Showing 33001 words to 36000 words out of 99740 words
Chapter 12 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf
wannan matsalar taki
karama ce. Ke kika zamar da ita babba gashi
kin cuci rayuwarki duniya da lahira. A duniya
kin jawowa kanki bashin da zai kaiki zuwa ga
kotu a daure ki, kin dauko hanyar rugurguza
karatunki. Sannan kin taba lahirarki domin
ibadae ki ta ragu saboda damuwa da kika jefa
kanki, kinje wajen boka mai duba wanda Allah
Ya haramta, duk wanda yaje wajen mai duba,
mai zuba wuri ko mai bugun kasa kuma ya
gasgata abin da ya duba ya fada masa tabbas
bashi da sallah har kwana arbain , Allah ba zai
karba ba. Idan kika mutu a tsakanin wadannan
ranakun me zaki cewa Ubangijinki? Kin zama
makaryaciya domin karairayi iri iri kike
shirgawa wanda ada ba halinki bane kuma
kinsa makomar makaryaci wuta ce. Baki kyauta
min ba farida da baki fada min matsalarki ba
har sai da komai ya cabe. Na girgiza kai nace
na hakura da dr shureim yadda iyayena suka
bar duniya na san na rabu dasu har abada
haka na rabu da shi daman bai san abinda
nake yi ba. Wallahi anty abida ba da ganfan na
dorawa kaina sonsa ba haka na tsinci kaina,
nima ba da son raina ba. Abida tace haba haba
kamar yaya zaki hakura dashi bayan wadannan
bala'I da kika fada a dalilin sonsa ai ba zai tafi
a banza ba. Nayi miki alkwarai da izinin Allah
(SWT) sai kin sami soyayyar dr shureim cikin
ruwan sanyi. Na kasa kunne ina sauraron
maganar abida tamkar tatsuniya. Na dauke ta
a matsayin mai iya zance don hankalina ya
kwanta kawai. Duk da nasan babu abin da ya
gagari Allah, amma abin da kamar wuya wai
gurguwa da auren nesa. Abida ta luta da
tunanin da nake yi a zuciyata ta ga alamar ban
yarda da abubuwan da ta fada min ba. Tace
aisha farida kin manta da yadda akayi na auri
yayanki hussaini? Kin manta ra'ayinsa na son
girma ba zai auri kanwarsa ba a lokacin da
iyayenmu suka yi sha'awar hadamu aure yake
kokarin bijirewa? Kin manta yadda muka fara
zama dashi a gidan nan, ni dake muna
tsoronsa ko muryarsa muakji jikinmu sai ya
dau rawa muna guje guje? Yaya kika ga
zamana dashi a yanzu? Bari in fada miki
abinda baki sani ba farida, yayanki hussaini a
tafin hannuna yake yanzu idan naso in daga shi
sama, idan naki sai in kifa shi kasa ya fado.
Yaya hussaini a halin yanzu baya iya bacci
idan ina fushi dashi sai ya bani hakuri na
hakura sannan hankalinsa yake kwanciya.
Hussaini baya boye min komau na game da
samunsa, baya boye min duk halin da yake ciki
na game da abokan sa zuwa danginsa balle
'yan matan waje domub mazan zamaninan
ba'a rasa su da 'yan matan zamani, ko basu ce
suna sonsu ba su 'yan matan zasu kawo
kansu. Ki tambaye ni ya akayi haka ta faru? Ta
ina na samo kansa? Farida wallahi ban taba
zuwa wajen wani boka ko malami ba nace ina
neman a mallake min hussaini. Mutane suna
mamakina yadda nake tankwasa hussaini yake
yin abinda nake so, har wasu kawayena da
'yanuwana suke tsokana ta wai ina hada su da
malamina wanda ya tankwara min hussaini.
Idan na fada musu ban taba zuwa wajen wani
malami ba a rayuwata sai suki yadda. Aisha
farida bana addua har karshen rayuwata in
taka kafata wajen wani malami ko boka don
yayi min adduar mallaka. Ina daga hannayena
sama in roki Allah Ya mallaka min mijina, mu
zauna lafiya, yasoni kamar yadda nake sonsa.
