Showing 57001 words to 60000 words out of 99740 words

Chapter 20 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf

Advertisement

ESHAT   

23 Mar 2025

5575


man gyada zaryan aka soya da albasa sai
kamshi yake dayar kuwa salad ne aka yanka
shi kanana da tumatir da albasa da
kokunba.ta isa ofishi kanta tsaye babu
shajja ba tsoro,don ba ta ga motar gogan
nata ba tasan bai iso ba don bai saba zuwa
da wuri ba.
Karfe 8 saura kwata a babur din a daidaita
sahu ta yi wa aisha Farida ita da kwandunan
abincinta har guda 2.ba ya ga kayataccen
food flask guda 2 manya,daya a shake da
hadadden dambu daya a shake da danwake
sai farantunan tangaran 3 sai cokulla sai
wasu robobi 3 yan kanana masu murfi daya
yaji ne mai dadi gaske ya sha maggi daya
man gyada zaryan aka soya da albasa sai
kamshi yake dayar kuwa salad ne aka yanka

shi kanana da tumatir da albasa da
kokunba.ta isa ofishi kanta tsaye babu
shajja ba tsoro,don ba ta ga motar gogan
nata ba tasan bai iso ba don bai saba zuwa
da wuri ba.
Ta kwankwasa kofa sai ta murda ta tura kai
dauke da kwandunan abinci riki-riki a
hannunta ta yi sallama ta shiga sai ta ga
wayam babu kowa a ofishin.babu tantama
ko ya shiga bandaki ne don haka sai ta daiki
gwandunan ta tura lungun da take ganin
yana ajiyewa dan ta kawo masa.tana tsaye
a gaban teburin tana jiran ya fiti amman
shiru kuma abun da ya bata tsoro ba ta jin
motsin komai a bandakin. Motsi ta ji an
turo kofa da karfi yayin da ta waiwaya da
sauri fuskarta cike da fara'a tana murna da
ganin yayanta.tace a ranta ashe ba'a
bandaki yake ba yana waje"sai dai kash da
ta hada ido da mai shigowar ba fuskar Dr
Lkman ta gani ba tayi matukar firgita gami
da razana a bayyane wanda shi kansa
wanda aka yi razanar dominsa ya gane.
Kallonta yake yi a nutse har sai da ya shigo
cikin ofishin ya mayar da kofar ya rufe ya
fara tafiya a hankali zuwa gaban teburin
kusa da inda take a tsaye. Numfashinta ne
yake kokarin daukewa, idanuwanta kuwa
sai suka kasa tsayawa a waje guda suka
dauki farfari yayin da ta nemi yawun
bakinta ta rasa, balle ta samu damar fitar
da lafaxi guda daya. Ya dauke kansa daga
kanta ya zagaya ya jawo kujera ya zauna
yaci gaba da bincike wani file. Da taimakon
addoui aisha farida taji numfashinta ya
daidaita, ta sami nutsuwa a cikin zuciyarta.
Ta dube shi cikin kunya hade da ladabi ta
sunkuyar da kai kasa, sannan ta kaskantar
da muryarta kasa ta zakaka makoshinta, ta
duka har kasa ta gaishe shi. Dr shuraim ya
daga ido ya dube kasa kasa da alama yaji
dadin yadda ta gaishe shi, sai ya amsa cikin
sakin fuska. Ya kara da cewa kina neman

