Showing 90001 words to 93000 words out of 99740 words
a
sarari,ta dube shi tayi fari da ido.ta ce,nayi
sa'a da nayi dace na sameka.Dr shuraim
hakika kana da kyau babu inda Allah ya
rage ka tun daga halittarka,ilimi da
dukiya.duk wadannan basu dameni ba,sai
na dinga lura da halayyarka.na shiga halin
damuwa alokacin da ka gwada ni cewar
zaka tafi da ni gidanka ko ba kayi bayani ba
na fahimci abun da kake nufi,sai na kudiri
niyyar rabuwa da kai har abada,kyawunka,
dukiyar baza su taba burgeni ba,tunda kake
sabawa Allah.sai daga baya na tabbatar ba
haka kake ba,kai mutum ne mai tsoron
Allah da tausayi shine na saki jikina na
tabbatar nayi dace da miji nagari.su dukka
sukayi dariya a lokaci guda.
Dr shuraim yace kin cika mai hankali mai
zurfin yunani,kuma ba zakiyi da na sani ba
tunda kika farga kika san kyau da kudi ba
komai bane in dai mutum bashi da hali na
gari.matsalar da ke damun yanmatan
zamanin nan ke nan,shi yasa ake samun
matsala a zaman aure,sakin aure ya yawaita
a kasar hausa.hirar so da kauna da fahimtar
juna suka yi tayi,har suka isa kofar
gidansu.yayin da yaran suke baya suna ta
hidima da kayan dadi,sai ci suke tayi,ya ki
ya kare saboda ledoji da yawa ya ciko
musu.aisha farida tayi godiya suka fito daga
motar suka shiga gida,dr shuraim yana daga
muau hannu,su ma suna daga masa har ya
tafi.su dukka suka ji kamar kada su rabu da
juna,sai kuma gobe idan Allah yaa kaimu zai
dawo don yanzu ba ya fashin zuwa wajen
farida.ASUBA TA GARI LIKITAN AISHA!!!
BABI NA ASHIRIN BIKI!BUDIRI! BIREDEDE!
Rana bata karya sai da uwar diya taji
kunya.tun ranar laraba aka fara gudanar da
shagalin bikin farida da angonta dr
shuraim.akayi kamu laraba,alhamis akayi
kunshi,jumaa akayi sisters eve da
yamma.ranar asabar aka daura aure da
misalain karfe goma sha daya na safe abisa
sadaki mafi kankanta don neman albarkar
aure,kuima a ranar akayi yinin biki.dangin
farida sunzo da yawa maza da mata daga
shagamu,tun sanda biki ya rage sati guda
suka fara zuwa don su taya ta murnar biki.a
ranar asabar da daddare akayi hadadden
party a hotel din tahir guest palace,wanda
mutane da dama suka halacci wajen.
Manyan likitoci abokan ango da kawayen
amarya,da yanuwaansu da abokan arziki
kowa yazo.makada kala kala sunzo kamar
mai dawayya,dan asharalle,yaron saadu
bori,fati niger,rabi mustapha,kowannensu
an bashi fili ya cashe.wannan yayi sai ya
matsa ya baiwa wani fili.babu abun da ake
kira sai likita shuraim angon sista
farida.barista muazzam da amaryarsa
janan,barista nuradin da uwargidansa
baraka su ma sun hallara.yan unguwansu ta
da duk sun zo babu wanda yasan adadin
wadanda suka zo,saboda yawansu.taro yayi
taro har amarya da ango basu iya gane
wadanda suka zo da wadanda basu zo
ba.kallo daya zaka yi wa ango da amarya ka
tabbatar suna tsananin murna.idan ka kalle
su zaka san maauratan nan suna tsananin
son junansu.sun ba wa kowa shaawa sosai
saboda sunyi kyau matuka,shigarsu ta
burge kowa,kowacce rana akwai kalar
kayan da zasu saka kala daya.
