Showing 93001 words to 96000 words out of 99740 words
Chapter 32 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf
zauna
lafiya wadannan matan da suka baibayeta
zasu iya zuge ta ta burkuce. Koma dai me
ye ba ta damu ba ba abun da ya kawo ta ba
kenan. Kuma zata yi iya kokarinta don ta
cika burinta. Ita ma kanta ta ga kyawu da
tsarin gidanta sai ta ji kukan dadi ya rufe
ta,ta yi ta godewa Allah a zuciyarta. Babu
abin da jama'a suke cewa sai addua da shi
albarka da fatan nemar musu zaman
lafiya.Allah ya sa gidanta ne sai dai mutuwa
ta raba. Sai kuka ya sake kece mata a
lokacin da ta ga duk sun watse an barta ita
kadai,fiye da awa biyu sannan abokan ango
suka rako shi. Bayan su dr lukman sun
gama yi masu tsiya da barkwanci suka tafi
suka barsu. Aisha ta iske angonta mai ilimin
addini ya aiwatarda duk addu'o'I da
nafilfilin daya kamata ango ya yi shi da
amaryarsa a daren farko. Ya cika da
tsananin farin ciki mai dimbin yawa,so da
yarda ya karu akan amaryarsa a lokacin da
ya same ta cikakiyar budurwa wacce ta kare
kanta daga wasu mazan kafin ta yi aure.
KYAN TAKALMI 3* 14
Kuskuren da wasu yan matan zamanin nan
ke tafkawa kenan a rayuwa,daga inda suke
fara jawo tsana,zargi,ras hin yarda har
karshen auren,kuma babu inda auren yake
zuwa ake rabuwa idan suka bari wani da
namiji ya fara saninsu a waje. Don haka
dole 'yan mata su yi yaki da zuciyoyinsu su
yi taka tsan-tsan da mayaudaran samarin
zamani ko da kuwa zasu aure su ne to a
guji zina har sai bayan an daura aure. Allah
yasa mu dace.
Satin ango guda a dakin amaryarsa kamar
yadda shari'a ta tanada.sati guda nan da
yayi ya fiye masa shekaru hudun da yayi da
aurensa a baya,don ya sami nishadi.
Lallausan lafazai,ladabi da girmamawa
bayan abinci masu dadi daga wajen
amaryarsa. Ya yi wa Allah godiya da ya sami
farida a matsayin matarsa. Ya kudiri niyyar
cure ta ba zai bari ta subuce masa ba a
rayuwarsa. Sai yaji bambarakwai da ya
koma bangaren fa'iza saboda rayuwar hutu
ta iya.sai sha biyun rana take tashi daga
bacci. Kafin ma ayi maganar abun karin
kumallo kuma ba ita zata yi ba.kofa zata
budewa masu aiki su shigo gidan daga can
bangarensu.kuku ya shiga kicin,mai shara
da wanke- wanke da goge-goge ta
fara.wanka kawai zata yi ta ci ado da riga
da wando ta zauna a falo tana game ko
kallo. Anci sa'a dai tana sallah da zarar
lokaci ya yi sai ta tashi,bayan wannan bata
san a yi wa miji wahala ba. Da zarar ya bata
mata rai zaka ji tana ce masa 'you are very
stupid' su a can karamar kalma ce wannan
dan mace ta furtawa miji. Sabanin abin da
ya ga farida na yi. Tunda asuba take tashi
ta shiga hidimar miji da kalkale gida,ta ce
ba ta bukatar masu aiki.ko cokali zata ba
shi sai ta durkusa har kasa,haka idan ya kira
ta. Sai yake jin kansa yana fasuwa tamkar
ya zama sarki,sarki da ake girmama shi a
fadarsa. Hutu ya dauka daga wajen aikinsa
yayin da ya sa farida ta rubuta takardar
barin aiki saboda ba ya bukatar ta yi ta
wahala saboda dan albashi. Ya yi mata
alkawarin zai bata babban aiki da zarar sun
kammala ginin katafaren asibitin da suke
ginawa shi da mahaifinsa a zoo road. Shi dai
ba zai bar aminu kano ba zai dinga shiga
lokaci2 amma zai fi ba wa asibitinsu
muhimmanci. Kafin nan faiza ta kammala
karatunta ta dawo gaba daya ita ma sai ya
sakata a asibitin a bangaren data karanta
wato acct section. Watanni biyu faiza tayi
tare da farida kafin lokacin jarabawarta yayi
don sun kusa fara jarabawar karshe.