lukman ne ko? Ta gyada kai ba tare da ta
iya hada ido dashi ba, tace eh. Ya dube ta
da gefen ido yace ai bai karaso ba, sai
anjima nine na bude ofishin. Aisha farida ta
duka tace nagode. Sannan ta juya zata fita.
Kamar a mafarki taji yayi mata magana.
Babu abinda za'a ce masa? Ta juyo a nutse
ta dube shi sannan tayi masa wani
dandasheshen murmushi, wanda ta
tabbatar an sha tabbatar mata idan tayi shi
yana kara mata kyau. Siririyar wushiryarta
ta bayyana yayin da kumatunta gefen dama
ya lotsa, fararen hakoranta sai su sake
haske. Tace dama sakonsa ne na kawo
masa, gashi can na ajiye masa. Sai ta nuna
lungun data ajiye kwandunan. Ya wurga
dara dara idanuwansa ya kalli wajen sannan
yaci gaba da dube duben file dinsa. Har
yanzu aisha farida tana tsaye a jikin kofa ta
rike kofa ita bata fita ba, ita bata dawo ciki
ba. Ya dago da kai a hankali ya dube ta,
yayin da ita kuma ta sunkuyar da kanta
kasa a hankali. Yace okay zan fada masa.
Tace kace masa kanwarsa ce aisha farida
umar. Ya dago da kai ya dube ta da alama
yaso yayi mata wata tambaya ya fasa, sai ya
gyda kai yace idan nace masa kanwarsa mai
hawan acaba ai ya sani. Sai ta ya danyi
murmushi lokacin da yake karshen
maganar. Ta langwabe kai ta marairaice ido
kamar mai shirin fasa kuka. Tace yaya
lukman ya fada min laifina jiya, nayi
kuskure bazan sake ba, nima nayi tunanin
naga ban kyauta ba. Sai ya kalle ta kawai ya
ci gaba da rubutu, can yayi magana ba tare
da ya sake dubanta ba. Yace hakan dai zaifi,
ki yiwa kanki fada, don ke mace ce, a
addinance ma bai dace ba. Dan wasu 'yan
acaba ba su da hankali. Ta duka tayi masa
godiya ta murda kofa ta fita. Ta jawo kofar a
hankali ta tafi. Taji kamar ta fasa ihu, ko ta
daka tsalle ta dire don murna. Ta shaki iska
ta lumshe ido ta daga ido sama tayi wa

Allah godiya gami da yiwa alkawarin zata yi
ma Sa azumi gobe don godiya, da Ya fara
karkato da hankalin dr shuraim kanta.
ALLAH ABIN GODIYA!!
BABI NA GOMA Nan da nan aisha farida ta
ajiye aikin ta take yi ta jawo gyalenta da
sauri ta biyo dan aike ta fito don taga mai
sallama da ita da yammacin nan. Tana
fitowa sai taga muazzam ne. Sai ta ji farin
ciki ya rufe ta, tayi sauri ta durkusa har kasa
ta gaishe shi, yayin da ta nemi izini a
wajensa zata shiga ta dauko sallaya ta
shimfida masa akan dakali. Sai ya dakatar
da ita, yace ta bari kawai daman daga wajen
aiki yake hanya ta bullo dashi tanan, shine
yace bari ya karaso su gaisa. Aisha farida
tayi murmushi ta lngawabar da kai tace sai
in rasa harshen da zanyi amfani dashi wajen
gode maka yayana. Allah Ya saka maka da
alkhairi da wannan zumuncin da kake
gudanwarwa a tsakanin mu, nagode. Ai na
sayi waya da wannan kudin da ka bani,
ashe ban karbi lambarka ba, na rasa inda
zan nemo ka, dole na hakura. Na kagu inji
halin da kake ciki, kai da janan. Muazzam
ya lumshe ido yace alhamduliilahi kanwata,
naga falalar addua da hakuri, kuma na rike
mutuncina yadda kika ce. Naje mata da
siyayya iri iri na kaimata, ko kallona takiyi.
Sai na sami waje na zauna nace mata janan
ina so ki saurari bayanina kiji dalilin zuwana
wajenki yanzu. Ada na soki ba kya sona, a
yanzu naso ki bakya sona, don haka na
hakura ba a dole a soyayya. Allah Ya sauya
min da wacce take sona har ma an saka
mana ranar aure. Kiyi hakuri da takura miki
dana yi a da. Ina so a yanzu ki saki jikinki
dani, ki dauke ni a matsayin yayanki, kuma
lauyanki bayan nan babu wata alaka
tsakanina dake. Ina gama fada naga
alamaun jikinta yayi sanyi. Kullum naje sai
inga tana yawan kallona tana kuma bude
baki tayi min magana, duk tambayar da

