Showing 42001 words to 45000 words out of 99740 words

Chapter 15 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf

Advertisement

ESHAT   

23 Mar 2025

5602

ta zamana mai nadama akan
kuskuren data tafka a rayuwarta a kwanakin
baya a dalilin shuraim sai kuma ta qudiri
niyyar natsuwa da cire duk wani abu da zai
gundiri rayuwarta giftawar husaini ta gani ta
tagar dakinta ya dawo daga masallaci zai
shiga dakinsa sai tayi wuf ta fito ta durqusa
ta gaishe shi ya juyo ya dube ta duba mai
cike da tausayi kasancewar yaga ta rame
idanu wanta duk sun kode mata
musamman data kwana 2 baka kwalli ba ya
fada cikin yar siririyar murya farida lafiayar
qalau kuwa ko baki lafia?tayi sauri ta
sunkuyar da kai qasa gami da yin
murmushin qarfin hali ta girgiza kai tace
babu abinda yake damuna yay yace za a tafi
makaratar ne har kinci dumame?ta gyada
kai tace eh yasa hannu a aljihu ya dauko
wata tsohuwar 200 ya miqa mata kamar
kullun kamar yadda ya saba bata kudin
acaba zuwa da dawowa da kuma na shan
pure water.ta durqusa ta karba tayi godia
ta shiga daki shima ya shige daki tana shiga
ta mistsika yan powder a fuskarta ta gyara
dan guntun hajabin da yake jikinta sai ta
rataya jakarta a kafada gami da saqula 200
a zip din dake jikin jakar ta fito a bakin qofa
suka hadu da abida lokaci daya suka yiwa
juna murmushi Aisha ta gaishe ta abida ta
amsa gami da cewa har kin fito ki tsaya

kisha koko mana.Aisha tace sauri nake
kada na makara supervisor nake son gani
abida tace yunwa kuwa baza ta dame kiba
ba kici komai da daddare ba na jiya da
ranar ma da yawa kika ci ba Aisha ta
langwabar da kai tace ba damuwa idan na
dawo zanci abida ta kuncegefen zaninta ta
dauko 100 ta miqawa farida tace kici abinci
a can don nasan dole kiji yunwa farinciki
yaa lullube Aisha ta karba gami da
murmushi ta duqa tayi godia sannan ta juya
ta nufi hanyar fita harta kai zaure sai taji
muryar abida ni kiran sunanta sai ta juyo ta
tsaya cak!tana dubanta kanar marar gaskia
ta qarso inda take taja. Hannunta zuwa
bayan kyauren zauren.
Ta fada cikin rada daman inaso na tambaye
ki dazu, to nasan halin kunnen hussaini, sai
ya jiyo mu. Hankalin farida ya tashi ta dafe
kirji tace me ya faru? Abida tace dr shuraim
mana, zaku hadu yau kuwa? Kafin kace
kwabo farida ta bata fuska ta kara da kai
gefe, ta zumburo baki. Tace ba zamu hadu
ba. Ta juya a fusace zata fice. Abida ta sake
jawo hannunta tace fushi kike don naayi
mmiki zancen shuraim? Kin daina sonsa ne?
Aisha farida tayi caraf ta fada cike da gadara
da takaici tace eh. Sai abida ta kwashe da
dariya, yayin da aisha farida ta fice a fusace
ko waiwayowa ba ta sake yi ba. A hanya ta
hadu da musbahi ya fito daga gidan akan
babur dinsa zai tafi wajen nema, sai ya
tsaya a kusa da abar kaunarsa yana mata
murmushin kauna. Sai dai kash! Zuciyar
masoyiyar tasa a bace take, sai ta kawar da
kai taki yin dariya ta gasihe shi ranta a
bace.
Wai kwana biyu nan wa yake taba minke?
Musbahu ya fada yayin da yake duban
fuskarta, yake murmushi. Ta kawar da kai
gefe ta fara tafiya ba tare da ta bashi amsa
ba. Yayi sauri ya sake biyo ta, ya tari
gabanta har yanzu yana zaune akan babur