Shureim yayi kokarin samarwa aisha visar
london,kamr ta sa har ta tsawon shekaru
biyar duk sanda suke son shiga sai si shiga
kawai. Don haka shuraim,farida da faiza
tare zasu tafi su yi zaman wata biyu har sai
ta kare su kauro gaba daya. Takaici ya
cikawa faiza zuciya don bata so ba shuraim
yace zai taho da farida,da ta so su tafi su
biyu abar ta saboda a fara zame mata
barazana wajen dauke zuciyar mijinta. A
cikin watannin nan biyu data yi Aisha ta
gama da mijinta,ta gama da iyayensa,ta
gama da danginsa kowa yana sonta saboda
da'arta,kyauta, ladabi,iya karbar baki dss.
Har wasu na tunanin ko da wani baki. Asiri
ta shigo ta asirce gida gaba daya, yayin da
masu hankali suka lura tsabar kirkinta ne da
iya zama da mutane ya jawo mata duk
wannan.
Abida tayi mata nasihohi masu ratsa jiki a
lokacin da ta je ta yi mata sallama zasu tafi
london su zauna har tsahon wata biyu.
Aisha farida tayi mata alkawarin yin amfani
da duk abunda take fada mata,kudi mai
dimbin yawa ta tulewa abida da mijinta a
gabansu har sai da suka tsorata da ganinsa
suka tambaye ta in da ta samu. Ta shaida
musu shureim ne yake bata kyauta wani
ragowar na cefane ne don kudi mai yawa
yake ba su kullum har ya fi karfin na
cefanen. Sannan mahaifin shureim ya ba su
kudi(dollars) mai yawa da zasu yi wannan
tafiyar kadan ta dauka ta canza musu
sauran. Ta umarce su da su cika su sayi fili
a unguwa mai kyau a hankali zata gina
masu. Kafin ta tafi sai da ta turawa
kanwarta munawwara kudi dubu hamsin ta
fara yin jari kafin ta dawo. Wannan shine
karo na farko da aisha ta fara hawa
jirgi,suka hay daga bab zuwa lagos daga can
suka hau zuwa london. A katafaren gidan
mahaifin shureim suka sauka sai dai su
kaiwa mahaifiyar faiza ziyara.babu irin
kallon banza da wulakancin da yan'uwan
faiza basa yi mata idan taje gidan,har
shuraim ya fara jin haushi ya fara kin son ya
kaita,ita kuwa sai tayi ta rokonsa sai sun je
tare saboda tasan kishi ne kawai ke
damunsu. Da suka zauna da ita sai suka
fara gane halin aisha tana da kirki suka fara
sakar mata fuska,haka baby yar gidan faiza
ta shaku da ita sosai koda yaushe suna tare
duk inda zasu je. Aisha tayi kallon duniya
da abunda ke cikinta kyau da tsari a garin
london ba'acewa komai. Sun zagaya koina a
birnin har sun shiga kasashen da suke
makwabtaka dasu don bude ido sunyi
siyayya sun shakata su dukka ukun.
Watanninsu biyu a london faiza ta gama
zana jarabawarta ta karshe ta kammala
degree,sannan suka dinguma suka wuce
saudiyya,ya zo daidai da lokacin aikin hajji
suka sauke faralli,duk da su shureim ba
hajjinsu ta farko ba ce.farida ce ta farko. Ta
nutsu ta yi hajjinta yadda Allah yace,sannan
ta yi addu'oin nemam zaman lafiya da
kwanciyar hankali a aurenta,da rayuwarta ta
duniya da lahira gaba daya. Tayi wa Allah
godiya da ya bata wanda take so a duniya
shi ma yana sonta kuma yana kula da
ita.suka dawo gida kano aka bude sabuwar
rayuwa zama ne na din3. Aka samarwa
baby makaranta mai kyau a akno ta shiga.
Bayan an kammala ginin asibitin aka saka
masa suna imran memorial hospital,ya
samarwa kowacce a cikinsu ofishinta a cikin
asibitin da albashi mai tsoka.
