Showing 81001 words to 84000 words out of 99740 words

Chapter 28 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf

ESHAT   

23 Mar 2025

5445

dai nace ta shirya mu tafi shagamu
sai ta dau kuka da ihu.
Dr shuraim ya cika da mamaki kafin yace
wani abu yaya hussaini ya mikawa aisha
farida wayar. Tayi ajiyar zuciya tayi sallama
cike da sansanyar murya. Dr shuraim ya
fara magana cikin tattausar murya. Yace
farida meyasa kike da rudewa ne haka? Ga
yayanki yyace bai fada miki ta mutu ba. Ta
fashe da kuka tace haba dr nifa ba karamar
yarinya bace nagane komai, meyasa za'a
boye min? Ni nasan anty abida ta rasu, ko
an fada min me zanyi, dole in dangana.
Yaya hussaini ne ya sake yi mata tsawa yace
kada ya sake ji tayi maganar rasuwan nan.
Ta rushe da kuka mai tsanani, hankalin dr

shuraim ya sake tashi ya shiga damuwa,
yace yi shiru baby, kiyi hakuri duk mai rai
mamaci ne , dukkanmu nan zaman jiranta
mukeyi. Kiyi mata addua Allah Ya yi mata
rahama. Ki kunna wayarki mu dinga
magana. Tace wayar bata wajena yaya ya
karba ya kashe tundazu da muke magana.
Dr shuraim yayi yace to anjima zan kiraki a
wannan layin. Idan anyi bakwai zaku dawo
ko? Ta girgiza kai kamar tana gabanshi, ta
zubo da hawaye masu yawa. Tace dr
shuraim ina ganin wannan wayar da muke
da kai itace rana ta karshe da zaka a duniya
ballantana ka ganni. Kuka ya barke mata.
See Translation
KYAN TAKALMI 3* 7
Yayi zumbur ya mike tsaye ya dafe kirji
yace farida me kike so ki fada min? Kina so
kice min zaki kashe kanki ne saboda anti
abida ta mutu? Ta girgiza kai tace bazan
kashe kaina ba, saboda nima musulma ce.
Rashin anti abida babban ciwo ne a zuciyata
wanda bazan taba warkewa ba har abada,
kuma duk sanda na ganka ko naji muryarka
zaka zama min fami a wannan ciwon nawa.
Ba lallai bane ka gane abin da nake nufi
yanzu ba, kuma ba zan iya fada maka yadda
zaka gane din ba. Ni kadai nasan abin da
nake nufi da hakan. A sanadiyyar anti abida
nasan ka, da ba zaka sanni ba ma balle ka
fara sona, nima haka ba donn yakin da tayi
ba da tuni na manta da shuraim a
rayuwata. Abida itace silar hada
soyayyarmu, naso ace abida na raye ta
ganmu tare. Ta mutu ba tare da burinta ya
cika ba, komai ya fita a raina tunda babu
abida. Ya daka mata tsawa domin ya gigice
gaba daya da jin kalamanta. Yace farida kin
kuwa san abinda kike fada min? Anya kuwa
kina cikkin hayyacinki? Ta fashe da kuka
tace nasan abinda nake fada likita. Nayi
sallama da kano ko hanya bana so ta biyo
dani ta kano , tunda babu abida. Kayi hakuri

ka yafe min, nasan irin ciwon da zaka ji a
zuciyarka saboda nina fara shiga ciwon so
kafin ka shiga. Sai ta mutsike wayar gaba
daya ta rike a hannunta ba tare da ta
mikawa yaya hussaini ba.
Ya juyo ya dube ta cike da mamaki ba tare
da yasan abinda zai fada mata ba. Dr
shuraim yayi ta gwadar wayar, ya kira yaji
an kashe mudik , sai ya sulale ya zauna
akan doguwar kujerar falonsa yana sosa kai.
Yace innalillahi waiinnna ilaihirajiun.
Meyake shirin faruwa dani ne? Dama
wannan shine cutar son da ake fada a gari?
Ashe ban taba sanin so ba sai yanzu?
Inama zan iya hakura da son farida in huta.
Ya jawo wayarsa a sanyaye ya kira dr
lukman. Cikin sanyin murya yace abokina
kazo muyi magana ka bani shawara , don
ina cikin masifa wacce zata iya kaini da
kamuwa da son zuciya. Farida tace in kyale
ta bazata iya cigaba da son ba saboda babu
ran abida. Dr lukman yayi tsaki yace
wannan ai shirme ne, zafin mutuwa ne ya
shige ta, zata dawo hayyacinta ta neme ka.
Dr shuraim ya girgiza kai yace a cikin
hayyacinta take magana ba zafin mutuwa
bane. Na kasa gane abin da suke nufi.
Yayanta yace min bata mutu ba, ita kuma
tace min abida ta mutu. Abin da na
fuskanta boye mata yake yi don yaga ta
damu. Ga shagamu da nisa kar ta sume
masa a hanya. Dr lukman yace nima na fi
yadda ta mutu don yanzu yahaya ya turo
min sako a waya ta yace inyi hakuri yana
cikin mutane zai kira ni anjima.
Dr shuraim yace idan ba zaka zo ba gani
nan zuwa gidan naka muyi shawarar, don
bansan yadda zan iya yini a cikin wannan
halin ba. Dr lukman yace naga ka damu da
yawa abokina, bari nayi wanka inzo tunda
gidanka babu kowa zaifi dadin magana. Dr
shuraim yace don Allah kazo da wuri ina
jiranka. Suka kashe waya. Dr shuraim ya

