Showing 75001 words to 78000 words out of 99740 words
ni'imar da yayi masa. Idan suka cinye
wannan kwanon sai su janyo wani, a na
janyo kwanon Aisha farida dr shrm yaji a
jikinsa wannan na Aisha fard ne,saboda
wasu dalilai da yaji a jikin sa, na farko ga
irin food flask din da take kai musu abinci,
na biyu ana budewa yaji irin kamshin
abincinta na ukku kuma ga irin dambun da
take kai musu. Ya dauki buta ya wanke
miyar kukar da ta bata mai hannu, sannan
yazo ya luma hannu cikin dambun da shi
aka ida cinyewa cin gaske yai ma dambun.
Kuma yana farin ciki don yasan daga
masoyiyarsa ne. Ko tantama ba yayi yasan
saboda shi tayi dambun nan saboda da
zafin sa kauu! Ba a dade da sauke shi ba,
yasan tana da labarin yana nan bai tafi ba.
Tunda ga kan abincin nan yasan farida ta
fita daban da sauran matan unguwannan,
girkinta yafi na kowacce mace dadi da
tsabta, haka yaji sauran mazan suna santi
da yabawa. Saboda tsananin ansan cewa
shine mai dadi sai aka barshi shine karshe.
Da suka gama ci sai suka wanke hannu, dr
shrm yaga alamar ya hssn bai da niyyar
sake mike kafa yai ana sabuwar hira, sai ya
mike ya babba su hannu yayi musu sallama,
da alama ya hssn bai da shirin biyoshi su
kebe, don haka sai ya dube shi yace yayana
zan tafi kuma ban gama baka sakon da
nazo ma da shi ba. A dole ya taso ya biyo
dr shrm suka tafi can gefe guda suka tsaya.
Dr shrm ya dubi ya hssn har yanzu sai cin
magani yakeyi, zuciyar shi zuciyar shi tana
yi masa kuna amma ya daure ya duka yace
yayana zan koma amma fa bazan bar kofar
gidan nan ba sai naji amsa daga bakinka.
Amsar me ya fada cike da gadara. Dr shrm
yai ajiyar zuciya yace ka bani dama in zauna
da ku ahankali zaka san ko yaya nakeson
farida. ... Wurin is not clear.. Tana da
bukatar nazari sosai, ka bani lokaci har sai
na nemeka. Dr shrm yayi shiru na wani
lokaci yana kallon ikon Allah, ya rasa me yai
ma ya hssn haka ya tsane shi, ko da wasa
bai taba tsammanin zai tsinci kansa a cikin
hali na wulakanci irin haka ba, lallai ashe da
bai san rayuwa ba sai yanzu ya fara sani?
Da kyar ya bude baki yayi magana yace to
yaya na gode ISA zaka sameni mai
kiyayewa kuma da yin biyayya akan duk
abinda kace, kuma yadda kace haka za'a yi.
Ka bani lambar wayarka sai na kiraka naji
duk abinda ka yanke. Ya zaro dalleliyar
wayarshi sai yaga msd calls din AF har guda
ukku, yay hssn ya karanto mashi nmbr ya
rubuta ya kira nmber ya hssn ya ciro
kwarabbyar wayarsa ya kalli nmber yace to
na gani zan adana nmbr. Dr shrm yayi
godia suka yi sallama ya nufi motarsa yayn
da ya hssn ya dawo kofar gida inda ya barsu
ya iske su suna hira da suka ganshi ma basu
daina yi ba domin yaji abinda suke fadi.
Mllm sadisu ne ya dubi mllm yushau yace
ni wannan ba shine mutumin da suka zo
wajen AF ba wadanda suka zo da wata
babbar mota ba, mllm yushau yace shine
mana ai daga ganin wannan yaron
mayaudari ne, ba maganar aure bace ta
kawo shi. Malm lawal yace to ni ba wannan
ba ma, mutumen da ba'a san asalin sa ba
ba'a san asalin kudin suba. Ya hssn dai yana
gefe yana kallon su yayin da zuciyarsa ta ci
gaba da gasgata zancen su, mllm sadisu ya
kalli ya hssn yace kai yaro ne kuma kai bako
ne mu muka san kano muka san mutanen
ta, don haka ka gaggauta raba shi da
kanwarka, gara dan unguwa da aka san
asalinsa da sana'arsa. Sauran ma suka
tsoma baki suna goyon bayan abinda mallm
sadisu ya fada. Ya hssn yaji kanshi yai nauyi
kamar zai fashe saboda toshewar tunani, ya
yanke a ransa raba AF da Dr shrm shine
abu mafi sauki a rayuwarsa. Dr shrm ya kira
AF yana fitowa daga unguwarsu, basu daina
magana ba har sai da ya iso gate din
gidansa, mai gadin sa ya bude masa gate.