Kawayen amarya su ma sunyi nasu
ankon,dangin ango da irin nasu ankon
daban.'yan shagamu ma da irin nasu ankon
daban.masu daukar hotuna da bidiyo suna
ta aikin dauka,sai yau mutane da yawa suka
gasgata shuraim yayi saar mace mai
kyau,don kyawunta ya fito kamar ba ita
ba.ana daf da za a tashi sai ga uwar gidan
shuraim faiza ta shigo fili,ta yi wa kowa ba
zata ita da kawayenta guda biyu hafsat da
halima su ma mazauna london ne,tare suka
zo daga can.don da shuraim yayi yayi tazo
bikin tace baza ta zo ba,toh ashe ta taho
bai sani ba.ta danne kishinta tayi ta musu
kari da daloli sai a lokacin aisha farida ta
fara ganinta,ita ma haka,don ko a hoto ma
bai taba nunawa ko wacce ba.kyawunta bai
tsorata aisha farida ba ko kadan,don bata
fita kyau ba.fari kawai zata nuna
mata,tsayinsu daya,har farida ta fita tsawo
da yawan gashi.faiza ce ma ta tsorata da
ganina aisha farida saboda tayi mata ba
zata,ba ta zaci ta hadu haka ba,don 'yan
gulma sun tsegunta mata yar talakawa
ce,baka mummuna,ashe abun ba haka yake
ba.
Faiza ta kudiri aniyar zama na kishi,ba
kishin dokedoke da zage zage ba sai dai
zata nuna mata ruwa ba saan kwando
bane.wayewa da gogewa a cikin wayayyun
duniya tabbas abun da ta sani farida bata
sani ba,kuma ba zata taba sani ba.zata san
tayi garajen aure mata mili,don mai karbar
shuraim ahannunta sai yayi shirin yaki sosai
DUK KYAN TAKALMI 3* 13
Sai dr shuraim yaji dadi da ganin faiza ta
saki ranta,suka gaisa da farida sosai,har da
baby yarsa mai kama da uban kamar an
tsaga kara.babu wacce ta fi jin mamaki da
ganin aisha farida ita ce amarya sai
kanwarsa da suka hadu da ita a asibiti.suna
ganin juna suka shaida kansu,suka gaisa
cike da farin ciki.
Washegari ranar lahadi da yamma akayi
walima da yamma a farfajiyar gidansu
farida,aka zuba kujeru da yawa da manyan
dardumai.mata ne zalla da kananan yara sai
amarya da ta sha alkyabba,kawaye nta suka
zagayeta tana kan darduma a zaune daga
gabagaba.
mata guda uku ne suka yi waazi a wannan
waje,dukkaninsu akan falalar bin miji suke
magana.saboda yadda aazin ya ratsa
zuciyoyin mata,sai kowacce jikinta yayi
sanyi har da masu zubar da hawayen
imani.daga karshe abida ce ta karbi
lasifikata hau kujerar malamai ta dubi
dandazon matan da suka taru a
wajen,yawansu ya kai yadda baza su kirgu
ba,yara,manya,yanmata da tsofaffi.sai tayi
murmushi tayi musu sallama,sannan tayi
bismillah,ta dubi aisha farida. Like · 2 · 9
April 2013 Hajara Haruna Mahmud Ta
ce,nasiha zanyi miki ya ke kanwata farida
game da zaman aure.na farko iani miki
nasiha da ki bi mijinki domin aljannar mace
tana karkashin tafin kafar mijinta.yake
kanwata,ki fi shi farin ciki idan yana farin
ciki,sannan idan yana bakin ciki ki fishi
bakin ciki.ki kwantar masa da hankali.ya ke
kanwata aisha,ki lura da lokacin cin
abincinsa,domin mayunwaci mafadaci
ne.duk lokacin da kika lura lokacin cin
abincinsa yayi toh ki tanadar masa kafin ma
ya iso.idan ya shigo gida bayan kinyi masa
tara irin ta darajawa,toh ki gabatar masa da
abinci ba sai yace ina abincina ba?don idan
bari ma ya tambayi abinci to ransa ya baci
ma kafina a kawo masa abincin.wani ma sai
yaji baya shaawar abincin,sai yaji gara ya
tafi hotel ya ci mai dadi,duk ranar girkinki
sai yaki dawowa yaje yaci awaje.