nayi mata. har na hada baki da wata matar
yayan, sai tayi ta kirana a waya a dai dai
lokacin da nake tare da jana, sai na dinga
amsawa kamar da budurwata nake
magana. Sai inga fuskarta kamar bata jin
dadi. Aisha farida ta cika da mamaki tace
duk a kurkukun ake wannan? Barr muazzam
yace eh ai ana bari na in shiga sai a
kirawota a hado ta da maikaciyar kurkukuk
daya,ta kawo ta inyi mata tambayoyi
saboda neman hujjojin da zan bayar da
kuma nemo shaidu a kotu. Aisha farida tace
lallai ni abin da na lura janan tanan sonka,
tsabar jan aji take yi maka don ta tabbatar
kana sonta, kuma baka fushi duk
wulakancin da zatayi maka. Muazzam yace
haka ne wallahi, sai yanzu na yadda da
haka. Ai nuna mata nake bata gabana kwata
kwata yanzu. Baraka ma ta samu sauyi na
fada mata duk yadda zatayi, kuma ta
aiwatar tana addua kuma tana hakuri,
sannan kuma tana jan ajinta tana yi masa
girki, ta tsaftace gida, ammma ta fita
harkarsa bata bari ma su hadu a gidan,
kwana biyu ko uku tana gidan bata bari ya
ganta. Sai gashi yana fada min wai baraka
ta sauya halinta yanzu ta daina damuwa
dashi, in bashi ya leka dakinta ba, ita ba ta
fitowa. Sai na kalle shi na watsar nace au
har dakinta kake takawa ita da kake korarta
da idan ta shiga dakinka? Sai yace ai dole in
leka inga halin datake ciki, kar inje ta shiga
daki ta kashe kanta ko ta hadiyi zuciya ta
mutu. Nace masa ashe kasan kana kuntata
mata har zata iya hadiyar zuciya ta mutu
ko? To kaji tsorn Allah. Sai yayi shiru bai ce
komai ba. Itama barakar take cemin wallahi
ya fara sauyawa, yanzu da kansa yake
dawowa gida yaci abinci, dga lokacin cin
abinci yayi, da kuwa har kifarwa yake yi a
gabanta idan ta matsa masa yaci. Aisha
farida tayi dariya tace alhamdulillahi, Allah
Ya kara yi mana jagoranci. Barr muazzam ya

dube ta yace ni naga duk kin rame, lafiya
kuwa? Ko dai shuraim din ne ya taba min
ke? Aisha farida ta girgiza kai tace babu
ruwansa bawan Allah, wlhi antina ce abida
bata da lafiya sosai, gabobinta gaba daya
tun daga kafa har wuyanta duk inda
mahadar kashi take ta kumbura suntum,
tana yi mata ciwo, da kyar take tafiya.
Shien muke ta sunturi asibitin kashi na dala
(autopeadic). Anyi xray da gwaje gwaje
sunce basu ga komai ba, ciwo kima sai
karuwa yake. Yanzu da kyar take iya
takawa komai sai anyi mata. Shiyasa kaga
duk na susuce. Subhanallah, Allah Ya bata
lafiya. Inji barr muazzam.
Aisha farida tace amin ai munyi sati biyu da
barin asibiti, rabona da dr shuraim kenan
amma akwai cigaba sosai. Ta zayyanowa
barr muazzam labarin abubuwan da suka
faru tsakaninta da dr shuraim da kuma
mataki na hudu da abida ta karanto mata.
Barr muazzam ya dubi aisha farida cike da
rashin fahimta yace to ni kamar ni ta yaya
zan yi mata biyayya? Kuma kamar baraka
wacce tayi biyayyar a baya bata ci riba ba,
sai da ta share shi ta fara samun saukin
wulakancin? Aisha farida tace ai a ganina
duk daya ne mu ukun. Yanzu kamar baraka
taci gaba dayi masa haka har lokacin da zai
karkato sosai, yana son zaman nata sai ta
dawo tayi masa biyayya sosai, tayi duk abin
da yake so, ta bar abinda baya so, ta nan
zai fara mantawa da nafisa. Ko kuma zai
fara kokonto ko ya rike matarsa ne, ya rabu
da waccan don na tabbata ba zatayi masa
biyayyar da baraka take yi masa ba. Saboda
wadannan dalilan nawa na farko kace babba
ce har ta dade da gama jam'ia. Na biyu
tasan yana sonta don haka zatayi ta jansa a
kasa kasan halin mata. Barr muazzam ya
gyada kai yace lallai kanwata na yadda da
tunaninki, kamar kina zaune a wajen duk
yadda kika fada haka ne. Aisha farida tayi