Ya shaida mata ya iso gida zai shiga yayi
wanka ya ci abinci zai kirata kafin ya
kwanta. I love you baby ita ce kalmar
karshen da yake gayama duk lokacin da
suka gama waya.
Ta sulale ta kwanta akan tabarmarta don
dadin da zuciyarta keyi, Dr shureim yayi
mata hira mai dadi wanda bai taba yi mata
irinta ba tun sanda suka hadu, ya fayyace
mata abinda ke cikin ransa watau irin
dimbin kaunar da yake mata, yace ta
kwantar da hankalin ta, duk rintsi yana tare
da ita babu gudu ba ja da baya. Yana da
kykkyawan zaton matsalolinsu sun kusa
karewa saboda ya fara shawo kan ya hssn
sannan ya shaida mata ra'ayin sa akan ta
idan Allah ya ruboto mas uzasu zamanto
miji da mata yana da ra'ayin ya aureta.
Dama ta dace da irin matar da ya keson
zama da haka ma mahaifinshi. Dukkan
godia sun tabbata da Allah SWT abinda
Aysha f take ta maimaitawa kenan take
kuma fadi a zuciyarta. Kamar bango zai
tsake ras haka ta ji ana ambaton sunanta
muryar yaya hussain ne daga dukkan alamu
a fusace yake. Sai tayi firgigit ta tashi zaune
ta dafe kirjinta tana fadin innalillahy wa
inna ilaihir rajiun! har yanzu bai daina kwala
mata kira ba sai ta mike da saukri, tana
amsawa muryarta na kakkarwa ta fito da ga
dakin ta sauri ta iske shi a bakin kofar
dakin, tayi sauri ta durkusa a gabansa cike
da ladabi. Ki biyoni dakina ya fada a fusace
sai ya juya.... Maganar boye boye ta kare
dan kowa yau zai fadi ra'ayinshi yau ita da
shi, don daga dukkan alamu baiyi amanna
da zuwan Dr shrm ba itama kuma ba zatayi
amanna ya raba ta dashi ba. Ayau tayi
damarar tunkarar duk wata muzgunawa,
zagi, duka da duk bakaken maganganun da
zai yi mata, don ba zata iya dadada masa
ba ita ta kuntata rayuwarta. Bata taba yi
masa mus ba amma yau zata fara saboda
kyakyawan takalminta Dr shurm. Ya hussn
ya shiga daki ya zauna a gefen katifa yayin
da AF ta tsugunna a bakin kofa. Ya daka
mata tsawa shigo ciki ki zauna munafuka.
Ta shige lungu yayin da jikinta yake ta rawa
don fargaba. Ya dade yana harbo mata
harara, takaici yasa ya kasa magana, can
yayi tsaki yayi ajiyar zuciya yace. Farida
yaushe kika zama jin magana, marar daukar
magana? Waye yake zugaki kike yin abinda
kika ga dama? Wai ke kin waye ko kina
ganin yanda wayayyun kawayenki sukeyi
kina kwaikayonsu, to bari kiji in gaya maki
bazan dauki nauyin wannan a gidan nan ba.
Ta sunkuyar da kanta kasa ta kasa magana
sai hawaye ne ke ta kwarara daya bayan
daya. Yay hssn ya ci gaba da magana cikin
fusata tun rannan na fada maki kada ya
sake zuwa baki ji ba, a waya nace kada kije
wajen sa kika fita din, in yaso in kashe ki.
Sannan yazo ya nace man yaki tafia sai na
saurtare shi, to ki fada masa karshen
magana kar in sake ganin kafarshi a gidan
nan don kowa yasan yaudarece yakeyi ba
auren ki zaiyi ba. Yaje can ya auro dai dai
shi yar masu kudi, kima ki samu talaka dai
dai ke ki aura yafi kwanciyar hankali.