Ya ke kanwata ki lura da lokacin da mijinki
yake jin bacci,ki bar shi ya kwanta ya huta
saboda wadansu matan sai sanda mijinsu
yake jin barci zasu tayar da shi su ce suna
da magana,yayi-yayi ta bar maganar sai da
safe tace wlh sai ka saurareni.daga lokacin
da kike hana mijinki yayi bacci a lokacin da
yake jin barcin to kina haddasa kakkaurar
gaba ce wacce ba zata gushe a tsakaninki
da shi ba. ya ke kanwata ki zauna a shirye
ki nunawa mijinki koda yaushe kina
bukatarsa.duk wani yanayi na kwarkwasa ki
dinga nuna masa.duk lokacin. Da kike
zaune da shi. Ki dinga shafar dukkanin
sassan jikinsa yadda zai yi farin ciki. Ya ke
kanwata ina horarki da yin ado ki lura da
ina yake fara kallo a jikinki da zarar ya shigo
cikin gida. Wani mijin fuskar matarsa yake
fara kallo,wani mijin da ya shigo kirjin
matarsa yake fara kallo,wani bayanta yake
fara kallo. To ki nutsu ki gane inda naki yaje
fara kallo. Idan fuska ce ki kula da lokacin
dawowarsa kafin ya shigo sai ki gyara fuskar
ki wanke ki saka hoda ki saka jagira,jan
baki,eye shadow da dai sauransu yadda
fuskar zata yi kyau sosai. Da ya zo sai ki yi
kokarin nuna masa fuskar kina murmushi.
Idan kirjin yake fara kallo to ki tanadi bra
mai kyau,irin mai karfen nan mai gyara
kirji. Tunda kin san kirjin yake fara kallo to
ba zai so kirjin ya ragwargwabe ba. Ko
bayan kin haihu sai ki bi duk hanyar da za ki
bi kada ki bari ya tamule,don wasu matan
su suke kwararraba kansu da zarar kin
haihu sau daya yaga kin tsufa sai ya fara
sha'awar ya auro wata budurwar mai kirji a
cike. To amma idan kika iya kula da
kanki,ba ki lalace ba ba zai tunanin neman
wata ba
In a gargajiyance ne akwai abunda larabawa
suke yi kirjinsu ba ya tamulewa,alkamadin
nan da kuka sani tana da amfani. Da zarar
kin sa rananr da zaki yaye danki kamar sati
uku kafin ranar da zaki yaye shi sai ki dinga
yin kunun alkama da nono ko
madara,madarar fulani ba yar kanti ba. Ki
sha kofi daya da safe kofi daya da yamma.
Bayan kin yaye yaron ma sai ki sake yin sati
uku kina sha,sati 6 kenan. Sannan randa
kika yaye yaron kuma sai ki saka bra wacce
ta matse ki sosai to wannan zai hana shi ya
zube duk da gyara ba zai yi kamar kari ba.
Ya ke kanwata ki lura da wuraren da mijinki
yake sa ido a jikinki in bayanki yake fara
kallo to akwai bukatar ki koyi tafiya idan
yace miko min buta sai ki juya kina
jujjuyawa ki wuce gaba yana biye da ke kice
za ki kai masa har bandaki. Ya ke kanwata
kada ki yarda mijinki yaga abun ki a jikinki,
ki kiyaye hancin mijinki kada ki yarda hancin
sa yaji wani karni,doyi ko bashi a jikinki to
duk lokacin da ya shigo dakin ki ko baby
warin sai yaji kamar da warin ba zaki taba
yin farashi a wajensa ba,kin zubar da ajinki
a wurinsa.saboda dauda ta dade tana kashe
aure sai a dauka wata aljana ce take zuwa
ta raba aure nan kuwa alnakiya ce kawai.
Ya ke kanwata ki kyaye kunnen mnki kada
ki yarda ya ji mummunar magana daga
bakinki. Ya zamanto duk abinda zai fito
daga bakinki zuwa kunnen mijinki to
magana ce ta girmamawa,jan hankali ko ta
tayar da sha'awa. Misali da na ganka sai
naji jikina ya yi wani zim don dadi (haha)
yake kanwata a lokacin da mijinki yake
kwance dake ki nuna tunda kike a duniya
ba a taba dadada miki ba irin a wannan
lokacin domin wannan zai sa kullum ya yi
sha'awar kasancewa tare dake. Ya ke
kanwata magana ta karshe da zan fada miki
ki guji bakin kishi,kishin da zai sa ki kasa
zaman lafiya da mutanen gida. To wannan
kishin zai saka tsana a zuciyar mijinki,kishin
da mace za ta yi shine wanda na fada a
baya,ya zamanto ba ya ganin wata mace a
duniya sai ke.duk abunda zaki yi ya
zamanto idan yana rumfar kasuwarsa ko
office ke yake tunawa.amma kishin da zaki
sa mijinki,abokiyar zamanki ko makotanki
cikin fitina to wannan kishi ne na lalatar
zamantakewa na aure. Allah ya nuna mana
ladubba na aure babu laifi mace taci abinci
tare da mijinta.ta bangaren maza kuma
addini ya nuna kada ango yaje dakin
amaryarsa haka hannu ba komai ya nemi
dan wani abu da zasu lasa kamar dan
nama,lemo ko dan cincin ya tafi da shi
dakin amarya.