DUK KYAN TAKALMI 3* 15
Af mai kula da dukkan nurses da leburorin
asibitin, yayin da fa'iza ce mai kula da duk
kudin da yake shigowa asibitin, abban
shuraim shine mai kula da duk likitocin da
suke asibitin, shima yana zama ya kula da
masu matsalar fata kudine sosai ake biy
kafin a ganshi. Dr lukman yana zama a
asibiti duk ranar litinin da laraba, dr
dayyabu yana zuwa duk ranar alhamis da
yamma. dr janan mu'azzam likitar mata
(gynae) duk ranar juma'a sda asabar da
yamma. Dr muhd lktr tiyata yana zuwa duk
ranar talata da laraba.dr ruqayya lktr yara
tana zuwa ranar lahadi da juma'a da
yamma bayan likita daban daban da suke
asibitin na dindindin. barr. mu'azzam shine
babban lauyan asibitin shima da ofishinsa a
ciki don haka duk wani mai isa da kudi da
mulki a kano koma ince a kasan nan ya
bude file a asibitin nan saboda iya aiki
tsafta da tsari. makudan kudi suke samu a
kowacce rana wanda yake isarsu su biya
duk wani ma'aikaci hakkinsa dakuma karo
kayan aiki daga kasar waje. bayan shekara
1 dr.s ya dauki nauyin karatun AF don ta
karo ilimi abangaren nurse, tayi amfani da
takardunta suka bata shekara 1 n half zata
sami shaidar degree akan nursin.Hutu
kawai take zuwa nigeria kuma da albashinta
take zuwa bayan kudin abinci da shuraim
yake aika mata.kan ka ce kwabo AF ta
rikide gaba daya ta zama yar gayun gaske,
haka kyakkyawa har kamar sai an wanke
hannukafin a taba ta.
haka naira da pounds sun zauna mata, tuni
ta kaftarawa su yaya hussaini gida mai
tsananin kyau a unguwar jan bulo, ta siya
musu motar hawa. ta canza masa aiki ta
samar mas a asibitinsu a matsayinsa na mai
kula da masu gadin asibitin suma da
ofishinsu. kan ka ce kwabo rayuwar hussaini
ta canza dashi da iyalansa tayi kyau, ya saka
'ya'yansa a makaranta mai tsada, shima
kansa da abida har suna iya taimakon
danginsu na shagamu ba sai sun jira AF ta
aiko musu ba. Allah bai bawa AF haihuwa
da wuriba har sai da ta kammala karatunta
ta dawo gida, sannan ta samu ciki don a
lokaci faiza ta sake haihuwar mace mai suna
fadila har ta yayeta. santalelen jariri AF ta
haifa mai kama da shuraim aka saka masa
suna imran, sunan mahaifin shuraim. yadda
abba yake ji da imran kai kace bai taba yin
jika ba a duniya sai a kansa. wannan kauna
ta samo asaline da kaunar da yakeyima
uwar dan
wato AF a sanadiyyar kula da girmamawan
da take masa. idan kaji abba yayi kukan
yunwa tabbata AF bata kasan don da
tananan gida ko office xata aiko masa da
abinci kala kala kamar kunun gyada,
tsamiya, kanwa, dalayi da sauransu. idan a
bangaren abincine dambu, danwake,
kwadon zogale, rama, masa, sinasir, wainar
'yar tsala, farfesun kaza ko naman rago
amma dahuwardadawa na gargajiya shi
yafiso. haka take yiwa mahaifiyarsa
hidimomi na dafe dafe da ladabi da
biyayya. komai takeso kan tace tayi har tayi
mata, don haka suke son AF ba don faiza
taji haushi ba sai don bazasu iya boyewa
ba. ita kanta faiza baza ta iya cewa AF tayi
mata laifi ba sai dai kawai tayi kishi da ita
don ta aure mat miji,amma babu wata
kyautatawa da girmamawa da bata yi mata
ita da 'ya'yanta. a dole Faiza ta fara
canzawa tana kwaikwayon wasu
abubuwanda AF keyi duK da bazata iya yin
duka don bata saba da wahala ba.
yau falon AFa cike yake da kawayenta kai
kace hada baki sukayi a rana daya suka
kawo mata ziyara har su hudu kowacce
kuma da ban tazo. hidima kawai AF take
tayi masu da kayan abinci, lemo da kayan
marmari kalakala. maimuna kanwar abidace
ke zama a gidan tana taimakonta da
hidimomin gida kuma take rike mata yaro.