dinsa. Abun mamaki sai yaga hawaye yana
zubowa daga idanuwanta, nan da nan sai
hankalinsa ya tashi ya shiga lallashinta yana
bata hakuri, gami da rokonta ta hau bayan
babur dinsa ya kai ta asibitin. Da farko taki
sai da kyar ta hau suka fara tafiya. Ba tare
da wani ya sake magana ba a cikinsu,
sheshekar kuka kawai farida keyi a ciki ciki.
Cikin marainiyar murya ta ambaci sunansa
tace makarantarmu za ka kaini ba asibiti
ba. Nan da nan ya amsa mata da to...to
farida. Har bakin ofishin malam basiru ya
kaita, ta sauko tayi masa godiya ba tare da
ta dube shi ba. Ya kira sunanta cikin
lallausar murya, ta juyo a tsanake tana
sauraronsa, sai taga hawaye ya surnano
daga idanuwansa, ta sake dubansa sosai, sai
tayi mamaki tace lafiya? Yace farida kiyi
hakuri ki yafe min nima ba da son raina
haka ta faru ba. Ta tambaya cike da
damuwa meya faru? Yace kwanan na ga kin
shiga matsananciyar damuwa, har aka ce an
kai wajen 'yan sanda an kulle ki duk da ba
fada min takamaiman laifin da kikayi ba.
Farida da ace tun sanda kika gama
sakandire muka yi aure, da na killace ki duk
da haka ba ta faru ba. Amma nasan komai
mukaddari ne daga Allah, bawa bai isa ya
tsarawa kansa rayuwar da yake so ba, sai
yadda Allah Ya so dashi.
Sanin kanki ne duk duniya ke nakeso, kuma
har abada ba zan daina sonki ba, matsalar
daga wajen goggo ne ba don ita ta haife ni
ba ina tsoron bakin uwa ba da tuni nayi faci
da maganarta munyi auren mu. Na kasa
son matar da ta aura min, na kasa cire raina
a kanki. Ba yadda zanyi nace kada kiyi aure
ki jirani, idan nayi haka na zalunce ki, tunda
bansan ranar da goggo zata hakura ba
amma kada kiyi gaggawar yin aure ki barni,
kullum ina ta fadawa Allah, nasan kema
kinayi. Toh muci gaba. Farida ta rushe da
kuka, tabbas musbahu yayi gaskiya, abin da

yake ranta kenan, cewar ba don yaki
aurenta ba da ya za'ayi ta afka cikin
wannan hatsarin? Sai ta juya da sauri ta nufi
ofishin da tazo, yayin da musbahu yake
kwalla mata kira taki ta waiwayo ma balle
ta amsa. Tana shiga ofishin taci s'a ta iske
malam basiru yana nan shi da abokinsa
malam sulaiman. Bayan ta gaishe su sai ta
barke da kuka marar kakkautawa, sai suka
shiga damuwa suka shiga yi mata
tambayoyi, lafiya take kuka? Suka bata
kujera ta zauna cikin sheshekar kuka ta fara
bayani. Sannan suka fahimci inda ta nufa da
kuma dalilin kukan nata.
ba 31 da 32 zan ci gaba da 33
Supervisor ya turo hula gaban goshi yace
rashin lafiyar da kikeyi ce ta hana ki aiko
'yan uwanki suzo su fada min ko kuma ki
aiko a rubuce a kawo min? Gashi yanzu sau
biyu ina zuwa duba ku ba kya nan, yaya
kike so nayi miki yanzu? Kije kawai wata
shekarar ki dawo ki maimata attachment
din. Ta sake fasa kuka taci gaba da ba da
hakuri. Mal sulaiman ya dubi abokinsa yace
a'a ba za'a yi haka ba, ka dai duba ka
taimaka mata. Itace fa monitor kasan aisha
umar bata da wasa, lalura ce ta jawo haka
da dai Khadija sani ce, kawarta ba zan ma
shiga zance ba, don nasan bata da kokari.
Malam basiru ya gyada kai yace shikenan
kije nan da kwana biyu zan shigo asibitin in
duba kiki zama cikin shiri dan a koda
yaushe zan iya fadowa. Ta durkusa tayi
godiya. Aisha umar ta fito tana matse
hawaya, amma zuciyarta cike da farin ciki,
hankalinta ya fara kwanciya. Tayi mamaki
da ta iske musbahu har yanzu yana nan
yana jira bai tafi ba. Jikinsa na rawa ya
kunna babur ya karaso inda ta ke yana
tambayarta ta gama su tafi, ko akwai inda
zai kaita kuma? Ta girgiza kai tace cikin
asibiti kawai zanje. Ta hau babur suka tafi
har yanzu ma dai babu wanda yake magana