Na girgiza kai nace na fada cikin kuka anty
abida na hakura da dr shureim saboda bai san
halin da nake ciki ba, mutumin da baya kallon
fuskata baya amsa min gaisuwata, ta yaya zai
soni? Kawayena guda biyu har mota gare su
kyawawa ne, ko khadija bata fini kyau ba.
Maryam ta fini kyau suma dole suka gaji da
wulakancinsa suka hakura dashi. Na rasa
yadda zanyi in daina sonsa duk da adduoin da
nake kwana ina yi don Allah Ya yaye min sonsa
amma sai karuwa yake yi na fada tsaka mai
wuya, hatta da karatuna ya tabarbare saboda
sau biyu supervisor dina yana zuwa yana duba
ni daga makarantar mu bana nan. Don haka na
san in banyi da gaske ba dole sai na maimata
attachment dinnan wata shekarar. Ko a littafi
ban taba karanta labarin wacce ta fada irin
wannan matsananciyar soyayyar da na fada ba,
makauniya kuma gurbatacciyar soyayya don
bai san dani ba balle ya san abinda nake yi ba.
Sai na rushe da kuka. Abida tayi murmushi ta
dafa kafada ta sai ta girgiza ni tace haba
farida, ke macece fa, dama akwai wani da
namiji da zai baki tsoro duk haduwarsa? Ina so
ki yadda da kanki, ki dauka duk in da wata
mace ta je zaki iya zuwa, ki dauka duk abinda
tayi zaki iya yi. Ki manta da farar fatar
baturiyar da yake aure, ke bakar fata sai ki fita
a wajensa. Sai naji abida ta fara bani haushi da
wadannan maganganun nata masu kama da
almara. Na rasa yadda zanyi in fahintar da ita
waye dr shureim. Na tambaye ta cike da
damuwa ta yaya zan samu soyayyarsa, har
nafi baturiya farar fata da yake matukar so? Na
fada miki fa bai sanni ba, yana dai ganina daga
dukkan alamu ma ya tsane ni da zara ya ganni
yake hada rai. Abida ta sake yin dariya tace kin
manta kissar matan nan da akayi mana a
makarantar islamiya? Kin manta matar nan da
take wajen malami ta nemi da ya bata abinda
zata mallake mijinta. Kissar ta rabu gida biyu,
an samu sabanin malamai, sabanin malamai
kuwa rahama ce duk dai abu daya suke
nunawa. Na farko aka ce ta da ta fadawa
malamin cewar maganin mallaka take so ya
bata, sai ya umurce ta data je cikin daji ta
nemo masa gashin idon zakanya mai rai da shi
zai hada mata asirin mallaka. Matar nan ta
firgita da jin wannan babban aiki sai tace dashi
malam ina zanje in samo gashin idon zakanya
mai rai ai bazata bari a tsinka ba saboda
fadanta. Cinye mutane take yi. Malam yace shi
dai gaskiya saida wannan gashin zai iya hada
mata wannan magani. Matar nan ta tashi ta
koma gida zuciyarta cike da zullumin tadda
za'a yi ta iya cirar gashin idon dabbar da tafi
kowacce irin dabba a duniyar nan hatsari. Da
farko sai taje kasuwa ta sayi rago aka fede
mata ta dauki himilin nama ta shiga dawa, tana
hango zakanya da 'ya'yanta daga nesa suka
fita neman abinci sai taje bakin ramin ta ajiye
mata naman nan ta gudu ta labe. Da zakanya
ta dawo sai ta iske abinci lafiyayye a kofar
dakinta ita da 'ya'yanta suka taru suka ci.
