" Ya amsa.


"Yaushe zamu je?" Mom ta tambayi Dad.


"Anjima zamu"


"Gidan late Uncle?" Zakia ta tambaya.


"Ehyi"


Shi sam ba son wannan hausar da sukeyi yake ba,sede yayi ta kallon bakinsu,tunanin yadda zey tsara tambayar mey suke cewa ya shiga yi amma fa da yaran Hausa,yafi minti uku yana tsara abin fad'e kafin yai gyaran murya.


"Mey cewa kukai?"Ya fad'a da confidence d'inshi.


Gabaki d'ayansu ba wanda beyi dariya ba,Zakia hadda ri'ke ciki dan dariya.Tuni ransa ya 'bace duk wannan tsare-tsaren shine zasi 'bige da dariya ,pillow na kan sofa d'in ya d'auka ya wurga wa Shaheed a fuska ya tashi ya koma d'aki.


Ganin haka Mom ta tsagaita da dariyar ta fara kiran sunanshi amma yayi burus.


" It's ok guys,enough please"


"Wani yasa ya kasa koya ,dole miyi masa dariya the next time yayi abinda yafi haka wani dariyan zamiyi +shame shame "Dad ya fad'a.


Tashi tayi ta nufi d'akin sa." Come in" Bayan tayi knocking.


"A zaune ta tarar dashi kan gadon yana tapping phone d'insa be ko kallo wajen ba.Zama tayi kusa dashi ta dafa kafad'arsa " Son we are sorry"


"You don't have to"


Ohh sweetheart ,you even try there is nothing wrong there it's just that you misplaced the words"


"Then you correct me not laugh"


"It won't happen again"


"Do you want learn the.."


"Not anymore" Ya katseta.


"No son it's good to ,what if you are to stay in Nigeria?"


"God forbid"Yayi saurin fad'a.


" Who knows if.." "


"Mom please stop it,I don't like talking about it,am not staying in any other country apart from were I was raised"


"Am joking ,don't worry" Ta fad'a tare da tallafoshi sekace 'karamin yaro.


4pm suka nufi gidansu Laila,aiko ranar an tashi da rana duk da a cikin mota suke Amjad be fasa complaining ba har suka isa gidan.Mami tana tsakar gida taji sallama,tana bud'e musu 'kofa wa zata gani.Iso tayi musu suka 'karaso har ciki ta sauke su a d'an 'karamin parlonsu inda aka ci sa'a ma daakwaia wuta ta kunna musu fanka,su Laila kuwa dukansu suna makarantar islamiyya.


*Dijensyโค*
๐ŸŒผ๐ŸŒผ ๐ŸŒผ๐ŸŒผ




๐Ÿ’ฆ ๐Ÿ’ฆ




*AMJAD*




๐Ÿ’ฆ ๐Ÿ’ฆ






๐ŸŒผ๐ŸŒผ ๐ŸŒผ๐ŸŒผ




*WRITTEN BY DIJENSY*


*WATTPAD:@dijensy*








๐Ÿ…ฟ 0โƒฃ3โƒฃ




Dukansu wuri suka samu suka zauna,Shaheed da Zakia suna zaune 2 seater se Mom da Dad da suke zaune kan 3 seater Amjad ya hakimce kan 1 seater daga can 'kuryar parlon se cin magani yake.


Cikin rissinawa yaran suka gaida Mami da yaran Hausa shima yai koyi da abinda suka ce yayi mata gaisuwa,suma Mom da Dad suka sake mata gaisuwa bayan sun gaisa.


"Ina yaran suke?" Dad ya tambaya.


"Dukansu sun tafi islamiyya nan da anjima zasu dawo"

"Allah yayi albarka" Cewar Mom.


Mami ta amsa da "Ameen".


Hira kad'an suka d'an ta'ba wanda kusan duk akan yaran nasu ne ,nan Mami take fad'a masu Laila ta kammala karatun secondary.Sun kwashe kusan 1hr tukun suka je gidan kawu Yunusa ,bayan sunyi kamar 40min Mom da yaran suka komo gidan su Laila Dad yana tare da Kawu yunusa suna tattaunawa.