suka jera musu kayan dadi kalakala babu
wacce bata cika tumbinta ba a cikinsu har
suka bari. bayan ciki ya dauka sai murya ta
washe sannan falo ya hautsine da hira.
hoton shuraim da AF khadijah sani isma'il ta
kafawa idanu tayi ta kallo,can tayi ajiar hrt
tace "ikon allah ashe dr.s mijinkine, mukayi
ta wahalar da kanmu a kansa? maryam
ahmad tayi ajiyar hrt ta sake rungume
danta tana jijjigawa tace " matar mutum
kabarinsa kana taka allah na tasaa.gashi
nima na auri miji mai sona ina jin dadin
zama dashi. rakiya musa tace, "nifa da gani
nayi kamarAF ta tsani dr.s basa shiri kwata
kwata." ummi yasar tace" ai ni yau takanas
zuwa nayi in dauki darrussa akan
zamantakewar aure. yanzu yasar ya dan
fara yabawa da hankalina shiyasa ya mayar
dani gidansa sai dai kash! har yanzu
kishiyata surayya ta fini fada a wajensa duk
da haka dai muna zaune lfy da ita da
surukata da facalata. yanxu so nake in
samu in sake shiga hrt dinsa ba da neman
gudunmawa daga bokaye ba kamar yadda
nayi imanin bakya bin bokaye amma kika
sami shuraim. kin zama abar kwatance a
cikin mata. kece babbar malamata wacce
tayi min silar canza rayuwata daga
gurbatacciyar hanya zuwa hanya
madaidaiciya. ada na sha wuya a sanadiya
bacewar basira na sabawa mahaliccina"
A.f tayi tagumi tana kallonsu 1by1 har suka
gama maganarsu. murmushi kawai takeyi
yayin da dadi ya kamata tana farinciki da
suka gane komai. ta gyara zama tace
"nagodewa Allah daya ganar daku, nadode
da kyautar da Allah yayi min a duniya wacce
zata zamemin hanyar shiga aljannah a
lahira. dan daga lokacin da mace tayi dace
da samun miji ngari addininta ma ya gyaru.
mace dakinta guda2 ne gidan mijinta sai
kuma na2 kabarinta, na shiga gidan mijina
ba fita inshaAllah sai kuma kabarina ne ya
rage
nabi ta hanyar data dace na auri masoyina
da nake yimasa soyayya saboda Allah,
narike kissar matar nan data debo nonon
'bauna ina lallashinsa muna zaune lafiya
sannan na rike nasihohin nan guda goma
wanda Abida tayimin a ranar walimar
aurena wacce uwa ya kamata tayiwa 'yarta
a ranar da za'a kaita gidan miji. na haddace
su a kwakwalwata kuma ina yin amfani dasu
ina ganin falalarsu. a yau shureim baya
kallon wata mace a duniya sai ni AF, baya
son ya jiyo muryar kowacce mace sai tawa,
bashi da wani tunani sai nawa kuma babu
boka ba mallamai sai tsabar kyautatawa
shima kuma bashi da buri a duniya irin ya
kyautata min. wannan kishin da mata
sukeyi da kishiyoyinsu baya gabana bantaba
saka mata ido ba inga abunda takeyi balle
inji haushinta haka bani da burin in koreta,
burina kadai in zauna da mijina
lafiya.shureim yana da adalci a tsakaninmu
baya bambamtamu. a halin yanzu na
mallaki komai a duniya daidai gwargwado,
motocinmu na hawa na zamani guda
bibbyu babu ta kasa da million4
suturuna masu tsadar gaske, mayukan
shafawa da kayan kwalliya masu tsada
(designers), abinci sai wanda na zaba
zanci.shureim baya dannewa iyalansa
hakkinsu tsakanina dashi sai addu'ar
Alkhairi da fatan yazi gaba da samun budi a
rayuwarsa ta duniya da lahira.yayimin
komai sannan yayiwa 'yanuwana dan yanzu
dangina 'yan shagamu sunyi sallama da
wannan dankararren talauci da muka sha
fama. na dauki nauyin 'yan sakandire da
yawa harsu gama,na dauki nauyin masu
shiga jami,oi
DUK KYAN TAKALMI 3* 16
na dauki nauyin taimakawa iyaye da suka
tashi aurar da 'yan mata da kayan daki ko
samarin da suke hada lefe.kanwata
Munauwara ta rabu da turmutsitsi da
wahalar zaman haya na siya mata gida a
shagamu mai kyau na siminti, na bawa
mijinta motar haya bus yana tuki yana
samun na cefane, na biya mata makka taje
ta sauke farari ta dawo na hada mata jari
tana 'yar sana'a a cikin gida tana samun na
batarwa,ita da 'ya'yanta suna saka sutura
masu kyau suna makaranta mai kyau.