Washe gari ma haka matar nan ta kawo
gyararren rago ta ajiye mata bayan ta tafi kiwo
ta sake labewa bayan ta ajiye. Zakanya taje
neman abinci ta dawo ta iske abinci har gida
suka ci ita da 'ya'yanta. Haka matar nan ta
dinga yiwa zakanya sai dai su dan matsa daga
bakin ramin don su dawo su tarar da abinci. Da
zarar sun matsa kuwa matar sai tazo ta ajiye
musu sai su dawo su tarar da abinci kamar
kullum. Zakanya ta tabbatar lallai kawai wata
mai kirki da take kyauatta mata dan haka ko
sanda taga matar ta ajiye mata abinci bata
biyo ta nemi ta lahanta ta ba. Ba sai dai tazo
taci kawai. Har suka fara sabawa tana ajiye
mata abinci a gabanta bata guduwa. Har ta kai
ta kawo matar ta fara shafa jikin zakanyar nan
bata motsawa. Tayi ta shafata don sabo har
ranan matar ta samu ta tsigi gashin idon
zakanya ba tare da zakanyar taji zafi ba. Mata
ta kaiwa malam gashin nan ya karba ya duba
ya tabbatar gashin idon zakanya ne mai rai
don yaga jini jini a jikin gashin. Sai ya cika da
mamaki ya tambayeta ta yaya akayi ta samo
gashin? shine ta bashi labarin yadda tayi.
Malam yace to haka zakije ki yiwa mijinki
kamar yadda kika yiwa wannan zakanya babu
wata mallaka da tafi hanyar nan da kika bi kika
saba da zakanyar nan. Na tambaye ta cike da
damuwa ta yaya zan samu soyayyarsa, har
nafi baturiya farar fata da yake matukar so? Na
fada miki fa bai sanni ba, yana dai ganina daga
dukkan alamu ma ya tsane ni da zara ya ganni
yake hada rai. Abida ta sake yin dariya tace kin
manta kissar matan nan da akayi mana a
makarantar islamiya? Kin manta matar nan da
take wajen malami ta nemi da ya bata abinda
zata mallake mijinta. Kissar ta rabu gida biyu,
an samu sabanin malamai, sabanin malamai
kuwa rahama ce duk dai abu daya suke
nunawa. Na farko aka ce ta da ta fadawa
malamin cewar maganin mallaka take so ya
bata, sai ya umurce ta data je cikin daji ta
nemo masa gashin idon zakanya mai rai da shi
zai hada mata asirin mallaka. Matar nan ta
firgita da jin wannan babban aiki sai tace dashi
malam ina zanje in samo gashin idon zakanya
mai rai ai bazata bari a tsinka ba saboda
fadanta. Cinye mutane take yi. Malam yace shi
dai gaskiya saida wannan gashin zai iya hada
mata wannan magani. Matar nan ta tashi ta
koma gida zuciyarta cike da zullumin tadda
za'a yi ta iya cirar gashin idon dabbar da tafi
kowacce irin dabba a duniyar nan hatsari. Da
farko sai taje kasuwa ta sayi rago aka fede
mata ta dauki himilin nama ta shiga dawa, tana
hango zakanya da 'ya'yanta daga nesa suka
fita neman abinci sai taje bakin ramin ta ajiye
mata naman nan ta gudu ta labe. Da zakanya
ta dawo sai ta iske abinci lafiyayye a kofar
dakinta ita da 'ya'yanta suka taru suka ci.
Washe gari ma haka matar nan ta kawo
gyararren rago ta ajiye mata bayan ta tafi kiwo
ta sake labewa bayan ta ajiye. Zakanya taje
neman abinci ta dawo ta iske abinci har gida
suka ci ita da 'ya'yanta. Haka matar nan ta
dinga yiwa zakanya sai dai su dan matsa daga
bakin ramin don su dawo su tarar da abinci. Da
zarar sun matsa kuwa matar sai tazo ta ajiye
musu sai su dawo su tarar da abinci kamar
kullum. Zakanya ta tabbatar lallai kawai wata
mai kirki da take kyauatta mata dan haka ko
sanda taga matar ta ajiye mata abinci bata
biyo ta nemi ta lahanta ta ba. Ba sai dai tazo
taci kawai. Har suka fara sabawa tana ajiye
mata abinci a gabanta bata guduwa. Har ta kai
ta kawo matar ta fara shafa jikin zakanyar nan
bata motsawa. Tayi ta shafata don sabo har
ranan matar ta samu ta tsigi gashin idon
zakanya ba tare da zakanyar taji zafi ba. Mata
ta kaiwa malam gashin nan ya karba ya duba
ya tabbatar gashin idon zakanya ne mai rai
don yaga jini jini a jikin gashin. Sai ya cika da
mamaki ya tambayeta ta yaya akayi ta samo
gashin? shine ta bashi labarin yadda tayi.