Kamar yadda sukai zaman farko haka sukai yanzunma ba wanda ya chanja position, Amjad da zafi ya fara isarshi se d'aga 'kasan T-shirt d'insa yake yana firfita sekace ba fan a d'akin.


Zakia ce ta d'auki jug d'in da Mami ta kawo musu ruwa ta tsiyaya a cup ta sha,Shaheed ma ta ziba mishi sannan Mom.Mom da kanta ta ziba wa Amjad ta bashi,shide ya ri'ke a hannu amma ya'ki sha se danna phone d'insa yake.


5:43pm su Laila suka dawo gida tun daga 'kofar gida suka gane anyi ba'ki sede basu san su waye ba.


" Assalamu Alaykum"Sukai sallama.


"Daga parlor Mami ta amsa ,Nusaiba da Fauzan ne suka le'ka cikin rissinawa suka gaishesu da sauri Nusaiba ta tashi shi kuwa yaje ya ma'kale da Mami yana sunkui da kai.


" Suwaye suka zo?"Maryam ta tambayi Nusaiba.


Laila da take cire hijab bayan ta ajje bag d'inta tace"Idan kin damu kije mana ki gani"


Dama tun a islamiyya wani malaminsu ya bata haushi.


"Daga tambaya"


"Wa'annan d'innan 'yan uwan Baba ,'yan farare"Cewar Nusaiba.


" Laa kawu Abdallah "


Laila da ta gano suwa ake nufi amma tayi kamar bata sansu ba koda ta gama sauya kaya waje ta samu ta zauna 'karamar wayarta ta d'auka ta hau danne -danne.


Maryam kuwa tana gama sauya kayanta ta tafi parlorn ta gaishesu,daga gefen Mami ta d'an raku'ba ta zauna Zakia se faman murmushi take wa yaran tana ji ina ma ace sun saba.


Amjad tun shigowarsu be ko d'ago kai ba dan koda suka gaida su Shaheed ne da Zakia suka amsa hankalinsa na kan chat d'insa.


"Ina Yayarku?" Mami ta tambayi Maryam a hankali.


"Tana d'aki"


"Toh kice mata tazo su gaisa mana"


Tashi tayi taje ta fad'a mata ko uffan bata amsa ta ba.


"Yaya baki jini ba?"


"Naji karki takura min"


Wucewarta tayi ta koma "Tana ina"Mami ta tambaya.


" Wai karna dameta"


"Bari naje na doko ta wannan halin bazata fasa ba mutum ya shige 'kuryar d'aki yana miskilanci"


Mami ce ta tashi ta tafi zuwa d'akin yaran ta isketa ma ta shingid'a kan katifa abinta.


"Mey kike yi da baza ki taso ba ana kiranki?"


"Mami yanzu zanzo"


"A hakan kina kwance,tun d'azu ana tambayarku dan wula'kanci kuma seki kwanciyarki bakisan abinda ya dace kiyi ba"


Sallamar Dad tasa Mami ta fita daga d'akin,se lokacin ita kuma ta ajje wayar ta mi'ke d'ankwalin ta yafa akanta dama doguwar rigar material ce sky blue a jikinta A shape ta fito.


Daga bakin 'kofa ta tsuguna "Ina yini"


"Lafiya lau" Mom suka amsa.


"Ya 'karin ha'kuri"


"Da godiya" Ta amsa.


Zakia da Shaheed ma ta gaisa dasu banda Amjad da bata san da zamansa a d'akin ba saboda yana daga can gefe bata lura dashi ba inba wai ta shiga ciki ta zauna da kyau ba.


"Wannan itace babba ko?" Dad ya tambayi Mami.


"Eh itace Laila ,se 'kannenta " Tayi masa bayaninsu d'aya bayan d'aya.


Laila da take jinta kamar akan 'kaya da sauri ta bar d'akin ta koma.Not more than 3min sega Mami ta shigo "Keda kika zo kika zauna anan mey zami basu?"


"Ga ruwa kin basu"Ta fad'a cikin rashin nuna damuwa.