Da farko yayi mata sallama ita kuma wajibi
ne ta amsa ba wai ta dinga noke-noke ba
wai sai an sayi baki. To bakin dukka ya biya
tunda ya biya sadaki. Bayan nan sai ya
shiga dakin da farko ya kama gashin
madigarta ya rike sai yayi addua yana tsaye
a kanta. "Allahumma inni as'aluka min
khaira ha wa khaira ma fiha wa khaira ma
jabaltaha alaihi wa'auzubikha min sharriha
wa sharri ma fiha wa sharri ma jabaltaha
alaihi. Ma'ana "ya Allah ina rokonka
alkhairin wannan amaryar tawa da alkhairin
da ka halicce ta akai kuma Ya Allah ina
neman tsarinka daga sharrinta da sharrin da
yake tare da ita da sharrin da ka halicee ta
akai" saboda wata ballagazar daga ya kai
hannunsa kanta sai ta buge hannun ta ce zai
murde mata kai. To iyayenta basu taba
fada mata ba ko malamanta. Ko da ya
manta to ki cire dankwalinki ki mika masa
kai,ki tuna masa idan ma bai sani ba ki fada
masa yadda zai yi idan ke kin sani. Kuma ba
amrya kawai ba ko da wani abu kika siya
kamar gida,mota ko dabba kafin ka fara
amfani da abin ka yi wannan addua. Idan
dabba ce an ce ka dafa bindin kamar kaza
sai ka kama bindinta ka yi wannan addua to
ba za ki ga wani abun bakin ciki game da
wannan dabbar ba. Haka idan sabon gida ne
ya dafa saman gidan yayi wannan addu'ar in
mota ya siya ya daga saman motar yayi
wannan adduar. Bayan ya yi wannan adduar
to sai ya zauna a kusa da ita su rungumi
juna su yi godiya ga Allah da yasa suka
zama halal ga junansu sannan ya gabatar da
wannan dan kayan makulashen da ya shigo
da shi su ci,ana ci ana hira ta sha'awa da
bege.
Amma an fi so kafin ciye- ciyen su fara
gabatar da sallah raka'a biyu nafila,kai ne
daman liman sai ka daga hannu ka yi muku
addua,Allah ya raba ku da sharrace-sharac
cen makiya,ya baku zuria ta gari,amarya
tana cewa amin.in duk sun kammala
wannan suka shiga kwanciya miji ya kusanto
matarsa sai yayi wannan addu'ar yace
bismillahi Allahumma jamnibnashaidan a wa
jannabul shaidana ma razaktana. Ma'ana,da
sunan Allah,ya Allah ka nisantar da shaidan
daga garemu,kuma ka nisantar da shaidan
daga abunda ka azurtamu da shi. Manzon
Allah (S.A.W) ya ce idan Allah Ya azurta su
da da a wannan saduwar da suka yi to babu
rabon shaidan a jikin wannan dan. Ba zai
iya cutar da shi a jikinsa ba ko a zuciyarsa
ba. Ba ranar angonci kadai ba duk randa
zaku sadu miji yayi wannan addua idan ya
manta ki tuna masa. Ba amarya kawai
ba,babu wacce bata karu da nasihohin
abida ba. Kuka yayi mata face-face a ido
kafin ta gama kamar yadda ya yiwa aisha
farida. Ta tabbatar yau abida ta cika amanar
da ta dauka ta rike ta tun tana karama har
zuwa wannan ranar data aurar da ita,ranar
da za ta damkata a hannun mijinta. Aisha
farida ta taso da sauri tana kuka ta
rungume abida suna ta kuka.kanwar
amarya manauwara ita ma ta taso ta zo ta
rungume su suna kuka.yayin da yan'uwa da
sauran jama'ar dake zaune a wajen suka
dinga fashewa da kuka don tausayinsu.