Malam yace to haka zakije ki yiwa mijinki
kamar yadda kika yiwa wannan zakanya babu
wata mallaka da tafi hanyar nan da kika bi kika
saba da zakanyar nan. Don haka babu wani
asiri da ci idan babu biyayya, na kaskan da kai,
ba tsabta, ba kalamai mai taushi tsakanin mata
da miji. Nima nan da kika ganni da wannan
kissar nayi amfani har na sami hussaini tamkar
jaririn da sai an dauka, sai an juya, haka zaki bi
ki samu soyayyar dr shureim. Na dube ta a
shelake nace ta yaya? Ta nisa tace zan fada
miki abubuwa guda biyar idan kika kiyaye zaki
sami shureim a garabasa ba tare da kin wahala
ba, kamar kibtawar ido da bismillah. Fardida
duk inda namiji ya kai da ji da kai, da daga kai
karshensa dai mace zai aura kuma dole ta
bautar dashi ko yaki dan kada ya bare sai yayi
dan Allah Ya wajabta akansu dole suyi. Dole ne
miji ya ciyar da matarsa, dole ne tufatar da ita,
dole ya nemo mata muhalli, dole ya kai ta
asibiti idan bata da lafiya. Idan aka sami marar
tsoron Allah wanda ba zaiyi dan Allah ba to
zaiyi ko dan kada duniya ta zageshi. Dan idan
ya bar ta cikin tsumma, ba abinci za'a nuna ta
agari ace matar wane ce baya kula da ita. Dan
haka DUK KYAN TAKALMI, duk tsadar takalmi,
ba za'a daura shi a wuya ba ko a goshi ba,
dole kafa za'a saka kuma a taka a kwata,
shiga daji, a shiga bandaki, a tako kazanta, a
taka bola ko a tako kaya dashi. To haka dr
shureim zai zama a wajenki da izinin Ubangiji,
babu boka babu malam. Naji tamkar tana busa
mi sarewa a kunnuwana saboda dadadan
bayananta, na gyara zama nace meye abu
biyar din da zan kiyaye....? Ban rufe bakina ba
sai muka ji ana buga mana kofa kamar za a
karya, hayaniyar matan da muke jiyowa daga
nesa ya matso bakin kofar dakin mu. Fadi ake
ke aisha farida, ki fito ko a balle kofar nan.
Yaya zakici kudin mutane ki shiga daki ki buya,
ga 'yan sanda nan an kira su, suna kofar gida
za'a tafi dake. Ko ki bude ko a kirawo su, su
shigo ciki su tafi dake. Na dora hannu aka na
fashe da kuka nace anty abida yaya zanyi? Na
shiga uku , yanzu ankwa 'yan sandan nan zasu
saka min su wuce dani ta gaban mutanen
unguwar nan ko kamar wacce nayi sata kowa
yana ganina ko? Hawaye ya zubo daga
idanuwanta itama, sai ta mike tsaye ta tashe ni
tsaye nima, ta dafa kafaduna da hannayenta
biyu. Tace kiyi ta karanta innalillahi wainna
ilaihir rajiun. Ki fita kice da yan sanda su rufa
miki asiri kamar yadda Allah ya rufa musu asiri,
su taimake ki kada su saka ki a gaba, zaki hau
babur kije can sai su same ki acan ba sai sun
saka ki a gaba ba. Nace ai bazasu yadda ba,
sai sun saka ni a gaba kamar wacce tayi sata.
