Showing 51001 words to 54000 words out of 99740 words

Chapter 18 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf

ESHAT   

23 Mar 2025

5452

zaba saiki zo tun ranar asabar
mu fara aikin hada musu mai dadi da kunun
gyada ko kunun tsamiya zakiyi musu mu
zuba kofuna qanana zasu so shi kinga suma
duk abincin gargajiya ne Aisha tace gaskia
koba a fada ba dr shuraim zai so kunu sosai
shike nan haka za'a yi.Anan dai suka bar
hirar Aisha ta hadawa abida dukka kudin 5k
ta ce ta riqe a wajenta ba sai ta dau ko sisi
ba tunda ita ce take cefanen nan a aljihunta
asuba ta gari farida shuraim.
Khadija sani isma'I'll ce ta duni Aisha tace
wai me yasa kullun idan nace kizo ki rakani
babban daki na maza saiki turje ki tsaya

daga nan kice inje in dawo ba kya son
shiga?Aisha tace babu komai wlh ni dai
kibar ni nan kije ki dawo zan jiraki ko hour
nawa zakiyi khadija tace idan dai bazaki
raka ni ba nima ba zan je ba daman ba
wani abu zanyi ba illa in leqa ta wajen ofis
din kyakyawan likitana dr shuraim musu
mukeyi da mrym kinsan yanzu ta saki ranta
ta daina kishin dani data ga ta rasa nima na
rasa kuma bazamu samu ba mu duka sai
dai in mun hadu muyita labarinsa cewa tayi
yafi kama da larabawa ni kuma nace kyan
indiyawa gare shi shine nake so mubi ta
ofishinsa mu tantan ce nida ke kinjin Aisha
ya ne ya buga bummm!don fargaba nan da
nan taji hankalinta ya tashi tace a ranta
daman har yanzu khadija da maryam basu
daina son abuda nake matuqar so ba? Lallai
ashe akwai hargitsi a nan gaba gara ma dai
kawai in haqura da son mutunmin nan in
hutawa raina abida ce taqi haqura dana cije
na daure na watsar da son koda kuwa
zuciata zata lahanta koda ciwon zucia zai
zama shine ajalina in mutu in huta.sai taji
kwalla ta cika mata ido sai khadija ta
mungure ta sannan ta fara fahimtar
maganar khadija keyi khadija ta kalli farida
tayi murmushi tace kiyi min wannan
taimako yau dai ki raka ni har ofishinsa ba
komai zanyi ba illa in kare masa kallo in
tantance nidai nasan akwai wanda yayi min
kama dashi a film din india Aisha ta fusata
tace shirme kenan haba khadija kamar
wasu yan primary?ki tuna fa jami'a muke
shirin gamawa kuma manyan ma'aikata
muke shirin zama ma'aikatan ma na jinya
masu kula da lafia jama'a wadan ake
girmamawa a al'umma ya kike abu kamar
marar ilimi?kinsan mutumin nan kinsan
halinsa ke za ki fadawa wani irin salo da
launin wulaqancinsa.ke kika cemin min kin
haqura dashi baki yadda kika burge ni ba
har kika umarci muhammad saurayinki ya