Musbahu tsohon saurayina kuma tamkar
dan uwana yanzu shima nayi masa rana don
na bashi dubu saba'in ya kama shago na
siya masa computers 3 da injin photocopy
ya bude business center tasa ta kansa ya
daina aiki a karkashin wasu. sai ga mamarsa
data tsaneni da matarsa an rakosu gidan
nan tana ta kuka tana neman gafara a bisa
tsana da cin mutuncin data yi min a
baya.harda cewa dama ace baya zata dawo
mana data bar Musbahu ya aureni ashe ina
da mutunci haka.tayita kallon gidana tasan
nayi musu zarra,
kyauta ta ban girma nayi musu na suturu da
kudi mai yawada zasu tafi kadan kenan
daga irin rahamomin da Allah yayi min duk
a sanadiyyar shureim bai rageni da komaiba
dan nima ban rageshi da komai ba.khadija
tayi ajiyar zuciya tace"ai ko baki fada ba
Aisha umar kallo 1 za'ayi miki mu2m yasan
kina cikin daula,jikinki ya nuna kuma muma
shaidu ne don babu abinda bakya yi
mana,kici gaba da godewa Allah sai ya kara
miki"Ummi tayi ajiyar zuciya tace"shiyasa
nazo daukar darasi kibani dama indinga
zuwa
kullum har tsawon wata guda inji ina ganin
abubuwan da kikeyi ni ban iya komai ba.AF
tayi dariya tace"zaki iya zuwa kullum amma
banda ranar weeEnd don mijina yana
gida"Ummi tace to, a wata zan zo sau
KWANA ASHIRIN DA HUDU. Saboda naga
alamar har yanzu GANGAR JIKINSA NA
AURA, zuciyarsa na wurin amaryarsa
surayya. gara inkoma kacokan indinga koyi
da abinda YARENA ADDININA, yazo mana
dasu.duk wanda na tara na fada masa
abunda Yasar yakemin sai yace INA RUWAN
WANI, dan abaya anyi min shaidar tsiya
as sanni da bin bokaye. nakan cewa Yasar
KAI KAFI CANCANTA' ka lura da cewar na
canza yanzu bana bin bokaye irinna da bai
cika kallonaba ma balle yasan nayi kwalliya
tsabar yariga dayayi min shaidar kazanta
abaya.sai Ummi ta fashe da kuka.Khadija ta
tabe baki tace wannan shi ake kirada ADON
DAWA'kenan kinyi kwalliya abanza don
baya lura"AF tayi murmushi ta dafa kafadar
Ummin Yasar ta girgizata tace"kwantar da
hankalinki kawata,sannu ahankali zaki gane
kan mijinki.Yasar zai zama takalmin takawa
tana rufe bakinta sai ga Dr.shureim ya
shigo, ya dubesu 1by1 yayi murmushi. yace
Farida, hakika ni takalmin kafarki ne, nayi
miki lamuni ki takani kije duk inda kikeso
dani 'DUK KYAN TAKALMI' a kafa ake
takawa......................**
*************** ***************
*************** *********ALHAMD
LILLAHI karshe
DUK KYAN TAKALMI 4
Aisha farida tayi karfin hali tace ba
damuwa, ai laifina ne dan banyi kama da
mai kamun kai ba, tunda ba'a tambaye ni
ba nazo na fara yi muku surutu, nasan ba'a
son mace marar kamun kai. Barr muazzam
ya girgiza kai yace zuwanki nan ba laifi bane
dan kin zo kin zauna a kusa damu, kujeru
ne a jejjere kowa zai iya zuwa ya zauna. Da
kika zo kika same mu kinyi mana sallama
duk da tun kafin mu amsa har kin zauna.
Daman kamata yayi ki gabatar mana da
kanki kuma kinyi hakan sai dai kika zarce da
bamu labari shine abinda ya daure mana
kai kenan. Kallon junan da kikaga muna yi
ina tunanin ya sanki ne, shima yana tunanin
ko na sanki ne. Aisha bani labarin
takamaiman abinda