a cikinsu, tana nuna masa hanya har ya
kaita inda take so, sannan ya tsaya.
Tana saukowa sai taga ya dauko kudi ya
mika mata, dubu daya 'yan dari biyar guda
biyu. Yace karbi wannan bashi da yawa, a
cikin kudin da na ranto miki ne ma zanje na
biya su, amma ba zai gagara ba. Daga nan
zuwa yamma zan cika in biya su. Aisha
farida ta girgiza kai tace ka barshi na gode.
Yace a'a ki karba farida babu komai, a shirye
nake nayi miki duk abin da kike so idan
baifi karfina ba, ko bani dashi zan nemo
bashi na baki. Ta mika hannu ta karba a
kunyace, ta duka tayi godiya. Ta dube shi
sai taji sanyi a ranta ganin annuri a fuskarsa
murmushi kawai yake yi mata naso da
kauna. Ta rike kan babur dinsa tana
murmurdawa ta dube shi tayi fari da ido.
Tace musbahu na gode da dawiniyar da ka
dade kana yi dani, nagode da kulawarka da
damuwar da kayi dani a tsawon zamana da
kai baka taba gajiya dani ba. Ko kadan ban
taba zarginka ba akan rashin aurenmu,
nasan daga inda matsalar take, ina adduar
Allah Ya zaba mana abin da yafi alkhairi
amma ba zan boye maka ba musbahu bana
jin a jikina zamu iya aure, don banson nayi
auren da zan kasance bani da kwanciyar
hankali. Saboda mahifiyarka ta fito baro
baro bata son abun. Koda naji sonka zai
mamaye min zuciyata nakan yi addua Allah
ya yaye min, sai nayi sauri na juya akalar
zuciyata wani bangaren.
Musbahu ya girgiza kai alamar takaici yace
yanzu aisha farida har addua kike Allah Ya
cire miki sona a ranki, koda yake bakiyi laifi
ba idan kinyi hakan, amma ni ban taba
fatan na daina sonki ba, ko da kuwa bama
tare. Wa kike so yanzu bayan ni? Nasan dai
ba zaki rasa ba, tunda a maganarki yanzu
kin furta wata kalma da take nuna
hakan....ke 'yar shagamu, lah lah lah zance
ma kikeyi da sassafen nan? Muryar da ta

jiyo daga bayanta kenan ita da musbahu
suka waiwaya da sauri, maza biyu ne suke
tafe akan doguwar barandar, su dukka suna
sanye da wando da riga na bakar suit
wuyansu sakale da abin gwaji. Ko ba a fada
maka ba manyan likitoci ne. Dr lukman ne
mai maganar, na kusa dashi kuwa dr
shureim ne, daga dukkan alamu daga duba
marasa lafiya suke, domin da daliba na biye
dasu a baya. Ta dubi dr lukman tayi
murmushi ta rufe ido da hannayenta biyu
ta fada a kunyace a'a ba zance nake yi ba,
yayana ne. Musbahu yace yayanmu ai
kanwata ce na kawo makaranta. Gogan
naka dr shureim baice komai ba, amma
yana tafe yana dubanta kasa kasa har suka
wuce. Kallo daya tayi masa ta watsar ba ta
sake waiwayarsa ba, taci gaba da duban
abin kaunarta musbahu, ta shiga yi masa
bayanin inda tasan dr lukman. Abin mamaki
abinda ya sake tsorata ta sai taji musbahu
yana yabon kyawun dr shureim.
Yace shi kuma daya likitan yay sunansa?
gaskia yana da kyau irin wannan ne fa yake
sawa wasu mazan suke hana matansu zuwa
aiki idan suna ganin mazaje kyawawa irin
wannan sai su tsani mazan su sai taji
zuciayarta ta harba bumm! don fargaba ta
tambayeshi me kace?ya maimaita abun da
fada tace a ranta haqiqa na daukowa kaina
ruwan dafa kaina amma Allah ya hayar dani
dana gane gaskia gaskia ce wato 'yar
uwansa maza ma kyawunsa suke gani balle
yan mata lallai shuraim ba sa'an soyayyarta
bane zuciata tayi garajen cusa kanta wajen
ajalinta.tayi zuciayarta ta yamutse fuska
tace bansan sunansa ba nima dai ina
ganinsa dai kawai misbahu yace kina
burgeni farida duk irin kyalkyalin dunia bai
cika damunki ba har dana fara kishi
musamman dana ga yana kallonki qasa-
qasa na dauka shima ya sanki Aisha tayi
murmushi tace ni banma kalleshi ba balle