kawo kudin aure ya kawo aka saka muku
rana tamkar matar aure kike saboda anyi
miki baiko ma'ana anyi wa wani alqawalin
bambancinki da matar aure kadan ne
mijinki kyakyawa dan gayu mai ilimi babban
ma'aikacin banki da kadan shuraim yafi shi
kyau habah khadija kada kibani kunya mana
ashe har yanzu akwai namijin da zai burge
ki bayan mijinki?kada fa ki zama irin matan
nan da zasu yi aute kuma suna son wasu
mazan a waje babban bala'I ne yin haka
dunia da lahira halaka ce.idan kin san
zuciayarki bata kwanta da auren
muhammad ba gara kada ayi kice kin fasa
kizo mu tayaki yaqin neman soyayyar
wannan dan wulaqancin!kahadija ta tuntsire
daria tace dadina dake Aisha umar akwai
fadar gaskia komai dacinta wlh ko dan
bazan zama daga cikin irin matan nan da
kika zano ba insha'allahu ba zan sake zuwa
ganinsa ba daman sai na manta dashi sai
maryam ta tsokano min zancen itace har
yau bata gama haqura ba Aisha umar ta
kalli barandar can ki gani.
Aisha ta wurga ido da sauri dr shuraim
imran ta hango yana tahowa tafia yake a
tsanake fuskarsa cike da fara'a jama'a suna
ta gaishe shi yana amsawa idonsa ne ya
wurga ya wurgo kansu Aisha farida
wadanda ke tsaye a jikin bishiyar dake kusa
da barandar da yake tafe kai kace ita da
khadija saurayi da budurwa ne suke
zantawa sun fuskanci juna suna tsaye cirko-
cirko babu wanda ya sake magana a cikinsu
yayin da khadija ke kallonsa tana yi masa
murmushi. Aisha kuwa sauri tayi ta juyar da
kanta gefe bata duban bangaren da yake
ma Aisha taji tamkar ta kurma ihu don
takaici tada ji khadija ta maqe murya ta
gaishe shi saii ya amsa cikin farin ciki ya
wuce abinsa sai da yayi nisa khadija ta
zungure ta tace amma bakida kirki kina
ganin malaminki amma kika qi gaishes shi ?

naga alama fa baiji dadin ba da baki gaishe
shi ba Aisha ta tabe baki tace yaya akayi
kika san baiji dadi ba? Khadija tace saboda
naga irin kallon da yake yi miki ne leqen
fuskarki yane tafe yana waiwaye so yake ki
juyo ya ganki Aisha tace ai ba dole ne in
gaishe shi ba tunda in an gaishe shi sai
yaga dama yake amsawa ke rabi ni da
wahala kinji ta kaina nake bani da lokacin
kowa.khadija tace kin huta ai shiyasa kike
burgeni ina son halinki ko bayan idonki ina
fada daman tun farko ma dai naga alamar
kin tsani dr shuraim ko zancensa ba kya ayi
miki Aisha tayi wani lalausan murmushi ta
gyada kai tace me yasa zan tsani musulmi
dan uwana ?aa wlh ban tsane shiba ko
kadan ina sonsa so tamkar raina zai fice
kamar yadda nake son dan uwana na jini
saboda shi ma musilmi ne musulmin ma
mumini mai riqe addini irinsa khadija tayi
doguwar ajiyar zucia ta dauka Aisha ma zata
ce itama ta mato a sonsa yadda itama take
sonsa sai taji farida tayi kwana.suna tafe
suna firarsa har zuwa bangaren da suke
wato wajen masu ciwon hawan jini da
ciwon suga Akan barandar da suke tafe a
nan shuraim ya taho suna daga ido sai suka
hango shi daf dasu shi yana tahowa su suna
tafia sai suka yi gum da bakinsu don birarsa
suke a lokacin dan halak yaqi ambato inji
khadija Aisha ta duqar da kanta qasa bata
sakw dagowa bahar sai daya gifta ya wuce
kamshin jikins ya daki hancinta sai ta
lumshe ido ta fada a zuciayar ya Allah ina
son wannan bawa naka sannu likita sanna
da qoqari kalaman da suka rikito kunnen
Aisha ke nan daga bakin khadija take
fadawa dr shuraim dai-dai sanda yazo
giftawa ya fada cikin qasaita thank u ya
wuce abinsa Aisha farida tafia take kawai
amma tamkar ta hadiyi zucia don jin
haushin barar da ajin da khadija keyia
wajen bawan Allah nan.