kame a zaune ko yatsarsa baya iya dagawa
balle ya tashi yayi wani abu. Shi kansa yana
tausayin kansa da kansa, halin da zai shiga
idan ya rasa aisha farida. Ya rasa yadda
akayi ya zurmuka cikin ramin kaunar ta
wanda yayi zurfin da ya kasa fitowa. Ya fada
a bayyane lallai karshen namiji a karkashin
mace yake. DUK KYAN TAKALMI a kafa ake
taka shi. Sai ya zubo da wani zazzafan
hawaye daga idanuwansa. TABBAS DUNIYA
RAWAR 'YAN MATA CE, NA GABA SAI YA
DAWO BAYA IDAN AKAYI WANI JUYIN.
ASUBA TA GARI LIKITAN AISHA FARIDA!!!
BABI NA GOMA SHA BAKWAI Mako guda
kenan dai-dai da tfyr su aisha misalin karfe
5 na yamma. Dandazon maza tsofaffi ne
suka cika a majalisar hirarsu ta 2ntuni,wato
kfr gdnsu aisha farida. Mahaifin abida shine
ya gaji kujerar tsohon af shine kadai yake
zaune akan kujera sauran dukka a zazzaune
suke akan tabarmi a gefensa. Af ita kadai
ce mace a cikinsu,tana zaune akan kujera,
sauran dukka a zazzaune suke akan tabarmi
a gefensa. Af ita kadaice mace a
cikinsu,tana zaune akan dakali ta lanqwashe
kafa,sanye take da bakr riga abaya ta yafa
dankwalin a kanta. Ta jima tana kallon
tsofaffin nan daya bayan daya,sai ta 2na da
a lkcn da mahifinta yake raye,mahaifin
abida ya juye shi sak! Kmrsu 1 a yanzu
shine babba a cikinsu. Tabbas abida da
mahifinta tayi kama sak! Sai taji hawaye ya
cika mata ido ta grgza kai dn tausayi. Tace a
ranta, Allah sarki, wata rana sai a shafe
kowa kmr ba a taba yin mu2m a doron
k'asa ba. Haka ake tfy daya byn daya. Baba
iliyasu ne ya dubi aisha farida yayi mrmshi
yace, kai girman dan mu2m babu wuya,
kmr ba 'yar yarinyar nan bace, 'yar karama
aisha, yanzu ga yadda ta girma. Af tayi dry
tace,kaima aika tsufa inda zaka san an dade
kenan. Sai suka hau hirar 2na baya,abun
tausayi a jajanta,abn dry a kyalkyace