" Gidanku,ruwa abinci ne? tun d'azu fa suke nan har sunje gidan Kawunku sun dawo kuma shine zan zira musu ido"


"Toh ga tuwo nan za'a d'ora idan zasu iya jira se a sa musu"


"Waike lafiyarki lau? Idan su iyayen sunci yaran taya zasi iya ci kinsan de ba cimarsu bace" Mami ta fad'a.


"Toh ya zami musu shi mike dashi"


"A'a baza'ai haka ba,yanzu de dama miyar alayyahu zanyi kinga se'a sayo musu gurasa sauran chanji a siyo musu lemo"


"Tohh"


"Maghrib yana yi bari na aika Nusaiba ta siyo,ke kuma ki had'a miyar ina Maryam seta taya ki kuyi sauri" Mami ta fad'a daga haka ta fita.


Nusaiba ba jimawa ta siyo kayan,Laila kuma suna had'a miya kafin su kammala maghrib tayi Fauzan ne ya zuba musu ruwa a buta bayan sinyi alwala ya rakasu masjid ,su Mom suma sukai tasu sallahr a gida.


Kafin su dawo har abinci ya kammala ,komai da komai aka jero a tray Maryam ta dire a tsakkiyar parlorn.


"Sannu"Zakia ta fad'a tana murmushi.


Itama Maryam murmushin tayi ta amsa mata da" Yawwa"


Sun dawo daga masjid Amjad be shigo ba ya tsaya a waje yana iyayi shi network yake searching.


Mom ganin shigowarsu tayi serving d'insu"Amjad?"Ta tambayi Shaheed.


"Yana waje yana ganin gari"Dad ya fad'a.


D'an dariya tayi ta ziba musu juice d'in" Zakia"Ta kira sunanta tana mata nuni da ta sakko 'kasa,ba musu ta sakko shima haka Shaheed.


Seda ya gama iyaye-iyayensa tukun ya tsiri d'aukan pic ,daga bisani ya d'akko camera d'insa a mota nan ma ya hau video na area d'in.


Bata dad'e da zama ba a d'aki tajiyo knock."Mtchww! ko waye a wannan lokacin"Tana jin haushi ta tashi ta nufi 'kofar waje.


Tana bud'ewa taga mutum a tsaye,tunani ta shigayi damage tare take d'azu,ganin zata 'bata lokaci ta matsa gefe ya wuce.


"To ko tare sike ?amma ba d'aya ne namijin ba?"


Tana waiwayawa bayan ta rife 'kofar taga har ya shige parlorn.Ra'bawa yayi ya shige zuwa seater d'insa yana kallonsu suna cin abinci ya ta'be baki ,Mom data ce ya sakko yaci ya girgiza mata kai alamar a'a.


Se 8:23pm suka tashi da zimmar tafiya kan lokacin tuni Amjad ya 'kosa su tafi saboda shi ba hirar ake dashi ba shi bada cin abincin ba su Zakia suna d'an hirarsu da Shaheed amma shi dinkim kamar bebe kawai kad'a 'kafa yake.


Dad 50k ya direwa Mami bayan fitar yaran dama Mom ,Mami tayi ta godiya har 'kofar gida suka rakasu banda Laila da ta tsaya daga tsakar gida.


"Kin wani ma'kale a ciki"Mami ta fad'a.


" Toh mey zan musu?"


"Bansani ba" Ta wuce ta barta anan.


โ˜…โ˜…โ˜…


Amjad suna shiga gida ko d'aki be shiga ba ya wuce kitchen ya nemi abinda zeci,yunwa yake ji sosai amma tsantsami yasa ya'ki cin komai balle yasha.


"Amjad ,so you're hungry" Ya jiyo muryar Mom ta fad'a.


"Yeah"


"But you refused to eat .."


"I can't eat that". Ya katseta.


" What wrong with the food?"


"Nasty!"


"Nop it's yummy ,you missed it boy"


"No it's not"


"Mom"


"Yes"


"When are we going back home"


"This is home too"


"Yes!" Ya jiyo muryar Zakia tana shigowa kitchen d'in.


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login