Khadija ta zunguri Aisha tace saki dago da
kanki dodon naki ya wuce don naga ko
kallonsa ba kya son yi ikon Allah shi kuwa
sai ya tsura miki iso yayi ta kallonki don
Allah ki dinga gaishe shi bin na gaba fa bin
Allah ne Aisha tayi ajiyar zucia tace Allah
yabamu ikon bin shugabanninmu amma
wadanda suke bin Allah khadija tayi daria
tace shegiya Aisha umar akwai iya magana
nasan baki yarda da abun dana fada miki ba
zaki dinga gaishe shi ba kenan?kin jini ne
dai kawai Aisha tace uhmm kawai take
fadin sai kuma gyada kai take tayi tamkar
kadangaruwar ta kasa cewa komai saboda
ganin dr shuraim dinnan da tayi yau yayi
mummunan fama mata son data keyi masa
Aisha shuraim haquri shine maganin zaman
duniya! Aisha ta cika mamaki a lokacin da
yaro ya leqo dakinta yace tazo wani yana
sallama da ita a qofar gida a motarsa a
zaune ta duba agogo karfe 7:30 na dare ko
isha'I ba'a kira ba yadda take zaune akan
abun sallarta sanye da hijabi da carbi a
hannuta haka tayi zunbur ta miqe tace da
yaron tsaya ni mu tafi tare ka kai ni wajen
mai yin sallamar dani faruk ta gani dan
abida a tsakar gida tace idan mamarka ta
idara salla a kace mata anyi kirana a qofar
gida ina zuwa ya amsa da to aunty Aisha
zaki siyo mun alewa da biscuit?aisha ta
girgiza kai banyi maka wannan alqawalin ba
nima nan daka ganni na dade ban sha
alawaba ta wuce da sauri ita da dan aike ta
kama hannunsa tace yaro a ina mai motar
yake?wayace ka kira?yaron yace a wajen ya
tsaya kafon a hayo sai ya kirani yace inzo
nan gidan nan mai bishiyar dirimi in kira
masa Aisha umar qanwar husaida mijin
abida shine nake ta leqawa ina tambaya har
aka nuna min dakinki mamaki ya sake
lullube farida ta dafe qirji tace inalillahi wa
inna ilaihi raji'un Allah yasa baqon nan
baqon Alkhairi ne toni waye wannan?ba dai

dr lukman bane balle in saka ran dr
shuraim sune kadai nasani a dunia masu
mota su kuwa basu san gidanmu ba haka
yaro yaya suffar mutumin take?yaro yace
dogo ne haka fari mai dan gemu a habarsa
kyakyawa mai kudi motar hadaddiya Aisha
ta juya kawai tana kallon yaron tana
mamakin yadda yake suffanta
mutumin.tabba s suffofin dr shuraim ya
zano mata amma tana tabbacin ba dr
shuraim bane a wanne dalilin ma zata saka
ran dr shuraim zaizo gidansu mutumin da
har yanzu bai game gane taba a hanya balle
wata hulda ta hada su harma ya tako a
qafarsa ya zo inda take don haka ta cire dr
shuraim a tunanin ko shine sai ta koma
sake saqen wasu daban suna tafe fakam-
fakam sai sauri suke zubawa ta sake juyowa
ta dubi yaron tace yaro shi kadai ne koda
macea motar?yace shi kadai ne! Aisha ta
fada a bayyane toni Aisha waye wannan da
akwai mace a motar sai ince khadija ce ta
kawo min mijinta mu gaisa yaro kawo bakin
wata dalleliyar motar qirar BMW baqa
wuliq sabuwa dal!har sheqi take ya ce ga
motar mutumin yana ciki,
Gabanta ya yanke ya fadi daf-daf taja ta cije
ta tsya a gefe tace kwankwasa masa gilashi
kace masa gata ka kira ta don inga ko waye
yaro ya qarasa da sauri ya daddage ya daki
glass kai kace qofar qarfe yake bugawa
lallausan hannu hade da kyakyawar fuskar
dan adamu ne ta fito fili sai gashi ya
bayyana a lokacin da ya sauke gilashin
wundonsa qasa Aisha ta kaikace tana
leqensa daga nesa har yanzu bata gane shi
ba kasancewar akwai duhu wajen duk da
akwai hasken redio motarsa na haska shi
kadan yaron ya dawo wajen farida yace ki
qarasa kinga har yabani N100 Aisha tace
lallai ka caba kaje na gode tafia take a
nutse amma a tsorace kamar ace kulle tace
cas!nauyi kunya fargaba da tsanaanin tsoro