Tsayuwar wata tsaleliyar mota baka mai
duhun gilashi ce ta katse hirar,sai hnklnsu
gaba daya ya koma kallon motar. Mazaje 4
ne suka bude kofofin moyar guda 4 suka
fito. Af ta cika da tsananin mamakin data
kasa boyewa,sai cimak ta mike tsaye, yayin
da aka hau kallom-kallo a tsakaninsu. Dr s,
Dr Lk, Dr Dayyab da yahya umar ne suka
nufo inda su af suke. Suna isowa sai su
duka suka zube a gaban tsofaffi suka kwashi
gaisuwa. Nan da nan suka matsa musu waje
suka umarce su dasu hawo kan tabarma su
zauna sosai.
Bayan kowannensu ya zauna sai af ta
durkusa ta gaishe su ckn sanyayyar murya.
A lkc guda suka amsa, yayinda Dr S ya kafa
mata ido yana kallonta, ko ba a fada ba
ansan yayi kewarta,sati guda kenan bai
ganta ba. Cikkin kunya kanta a sunkuye a
kasa ta yunkura zata tsh ta shige gida.
Yahya umar yace ta daawo ta zauna zaiyi
magana. Sai taji zuciyarta ta harba, a ckn
ranta ta hau addu'a ALlah yasa alkhairi zai
fada. Numfashinta ya fara cikewa,yayin da
da babu abnda tafi bukat irin ta shige gida
kada ayi maganar nan a gabanta,tasan
koma dai me za a ce ya shafe ta. Ta fada
cikin ladabi,ruwan sha zan kawo muku.
Yahya yace munan ea kika ganmu a koshe
muke,su kuma basa shan ruwan randa irin
naki, sunada ruwansu na rba a mota. Sai
dukkansu sukayindariya. Af ta dawo jikin
dakali ta rabe kmr marar gsky. Ahya
yagyara zama ya dubi tsofaffin yace, baba,
wadannan gudaukun da kuke gani baki
netun daga kano,kuma gaba dayansu likitoci
ne a asibitin aminu kano. Sai tsofaffin
sukasuka hautsine da maganasuna cea,
likita bokayen turesai,ai da ga gani babu
tmby gasu nan a nutse kowanne cikin
kyakkyawan shiga. Wasu shaddoji ne suka
saka masu kyau,kowacce tsasaddiya ce sai
daukan ido takeyi. Farare sol sol anyi musu

dinkin surfani dinkin boda,rigar iya gwiwa.
Su shuraim dai dry kawai sukeyi. Yahya ya
cigaba da byani,ya nuna DR LK yace
wannan sunansa dr lk, babban abokina ne
tun. Una yara a yobe tare mukayi
sakandire. Ya nunaDR S yace ga shuraim
babban liktan fatar da akeji dashi a kano
shima aminin lukman ne, kuma shine yake
so r AIsha FArida. Sai gaba daya suka juyo
suna suka dubeta,tayi sauri. Ta sunkuyar
kkasa yayi akwakalra tsg aito m da y
yanaa,tmakr lma. Tana tmbyr zuciyarta
''ANya kuwaa mafarki nakeyi ba,yau
shuraim ne ya fara mgnr aure na. Allah mai
ikobabu abndaya gagari ubangiji.
Dr shuraiam har yanxxu kallon aishaa f
yakeyi kasa kasa yana soyaga yanayinta da
taji mgnr aurensu. Ya fusknci ta cika da
mamkikuma yaga annuri a fskrta yya karu,
dn haka ya sake csamun kwari. Gwiwar
tana sonsa. Tsofafi sai suka shiga jan
dogayen addu'oi. B.Sule ya dubi farida
yace,ja'ira ashe kin ruso miji kyakkyawa daa
kano haka kikeboyewa. Yanzun nan ika
gama cewa bakidasaurayi. Sai su dukka
suka tintsire da dry,harda ita. Yahya umar
ya nuna dayyan yazxe,wannan sunansa DR
Dayyabu shima a sibitin m. Aminu kano
yake aiki sunaji dashi ko kuma ma ince a
arewa anaji dashi. Reumatologist ne,likitan
daya shafi ciwon cikin kashi da jijyoyi. Shine
likitan daya shafi ciwon abida,dn haka nema
suka tzho dashi. Sai gaba daya suka zabura
suna kalonsa,musamman ma aisha f.
Mahaifin abida ya grgza kai, yace, ciwon
abidaaiba naasibiti bane kada ma ku
wahalar da kanku. Dr lk yayi gyarsan murya
yace, baba ni babu waniciwo da za'a ce
babu maganinsa a asibiti. Kada ku hana shi
gwadawa,abunda ya karanata kenan,aikinsa
ne shiyasa muka tahho dashia. Baban
abidaya grgza kai yaxe, me likta zaiyi mata,
yarinyar da htta gashin knta ya kde