Tace ke dai kici gaba da addua, ki fada musu
hakan zasu yadda. Idan kinje can ki basu
hakuri kice a baki kwanaki biyu zaki nemo
kudin ki biya su, ni kuma anan zan tilastawa
yayanki dole ko rance ne ya fita ya nemo a
biya su kudinsu kaddara ce ta hau kanki kada
ki damu. Kuma koda wasa kada ki sake ki
fadawa wani ko wata abinda kikayi da kudin
nan, dan kada ma labari ya dawo kunnen
yayanki kenje wajen boka, ki barshi a kawarki
kika taimakawa aka yi mata tiyata mijinta
bashi da hali, yafi sauki dan idan muka
kusukura mu ka bari yaji wannan labari sai ya
bata mana rai. Dazu na siyar da samiruna hudu
na biya su maijidda, dahare da dija dillaliya da
kikaje suma kika ranto kudadensu. Wata tace
dari takwas kika karba mata, wata dari bakwai,
wata dubu daya, suma na suka zo suke daga
min hankali suna nemanki danaji kudin ba yawa
sai na aika kasuwa aka karyar min da su nazo
na bibbiya su. Na uwani ne naji kudin da yawa
ba zan iya biya ba. Kiyi hakuri aisha farida, kiyi
ta istigfari game da wajen bokan da kika je,
kinyi wa Allah laifi kuma kiyi ma Sa alkawari
har ki koma gare shi ba zaki sake zuwa ba.
Kiyi ta karanta wannan adduar ta neman biyan
bashi "Allahumma bi jalika an haramika wa
agnani fadhlika amman siwaka". Sannan ta
bude kofa da sauri muka fito saboda bugun da
ake yi ya tsananta. Dandazon matan gidanmu
da matan unguwa da yaransu sun taru suna
kallona. Abida na rike da hannuna muna kuka
muka nufi hanyar waje. Muryar yaya hussaini
mukaji ya daka tsawa mai firgitarwa har sai da
kowa ya firgita. Yace da matarsa ta sake ni in
tafi ni kadai ta dawo daki inje can in karata ni
kadai. Ni da ita muka fashe da kuka. Ta
rungumeni sannan ta lalubo hannuna ta damka
min kudi naira dari biyu. Ta juya ta bar mi, sai
na cigaba da tafiya a sanyaye na fice yayin da
dandazon mata suke biye dani suna ta cece
kuce. Masu bada hakuri nayi, masu neman
ba'asi nayi, haka masu zuga nayi. Uwani kuwa
sai mayar da zancen take yi. In da Allah Ya
taimake ni duk sanda nazo wucewa ta ofishin
'yan sandar unguwarmu sai na duka na gaishe
su kullum, suna ganina suka gane ni nima na
gane su. Kalmar da suka fara ambato itace ah
kece daman? Ke kuwa yarinyar nan mai hankali
meya jawo kika shiga rigima irin wannan? Na
fashe da kuka nace ku taimake ni dan Allah ina
neman wata alfarma guda daya. Sai mai kivar
cike yace yarinya ai babu wata alfarma da
zamu iya yi miki anan, duk wata alfarma sai
dai ayi ta a ofishinmu. Tunda an riga an kira
mu dole mu tafi dake. Nace daman zanbi ku,
bana so ku saka ni a gaba da ankwa ku wuce
dani ta gaban mutanen unguwa yara suna bina
suna kallo kamar wacce tayi sata. Zan hau
babur ya kain ni sai mu hadu a can. Wallahi ba
zan gudu ba. Sai suka yi dariya suka ce idan
kin gudu ma ai zaki dawo, ba gamu a kofar
gidanku ba. Ko zaki shiga duniya ki bar
iyayenki saboda bashin da bai kai dubu ashirin
ba? Suka yi min izini na tari acaba na hau, duk
da babu nisa daga gidanmu. Na dan dade ina
jiransu sannan suka karaso, aka shiga da mu
uku ofishin mataimakin DPO, 'yan kallo aka
barsu a farfajiyar suka ci gaba da gulmace
gulmacensu. Saii a lokacin na gane makiyana
wadanda ada na dauka masu kaunata ne,
wadanda ada bana kulawa ashe sune masu
kaunata, sune masu jimamin abinda ya same
ni, sune masu nemar min afuwa a wajen
wadanda na yiwa laifi, sune