sun gallabe ta ta isa jikin window da yake
zaune ya zuba mata ido yana kallonta
fuskarsa cike da annuri yana nuna farin cikin
da ganinta ta kasa kallonsa saita duqa ta
gaishe shi ya amsa cike da fara'a hadi da
cewa hajia Aisha farida yar shagamu nasan
zakiyi mamakin ganina ko?wannan karon da
sauri ta dago kai ta dubi kyakyawar fuskarsa
domin tana jin muryarsa ta gane ko
wanene tabbasa muryarsa ta tabbatar mata
dashi dinne wanda take zato a lokacin data
dubi fuskarsa.dadi marar misaltuwa suka
tabbata a zucia yar Aisha ta dafe qirji ta
fada cike da mamaki marar adadi barista
mu'azzam yau kaine a gidanmu nayi
matuqar mamaki hade da dinbin farin ciki
dana ganka a gidanmu ka kyauta gaskia
Allah ya bar zumunci yayi daria yace miki
wannan shine zuwana na farko aina sha
zuwa nansai in aika yaro ya dawo yace min.
Ance ba kya nan kai rannan ma ce min kayi
gidan naga wasu maza 3 a zazzaune akan
tabarma suke cemin kina ciki amma
shwararda zasu bani kada in sake dawowa
ba kula zaki yiba haka yayanki ma idan ya
ganni korar kare zaiyi min.na fahimci dai
hassada ce kawai na tafi na barsu yau dai
Allah yasa na sami yaro mai wayo nace ya
shiga ciki ya nemo har. Dakinki ya kirawo ki
amma wanne irin zama kuke da
mutanengidanku haka shin bakwa shiri ne?
sai hawaye ya fara surnanowa a idontaAisha
tana sharbewa da hijabinta barista
mu'azzam ya warwaro toilet paper ya miqa
mata yace aa qanwata kin fara koke -koken
naki ko?bana son kukan nan yanzu zaki
kore ni fa Aisha farida ta goge idanuwanta
tace na daina kuka yayana abun ne yabani
mamaki muna zaune dasu zucia daya muna
qoqarin kyautata musu su basa qaunarmu
ba'a son ci gabanmu ko zaka rufe motar
kazo muje kan dakalin qofar gidan mu
zauna kada in shiga motarka ayi ta

yamudidi dani a unguwa da sharri kala-kala
Alhamdulillah daka san yadda mutanenmu
suke. Barista mu'azzam yace kwarai kuwa
yi gaba zan biyo bayanki kada a ganmu mun
jera muna tafia Aisha tayi sauri ta shiga
gida don dauko sallaya da pure water.
Abida tabi ta daki a gigice tana tambayarta
wai waye yazo a dalleliyar mota ne, naji
matan gidan nan suna ta yamadidi, har
suna aika 'ya'yansu suje su gano musu ke.
Aisha farida ta rike baki tace mun shiga uku
da zaman haya, au faruk ba fada miki sakon
dana bashi ba, nace ana kirana a waje na
tafi. Abida tace bai fada min ba a tsakar
gida nake jiyo gulmar. Kada fa kice min dr
shuraim ne? Aisha farida tace in dr shuraim
ne ba sai mu gudu ba? Bashi bane, barister
muazzam ne. Ta kwashe labarin daya bata
ta fadawa abida, na 'yan hassada. Mamaki
ya rufe abida ita ma sai da tayi kuka. Aisha
farida ta hanzarta daukar sallaya da pure
water guda biyu ta fice da sauri ta iske har
barrister muazzam ya karaso kofar gidan,
kasancewar bayan magriba ne don haka
yawancin mazan gidan duk suna masallatai,
sai anyi sallar ishai zasu dawo. Ta shimfida
akan dogon dakalin mai fadi, sannan ta
umurce shi da ya zauna. Yana zama sai ta
duka ta mika masa pure water ko sanyi
babu, ya karba yayi murmushi yace nagode
ki zauna mana ya zaki tsaya a tsaye, ai ina
ganin akwai tazara a tsakanin mu idan kin
zauna a karshen dakalin, ni ma ina karshe
ba za a ce kinyi rashin kunya ba dai ko? Don
naga alamar unguwar nan taku abar tsoro
ce, suna da saka ido da gulma, koda yake
duk cikin gari haka suke, 'yan gargajiya ne
kawai. Babu maganar wayewa a tattare
dasu.
Aisha farida tayi murmushi ta zauna a
tsorace ta sake gaishe shi, sannan tace yaya
muazzam sai hakuri, bamu da fridge kuma
inda ake sayar da ruwan sanyi babu saboda