dukka,kan nan kmr anyi mata kwal-kwal,I
wannan aikin kowa yasan iska ne.
KYAN TAKALMI 3* 8
Dr dayyabu yayi murmushi yace ciwon ya
gaji haka, yana zubar da gashi, yana saka
ciwon ido, yana sa mutum yayi ta zabura,
kuma da kumburin gabobi, wani lokacin da
yawan jin sanyi. Idan ciwon ya tsananta zai
iya taba dukkan kayan cikinta kamar koda,
zuciya, mahaifa da kuma kurajen baki. Allah
dai Ya kiyaye. Nan da nan tsofaffi suka fara
gamsuwa da bayanan dr dayyabu, domin ya
zano duk abubuwan da abida take ciki. Ya
kara da cewa kurajen suna iya feso mata a
kirjinta, baya, wuya, da kuma fuskarta. Na
fuskar zai zagaye kumtunta da kuma kan
hancinta. Zai yi siffar malam buda mana
littafi a turance muna kiransa butterfly
rashes. Aisha farida ta dafe kirji tace likita
wannan wane irin ciwo ne? Yaya sunan
ciwon? Kuma me yake kawo shi? Dr
dayyabu yayi dariya har sai da kyakkyawar
wushiryarsa ta bayyana. Ya girgiza kai yace
bazan iya tantancewa ko me yake damunta
ba har sai anyi gwaji. Gwajin ciwon kuma
ba a yinsa a kasar nan, sai a south africa ko
a beiruit. Aisha farida ta dafe kirji yayin da
kake iya ganin gigicewa a fuskarta. Tace
likita yanzu dai sai an kaita can sannan a
gano ciwon? Sai ta fara hawaye saboda
tunawa da tayi basu da wannan gatan.
Dr shuraim yayi sauri yace kada ki fara koke
koken nan. In Sha Allah komai yazo karshe
tunda kika ganmu da likita. Sai ki shekara a
AKTH baki samu damar ganinsa ba, amma
gashi mun kawo muku shi har gida. Kuma
zaiyi mata duk abin da ya kamata har sai ta
ji sauki in sha Allah. Dr dayyabu ya girgiza
kai yace ba sai an dauke ta an kai ta south
africa ba, za dai mu tura jininta wani lab a
abj su zasu aika jinin can idan anyi gwajin
sai su turo mana da sakamakon online.
Idan na duba sai in tantance takamaimain

matsalarta, sai in bata magani. Amma
bayan wancan gwajin mu ma anan akwai
gwaje gwajen da zamuyi mata kala kala
muga ko akwai matsala a cikin jikinta kamar
su koda, zuciya, hanta da dai sauransu.
Kowa yayi tagumi yana kallon bakin dr
dayyabu zuciyarsu cike da fargaba da
tausayin abida. Yayi murmushi yace kada
ku damu, ba wani abu bane na daban.
Anayi kuma ana warkewa sai dai don masu
irin ciwon basu da yawa ne a duniya. Yaya
hussaini ne ya fito daga cikin gida, baba
ahmadu yace yawwa hussaini zo ka zauna
kaji da kunnenka, likitoci ne suka zo daga
kano suna bayani akan ciwon matarka. Yaya
hussaini cike da mamaki yake kallonsu, bai
san sauran biyun ba amma ya gane dr
shuraim. Yazo ya mimmika musu hannu
suka gaisa, ya samu waje ya zauna ya
cigaba da sauraron bayanin dr dayyabu. Dr
dayyabu yace daga yadda yahaya umar ya
min bayani yadda ciwon nata yake yayi min
kama da Systemic lupus erythramatosis
(SLE). Sai kowa ya gyara zama suka mika
tunaninsu gaba daya kan likita dayyabu.
Yaya hussaini yace me kenan? Me yake
kawo ciwon? Dr dayyabu ya lankwashe kafa
yace SLE ciwo ne wanda yake samuwa jikin
wanda Allah Ya dorawa. Lupus is an auto
immune disease characterised by acute and
chronic inflammation of various tissues of
the body. Auto immune disease are illness
that occur when the body tissues are
attacked by its own immune system.
Bansan yadda zan fassara muku ba, amma
dai ba a gado, kuma ba'a daukar ciwon.
Ciwon yafi ga 'yan america bakaken fata
(africam americans) da kuma 'yan chinese
da japanese. Anfi samun SLE a jikin mata
fiye da jikin maza. Kuma yafi kama masu
shekaru ashirin zuwa arbain da biyar.
Malam ahmadu yayi dariya yace likita bokan
turai, ai ni wannan bayanin naka kamar