Aisha farida ta dago ta dubi jama'ar dake
wajen ta sharce hawaye. Tace" aunty abida
ta yi min komai wanda uwa da uba suke yi
wa yarsu. Tun ina karamata har izuwa ranar
da zata raka ni gidan mijina. Alllah shi ne
gatana abida ita ce jigo kuma jagorar data
kaini ga samun nasarar komai da na samu a
rayuwata.karatuna,zama da jama'a,farin
cikina da mijin da na aura. Abida ta hana
dan cikinta abu ta bani dan uwana yana
hana ni abu ita ta ba ni.anti abida bata son
taga damuwata,balle ta ga kukana. Ina yi
mata fatn Allah ubangiji Ya saka mata da
gidan aljanna,Ya raya mata 'ya'yanta Ya yi
masu albarka ko bayan ranta.Allah ka bani
ikon cigaba da yi mata biyayya da amfani a
rayuwa duk da nasan ba zan iya biyanta ko
da rabin2 abun da tayi min ba. Aisha farida
ta rushe da kuka sai jama'a suka dauka
gaba daya suna shi albarka suna gasgata
bayanan Aisha farida,musamman yan
uwansu yan shagamu.sannna aka watse
daga wurin walima domin ana ta kiran sallar
magriba.
Bayan sallar isha'I aka sake cancada
kwalliya kawayen amarya ne kawai da
abokan ango babu yara babu tsofaffi.
Hadaddiyar dinner ce za'a yi a royal
tropicana daga can za'a wuce da amrya
gidanta da yake ahmadu bello way,sai su
hadu da sauran mata da tsofaffi yan rakiyar
amarya a can, duk da daman wasu tunda
yamma suke can suna ta jere. Dr shuraim
ya kawata sabon gini a sabon gida wanda ya
tsantsara shi tamkar a turai mai dauke da
bangarori biyu iri daya sak. Kowanne ya
kunshi dakuna uku,faluka biyu,dinning
area,katafaren kicin da bandaki guda biyu.
Dakuna biyu!falo daya kicin da dinning area
dr shuraim ya zuba kaya gaba daya yan
waje ne,carpet da labulaye da fenti duk sun
yi iri daya,kalolin purple da pink. Ita kuma
amarya suka zuba nasu kayan a daki daya
da parlour daya ta roke shi da kyar ya yarda
ya bar musu don da ya ce komai ma su bar
shi. Tana gudun surutun danginsa saboda
an daukaki alada,haka gara ma sai da
danginta suka mata. Adashi yaya husaini
yayi abida da ita kanta faridar. Yan shagamu
ma sun taka rawar gani wajen hado kudade
aka hada da kudin aure da sadaki aka siyo
mata komai dai-dai karfinsu. Sai a yau su
uwani su ummulkhair suka sake gasgata
maganar abida da tace su zuba ido su ga
mijin da aisha farida zata aura. Yau sun gani
kuwa da idanuwansu. Tun daga gate din
shiga gida zuwa farfajiyar gidan ma abar
kallo ce don an kayata da shuke-shuke da
tsuntsaye,liluka,swimming pool kamar ba a
kano ba. Cikin gida kuwa ba ya kwatantuwa
aisha ta haye a rayuwar duniya dai,yadda
bangarenta yake haka bangaren kishiyarta
faiza yake,bambancin kala ce kawai ita
komai nata shudi ne da baki.
Gidan iyayen ango aka fara wucewa da
amrya,abban shureim yayi mata nasihohi
akan ta zauna ta bi mijinta lafiya,nasihohin
da yayi mata masu ratsa jiki ne.daga can
aka zarto da ita gidanta,bangaren kishiyarta
fa'iza aka wuce da ita suka iske falon nan
nata a cike dankar da hadaddun mata kai
kace su suka zabi kyawu da kudi sannan
Allah Ya basu. Kawayenta ne da kawayen
mahaifiyarta,danginta da wasu daga cikin
dangin dr shureim masu bin bayanta.wasu
sunyi musu faram-faram.wasu kuwa ban da
hararta da kallon banza babu abinda suke yi
musu,kai ka ce su aka yi ma kishiyar. Faiza
kuwa na zaune ko uffan ba ta iya cewa har
aka gama bayanai saboda tsananin kunar da
zuciyarta ke yi mata. Dangin farida ne masu
bayani har suna kiran ga 'yar su
amana,farida bata da matsala tana da
ladabi akwai bin na gaba ga hakuri da
kawaici. Suka yi kidansu suka yi rawarsu
suka fito. Hankalin aisha dai ya fara tashi
taga alaamr ko faiza na da niyyar su