insan yana kallona kai ka lura da hakan
misbahu yace aini tun daga nesa na hango
su suna tahowa kece baki gansu saboda kin
juya baya tunda ya tunkari mu yake kallo
har na tsorata na dauka shima yana ciki
Asiha tace aa ni ban ma sanshi bama zai
wuce babur dinka yake harara bana ji ance
ya tsani yaga mace ta hau babur.misbahu
ya kwashe da daria yace kai dalibai akwai
sharri waya fadawa haka?a zamanin kuwa ai
sai an hada da hawan babur abu zai tafi dai-
dai ba kowa yake da kudin daukar taxi drop
na musamman mu talakawan da muke
zaune a lunguna koda yake su manya ne
matansu ba zasu hau babur ba sai mota
ko? farida ta tabe baki tace shi ya sani
wannan matsalarsa ce ni har bana son
zancensa ma ya cika dagun kai.
Dadi ya kama misbahu kansa ya fara
huruwa wato saboda sonsa da farida keyi
har bata ganin fuskar wani da namiji sai shi
sai ya shiga washe baki tamkar sakaran
daya ga sabon dinki yace in dawo na dauke
ki idan kin tashi? ta riqe baki ce rufa min
aisir misbahu qasada ce ma yanzu dana hau
mashin dinka a unguwarmusaboda safiya ce
babu jama'a da bazan hau ba sai a yi mana
sharrin da ba zamu fita ba.anga mun fita
tare sannan da yamma aga mun dawo me
kake tunanin za'a ce mana?kaje kawai
nagode sai wani lokaci idan Allah ya sake
hada mu a hanya don goggo ta hana ka
zuwa qofar gidanmu kuma bana so ka saba
mata ta juya ta tafi tabarshi zaune akan
babur yana dubanta zuciyarsa cike da da
tsananin sonta gami da takaicin abun da
mahaifiyarsa tayi masa ina ma za'a hada
farida da matarsa?aiko kusa basu hadu ba
farida mutun ce kuma abar so ce yarinya
kyakyawa mai fara'a ga son mutane iya
magana tafiya a nuste da dadadan kalamai
mai dadin murya da iya kallo da sai kaji
kwakwal war kanka za zillo.ga kyakyawan

halaye bata da hassada ba kyashi ko
mugunta bai motsa ba har sai da ta bace
masa ya daina hango ta yayi ajiyar zuciya ya
girgiza kai ya kunna babur dinsa ya tafi a
sanyaye gabobinsa sunyi sanyi.
DUK KYAN TAKALMI 2* 4
Cikin satin nan kakaf babu abinda farida
keyi sai karatu agida da makaranta. Bata
shiga kawaye, har a gida ba ta fitowa tsakar
gida. Tana lungu ko da yaushe littafiinta ne
a hannunta. Burinta ta kamo 'yan ajinsu
inda suka wuce ta, ga uwa uba a cikin satin
supervisor dinta zai zo ya duba ta. Ta cire
damuwa a ranta, haka bata da sauran
tunani yanzu, sai karatunta. Abinci ma ba ta
fiye son ci ba, sallah ce kawai ta zame mata
dole ta tashi tayi, sai bacci barawo idan ya
sace ta, tayi kadan ta farka taci gaba. Kafin
kace kwabo farida ta rame, kowa ya kalle ta
sai yayi maganar ba ta damu ba, haka bata
tsahirta ba. Burinta taci nasara akan abin
da ta sa a gaba. Duk da wannan jajircewar
da tayi, da dagewa ta haddace kusan duk
inda take tunani za'a tambaye ta daga
kowane bangare na karatunsu zata amsa.
Amma sai ta hada da addua tana mai
neman taimakon Allah akan karatunta.
Alhamdulillah da supervisor yazo dubata a
karo na farko ta amsa tambayayin dukka
har sai da yayi mamakinta. Sati mai zuwa
karo ba biyu ya sake zuwa ya duba ta, a
wannan lokacin ta sake shiri sai yaji
rugurguza tambayoyin da ya jero mata har
ma tana kara masa bayanai akn abin da bai
tambaye ta. Ya jinjina mata, kuma ta burge
shi matuka. Taci maki da yawa don tafi
dukkanin 'yan ajinsu ci. Daga karshe ya
shawarce ta yadda take da kokari ta daina
wasa da karatunta, taci gaba da dagewa ta
fita da sakamako mai kyau, shi kuwa yayi
mata alkawari zai taimaka mata wajen
neman aiki, kuma ko cigaba da karatunta
take so zai taimake ta.