tatsuniya nake ji, mu nan 'yan chinese ne
da zai zo ya kama 'yarmu? Ai ciwon abida
sammu ne, daman ance tana da makiya a
kanon nan, musamman da awararta tafi
kowacce dadi suka jefe ta. Aisha farida ta
girgiza kai tace a'a baba ahmadu, ka bari ku
bari ya bata magani. Yau wata nawa kuke
yin na sammun amma babu alamar sauki
sai ma ciwon gaba yake ci. Yahaya yace
gaskiya fa tunda yazo a dakatar da duk wani
hayaki a zuba masa ido. Da yawa daga cikin
tsofaffin suka kushe maganin asibitin har da
mahaifin abida. Kadan ne suka goya bayan
likita. Daga karshe yaya hussaini yayi
magana yace ya yadda likita yazo ya duba
abida ko Allah zai sa a dace. Gidan su abida
da gidan su aisha farida babu nisa, don haka
aisha farida, hussaini, yahaya, da likitocin
guda 3 suka dunguma gidan su abida. A
zauren gidan aka iskesu an daukota tamkar
tsumma , wata mata mai maganin gargijiya
ta shafe jikinta sharkab da man shanu ta
tilo mata itatuwa a leda tace ayi ta jika
mata a sabuwar kwarya. Hankalin likitocin
ya tashi da ganin irin wannan kwabe
kwaben. Yaya hussaini yayi wa surukarsa
bayanin likitocin, tashin farko taki
amincewa ita da mata mai magani, tace
ba'a hada aikinta da na asibiti. Yaya
hussaini dai ya takura sai likitoci sun duba
matarsa. Mahaifiyar abida da mata mai
magani suka yi fushi suka bar wurin a
fusace daya ta shiga gida, mai magani ta
fice dauke da buhunta a kai.
Hakika abida tana jin jiki matuka, kamar ba
ita ba, gaba daya halittarta ta sauya, yanzu
ko magana bata iya yi saboda azaba. Sai
gyada kai, sai hawaye kawai zaka ga yana
zuba saboda tsananin wahalar da take sha.
Aka kawo musu tabarmi suka zazzauna
yayin da dogon turanci ya hautsine tsakanin
likitocin uku, likitan fata, likitan kwakwalwa
da likitan kashi da jijiyoyi. Dr dayyabu ya

bude jakarsa (brief case) ya jawo allurar
intramuscular injection wacce ake kira
dexamethasone 8mg start. Ya umurci aisha
farida tazo ta juya masa ita. Yayi mata
allurar sannan ya debo wasu magungunan
kala kala har kala biyar ya mika ma
maigidanta yace lallai a dinga bata
magungunan nan, kuma akan lokaci har
tsawon sati biyu za aga canji In sha Allah
kafin a gama gwaje gwajen jininta, idan an
gama tantance takamaiman ciwon. Dr
dayyabu ya dubi aisha farida yace matso
kusa nayi miki bayanin yadda za a dinga
bata maganin. Ga prednisole nan ta sha
kullum guda uku HOQ daya da safe, daya
da dare, calcium kuma kullum tasha daya.
Sai kuma methothroxate ranar asabar zata
sha 10ml. Ranar lahadi kuma ki bata folic
acid guda 2. Yanzu zan dauki jininta kashi
kashi in tafi dashi, wasu a kano zamuyi
gwajin wasu kuma a abj zamu aika lab suna
harhada jinin mutane da yawa, su tashi
mutum a kai south africa a gwada. Yaya
hussaini ya langabar da kai yace nawa ne
kudin maganin? Kuma nawa ne zamu bada
na wannan gwaje gwajen naji har da wanda
za aika kasar waje. Dr dayyabu yayi
murmushi ya girgiza kai yace kada ka damu
da wannan, abokina shuraim ya gama
shirya komai. Dan yanzu ma lagos zanje in
hau jirgi cikin dare in isa abj in bada
wannan jinin, kwana goma zaiyi sannan ya
fito, to sauran gwaje gwajen ma sai inyi a
national hospital abuja don yawo da jini
babu dadi, duk dr shuraim zai biya. Gwajin
jinin wanda za'a aika south africa ma dubu
sittin za a biya, yace shi zai biya.
Sai aisha farida ta fara hawaye haka itama
abida hawaye ya fara kwaranyo daga
idanuwanta dan tana jin duk abin da ake
cewa. Yaya hussaini ya hau godiya yana shi
albarka. Dr dayyabu ya zaro sirinji da
kwalabe ya zuzzuki jinin abida ya ciccika. Ya

dauko wata 'yar akwati ya jera su ya mayar
ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login