munfi sata ba a kawo mana wuta ba, zaka ji
ruwan babu sanyi. Muazzam yayi dariya
yace kada ki damu, yanzun nan na sha ruwa
har roba biyu a mota, na karba ne dai don
kar kiji babu dadi, nagode. Aisha farida tayi
dariya tace a'a nice da godiya, naji dadi da
na ganka, Allah Ya bar zumunci. Ina
abokinka barr nurruddin? Ina baraka
matarsa? Ina kuma matarka dr janan? Barr
muazzam ya kwashe da dariya yace har kin
daura mana aure ne ta zama matata? Duk
suna nan lafiya kamar yadda kika barsu,
babu wanda ya sauya a cikinsu. Nuraddin
yana nan yana taurin kansa, da gallazawa
baraka. Haka itama baraka tana nan tana
hakuri. Ko da yake kwanan nan ta fara ce
min hakurinta ya fara karewa, zata fadawa
magabata a raba auren. Ita kuwa janan
tana nan a daure ana ta tafka sharia babu
wani canji a tsakanina da ita. Iyayenta ne
dai kawai suke ganin kokarina da nake a
kanta, ita har yanzu bana gabanta. Ni har
haushin kaina nake ji wata rana ince to wai
me yasa na nace sai janan bayan a gari ga
'yan mata nan reras wadanda ma suka fi ta
kyau da kwalliya, saboda a yanzu idan kika
ga yadda janan ta koma idan kinsan ta a da
ba zaki ce ita bace, kamar wacce aka sauya
ta gaba daya duk tayi muni, tayi baki, an
aske wannan gashin nata mai tsawo sai
kwas kwas. A ficika wani ba zai dauke ta ba,
amma har yanzu zuciyata bata daina sonta
ba, kuma ita kadai nake so bana son wata.
Wannan al'amaro yana bani tsoro da
mamaki. Aisha farida ta girgiza kai tace
Allah sarki rayuwa, har naji tausayinka.
Wannan shine ake kira soyayyar gaskiya, so
saboda Allah kenan ba don wani abu ba.
K KYAN TAKALMI 2* 9
Dr lukman yace kin tabbata baki gane abin
da yake nufi ba? Kada ki boye min komai.
Aisha farida ta girgiza kai ta zubo da
hawaye da ya cika mata ido tace bansani ba

wallahi. Yace to jeki zanyi miki waya anjima
kada kiyi kuka. Aisha farida ta tashi da sauri
ta fice yayin da dr shuraim ya bi ta da
harara. Tana fita sai ta rufe kofar kuma ta
labe ta dora kunne a jikin kofa tana
sauraronsu. Dr lukman ya juya ya dubi
shuraim yace wai me yake faruwa ne?
Yarinya ce fa kimtsatsiya. Tana bin maza ne
ma'aikata? Dr shuraim yace kaji matsalar ku
kenan, baku da kyakkyawan zato, nan da na
sai ku ballo bala'I. Meya kawo wannan
zargin kuma? Dr lukman ya juya ya dubi dr
mohd yace don Allah dr a kasar hausa idan
aka dubi mace akace ki kama mutunci da
darajarki ta 'ya mace meke nan? Ba 'yar
iska ba kenan? Dr mohd yace kwarai kusa,
kasan bature ne su a london ustazan mata
ake fadawa haka. Suka kwashe da dariya su
dukka, dr shuraim yace uhumm kai kake
ganin hankalin yarinyar na, ai ni tuni nasan
maciji sari ka noke ce. Nafi ku karantar
halayanta. Wato tunda Allah Ya halicce ni a
duniya tsakanin jinsin mace ko namiji ban
taba ganin wacce ta iya hawa acaba irin
wannan yarinyar ba. Sai su dr lukman suka
kwashe da dariya, yayin da dariya ta
kubcewa aisha farida sai tayi sauri ta toshe
bakinta. Dr shuraim ya bata fuska yace ai
ku abin ma dariya ya baku? Wallahi ba abin
dariya bane, ya kamata kayi mata fada.
Hawan jini ne kawai rannan banyi ba,
shekaran jiya ne ma ba adade ba. Caraf
zaka ga ta haye

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login