dariya tace kai kuma a bangarenka kaci
gaba da nuna mata ka sami wata bata
gabanka yanzu. Kada ka bari alakarku ta
rabe, ku cigaba da yawan haduwa ko bayan
ta dawo gidan a matsayin abokinta zaka ga
ta dawo. Kada ka fada mata da wasa kake
da wuri, kayi ta kyautata mata, kanayi mata
duk lallashi da tarairaya. Kayi ta yin duk
abin da kasan tana so, ka kiyaye wanda ba
taso tabbas zataji kai kafi dacewa da
rayuwarta, ko bata zo tace tana sonka ba,
zata nuna alamu. Barr ya gyada kai yayi
murmushi yace gaskiya ne wannan kinyi
hikima, Allah Ya sa mu dace. Bani lambarki
don muci gaba da tattaunawa a waya. Ya
zaro wayarsa daga aljihun, aisha farida tana
karanto masa lambar yana rubutawa har
suka cika. Sannan ya kira lambar ta shiga,
amma wayar tana gida. Aisha farida tace
idan na shiga ciki zanyi saving. Barr
muazzam ya zaro kudi daga aljihu, naira
dubu biyu ne 'yan dubu dubu guda biyu, ya
mika mata nan fa ake tataburzar, don aisha
farida ta tubure ba zata karba ba, shi
kumwa yace sai ta karba. Ko zubarwa zatayi
sai dai ta zubar. Sai da ta ga ya dage sosai
har ransa zai baci sannan ta durkusa ta
karba, tayi masa godiya suka yi sallama ya
tafi, tashiga gida cike da farin ciki kamar
kuwa yasan suna cikin tashin hankalin
rashin kudi, asibiti duk ya cinye musu
kudin. Cefane ma sai harhade harhade ake
yi, a dafa a ci ba dadi don kar a mutu.
Ciwon abida kamar da wasa, abu ya fara
tsananta hankalin kowa ya fara tashi, don
har hussaini yayi waya ya sanarwa da
iyayenta da 'yanuwansu na shagamu.
Babban likitoci yanzu take gani a asibitin
kashi, don ciwon ya wuce kananan likitoci.
Magani take dirka amma fa a banza, ko
alamun canji bata ji a jikinta. Daga nan sai
suka rabu da zuwa asibitin kashin ma, suka
dawo gida aka fara na hausa, wannan yace

sanyin kashi ne, waccan tace mayu ne.
Kowanne magani hussaini yaji sai ya karbo
ya kawo, burinsa matarsa ta sami lafiya.
Abinka da mai ilimi aisha farida bata son
wannan gwafje gwafejen magungunan
gargajiyar ko hussaini ya kawo ya bata, sai
ta boye bata bari tasha. Gara ma na
shafawa a gabobi tana shafa mata kamar na
sanyin kashi da aka karbo musu a wajen
sarkin ruwa na wudil. Maganin sanyi kashi
ne da man shanu ake kwabawa a shafa a
gababin. Sai man tafarnuwa dashi ma akace
ta dinga shafa mata a gabobi shima tana
shafa mata kullum da daddare kafin su
kwanta.
DUK KYAN TAKALMI 2* 11
Babu abinda abida ke iya yi, sai anyi mata
tana kwance kawai. Amma tana magana
radau kuma idan an bata abinci tana ci
sosai. Sai tsananin sanyin da take ji, sai tayi
ta makerketa duk da bargunan da aka lufga
mata, kuma a lokacin zafi ne. Ba asiha
farida da hussaini da 'ya'yan abida ba kadai,
duk wani mahalukin da yake da dison imani
a cuciyarsa hankalinsa sai ya tashi idan yaga
ciwon nan kuma ya tausaya mata. 'Yan
dubiya basa karewa layi layi mata suna
shiga, wasu na fitowa. Sai yanzu 'yan gida
da 'yan unguwa suke zayyano kyawawan
halayen abida. Idan akace yau asabar da
lahadi ce lokacin yaya hussaini yana gida
baije aiki ba, to mazan unguwa da abokan
aikinsa sai suyi ta tururuwar zuwa dubiya.
Kuma yawanci basa zuwa hannunsu haka ,
suna riko kayan dubiya kamar ayaba da
lemo, ko kayan shayi, wasu kuma sai su ba
da dan kudi suce a sayi magani. Aisha
farida ta labe tayi kuka har ta gaji, addua
take Allah Ya tashi kafadun abida uwarta,
ubanta, yayarta kuma kawarta, sannan
aminiyarta mai bata shawara. Aisha farida
ta tari yaya hussaini a bakin kofar dakinsa
ya shirya ya fito zaije aiki. Bayan ta gaishe