Farida dai sai farin cik take tana yi masa
godia ji take tamkar an sauke mata nauyin
da yake kanta sai yanzu hankalinta ya
kwanta walwalarta ta dawo ta shiga cikin
qawayenta kamar da suka ci gaba da
karatunsu da kuma koyon aikinsu.idan ta
dawo gida taci gaba da wasa da dariyarta ita
da abida da 'ya'yanta duk da Asiha bata
nunawa 'ya gidansu da maqotansu bacin
ranta akan abubuwanda da suka yimata
suna gaisawa sosai tayi musu fara'a amma
ta daina zama cikinsu tayi hira dasu kuma
sai suka dinga jin kunyarta ba kasafai bama
suke iya hada ido da ita ba saboda kunyar
abun da suka yimaya domin Aisha tana da
kirki kuma tana taimaka musu ta kowace
hanya.tun yaya husaini na tambayar kudin
da ka ranta 5k har ya gaji da dadin bakin
abida yayi shiru ya daina tambayarta.ranar
lahadi misalin qarfe goma sha biu na rana
bayan abida da aisha sun gama aikin tsaf
sunyi wanka sunyi wa yaransu wanka sun
tura su islamiyya yayin da yaya husaini ke
cikin daki yana shigar baccin gajia kamar
yadda ya saba ranar labadi ce kawai baya
zuwa aiki itace kadai ranar hutunsa a
sati.don haka abida da yaranta basa garajen
yin shige da fice a dakin abida kada a tashe
shi tunda sassafe take hado musu yan
komatsansu ta kawo dakin Aisha a karo
masa qofa daga ya karya kumallo yake
kwacia saida azahar kuma zai farka.Aisha ta
gama rangawa abida kitso ras a kanta kai ka
ce fula ce akasa dan kyau sannan itama
abida taya ta tsifar nata kan Aisha na
kwance akan tabarta yayin data dora kanta
akan cinyar abida wacce ke zaune ta
mimmiqe qafa hira kala-kala Aisha ke zaune
ke rerowa abida hirar da data yanzu ta
shagamu data kano hade da qawayenta na
makaranta.abida ta dubi Aisha sai tayi
murmushi misbahu kuwa yana nan? farida
ta gyada kai gami da yin

murmushi .misbahu yana nan kin manta
kwanaki na fada miki yabani 1k harna
saywa sa'id takalmi kito? abinda tace haka
ne na tuna Allah sarki misbahu yana sonki
har yanzu amma wannan uwar tasa bata
kyautawa danta ba taci amanar haihuwa
koda yake mijin wata baya auren matar
wani mijinki na nan tafe.Aisha ta dago ta
dubi abida saita mayar da kai ta kwanta
jikinta a sanyaye ta fada cikin marainiyar
murya insha'allahu.Abida tace ina dr
shuraim?
Takaici ya hana ta magana har zuwa wani
lokaci mai tsawo babu wanda ya sake
magana a cikinsu abida tayi ajiyar zucia tace
farida kin cika sarewa baki da juriya akan
abunda kike nema ki zama jaruma ki jajirce
har sai kin sami duk abunda kike so kada ki
tsorata domin qaramin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login