shi ta shawarce shi tana son ta kai abida
asibitin malam aminu kano a duba to ko
Allah zai sa a dace.
Hussaini yayi shiru can yace kina ganin aje
asibitin nan alhali na tabbatar ba ciwon
asibiti bane, tunda ga kasusuwan sun
kumvura suna ciwo, amma likitocin kashi
sunce basu ga komai ba. Aisha farida tace
ina ga ai ba bangarensy bane, wata kila
ciwon ba a jikin kashi yake ba, gara in kai ta
tunda can akwai likitoci manya manya zasu
gano ciown. Hussaini yace kinga abin da
yasa nace bana asibiti bane, idan tana bacci
sai tayi ta zabura har sai na rirrike ta cikin
dare. Aisha farida tace haka ne yaya, ai
asibitin ma suna da maganin razana da
zabura. Ya lalubo kudi ya bata yace suje,
Allah Ya sa adace. Aisha farida ta harhada
'yan kudaaden da take adanwa na masu
dubiya, misbahi ma dubu daya ya bata,
haka wani yayansu da yazo daga shagamu
shima dubu daya ya bata, taje ta hado
cefanen dambu ta shirya wa rabin ranta dr
shuraim. Bayan ta yi wanka ta fesa kwalliya
da wata doguwar rigarta bakai mai dankwali
(abaya). Sai ta shirya abida aka kirawo
musu mai adaidaita sahu yazo har kofar
gida. Sai da matan gidan suka taimaka mata
aka rirriko abida aka saka ta ciki domin duk
gabar da aka rike mata ciwo takeyi mata.
Sai ta dau kuka kamar wacce ake balla mata
kashinta don azaba. Aisha farida rike da
kwandon abincinta ta shiga adaidaita sahi
suka tafi. Ta dubi abida ta zubo da hawaye
don tausayi tace wannan dambun ne nayi
wa su dr shuraim in kai musu ko in kyale
su? Abida tayi murmushin karfin hali ta cije
baki saboda tsananin ciwo ta gyada kai tace
ki kai masa.
Mai adaidaita sahu ya kai su har bakin
GOPD kafin su sauka, sai aisha farida ta
shiga ciki da sauri tayi magana da maikatan
suka bata kujerar tura marar lafiya. Lebura

daya ta dauko kujerar ta biyo ta da ita. Nan
ma sai da aka agazawa aisha farida sannan
aka dora abida akan kujerar saboda tsabar
ragargazar da kashinta ke yi har kara zaka ji
yana yi bas! Bas! Idan ta motsa. Aka turata
aka shiga dasu wajen bude file kasancewar
duk ta sanu ba ta bi dandazon layi ba aka
bude musu, nan da nan aka mika musu file
din dakin likita. Nan ne fa za asha jira
sabida likitoci basu karaso ba, don haka
dole a sha jira akan bencina. Aisha farida ta
dubi abida wacce har yanzu take kan wheel
chair tace inje ofishin dr lukman in dawo,
zaki iya zama ke kadai? Abida tayi
murmushi tace kije a tsanake ki gama
abinda kike yi, kada ki damu don kin barni,
ni kadai zan zauna a cikin kabarina. Ni kadai
zan zauna babu mai tayani zama, saini sai
halina. Sai aisha farida ta runtse ido yayin
da kuka ya kcece mata, ta kasa magana
saboda jama'ar dake kallonsu. Cikin sanyin
jiki ta dauki kwandon abincin ta tagi.
Hawaye yake ya tsaya har ta kusa isa
ofishin dr lukman don haka ta sami lungu ta
labe tayi kuka har ya isheta, ta goge
hawayen ta fito. Amma kuwa kallo daya
zakayi mata kasan kuka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login