DUK KYAN TAKALMI 3* 5
Ta sa hannu ta goge hawaye ta gyara
durkuson da takeyi, ta dube shi duban keke
da keke tace yaya hussaini naji abinda kace
amma naso ka bani dama nayi maka bayani
kaji ta bakina nima tunda kaji ta bakin masu
kawo maka gulman. Ya fusata yaji tamkar
zai kai mata bugu sai ya fasa. Ta fada cike
da tabbaci tace mutanen gidan nan mata
da mazansu, wadanda ba sa kaunarmu da
alkhairi. Burinsu kullum suga mun tozarta.
Baka sani bane dan baka zama dasu a
gidan. Ya sake fusata yace da na turaki
karatu makaranta aka tura ki asibiti sai
akace kije jajibo soyayya? Ashe daman ba
karatun kike yi ba? Ke gwanar iya magana
zakice min magulmata ne suke hadawa?
Bangani da idona bane ko bai fada min shi
likita bane daga asibitin? Ni bani da hankali
sai wani ya fada min? Toh barikiji farida
bake babu mutumin nan, idan kina so ki
cigaba da jin dadin zama dani a rayuwarki.
Farida ta dago da sauri ta dube shi tace naji
abinda kace yaya, na yadda da abin da ka
fada, amma ka sani raba ni da shuraim
dinnan da kake kokarin yi tamkar rabani da
raina ne.
Sai ya dago ido da sauri ya dube ta yayi
mamakin ganin idanuwanta a tsaitsaye tana
magana cike da tabbaci ko alamar kuka ma
babu. Ta sake cewa shuraim bashi da aibu,
kuma shi mai sona ne tsakani da Allah. Ina
son shuraim fiye da yadda yake sona kuma
sai da naci uwar wahala kafin na same shi.
Anti abida tafi kowa sanin yadda abubuwa
suka faru. Babu irin masifun da ban shiga
ba a sanadiyyar sonsa. Sai yanzu da Allah
Ya amshi adduata ya kawo min shi har gida
sannan zasu zuga suce a raba mu? Ya sake
cika da mamaki da jin kalamenta, yaci gaba
da yi mata duba na rashin fahimta. Can
yace farida me kike so kice min? Kina nufin
kun dade tare dashi? Tun abida na da
lafiya? Aisha farida ta muskuta ta zauna
sosai ta fayyace masa gaba daya labarin
abin da ya faru tsakaninta da dr shuraim
tun daga ranar da ta fara ganinsa a duniya
har zuwa rana irin ta yau. Yaya hussaini yayi
shiru yana jujjuya maganan nan yadda abida
tayi kicin kicin a cikin maganar. Sai yanzu da
ta fada masa wannan labarun yake ta
tunano wasu abubuwa da ya gani suna
faruwa. Shiru kawai yayi musu. Misali a
ofishin 'yan sanda ance wani namiji ne yazo
ya fito da aisha farida babu mace yayin da
abida tace masa mata da mijinta ne suka
fito da ita. Haka yana sane da girke girken
da sukeyi da asuba a jujjuye a sababbin
foodflask , idan ya tambaya abida tace mara
lafiya ake kaiwa kawar aisha farida
Yaya hussaini yana matukar son abinda
abida take so, shima zai so ace ya cika
mata burinta koda bata raye. Yayi mata
nuni da hannu alamar ta tashi tafi ya
sallame ta don ya kasa sake cewa komai.
Aisha farida tayi wuf ta fice daga dakin
yayin da ta danji sanyi a cikin zuciyarta don
taga alamar zai saduda. A cikin daren sunyi
waya da dr shuraim kuma ta shaida masa
yadda sukayi da yayanta. Duk da dai bata
fada masa duka ba amma ta fada masa
abubuwan da ta fada masa cewar raba ta
dashi tamkar yana shirin raba ta da ranta
ne. Sai dadi ya rufe dr shuraim, ya cika da
mamaki. ASUBA TA GARI 'YAR SHAGAMUN
LIKITA!!!
BABI NA GOMA SHA BIYAR "Zuwa nayi ki
maimaita min kalmar da kika fada min a
waya a daren jiya. Inji dr s yake fadawa af a
lkcn da suke tsaye a kfr gdnsu suna zance
da yammacin ranar asabar. Af tayi mrmshi
tasa hannu ta rufe ido dn kunya. Yace,
daman na sani ba zaki iya fada ba,idan kika
ganni amma a waya harda fada da
maimaitawa. Toni bari na fada miki 2nda
ba zaki iya fada min a fili ba. Ina sonki kmr
yadda kaza take son kwanta,bazan iya
rabuwa dake ba kmr yadda ba za a iya raba
hanta da jini ba. Koba haka kika ce min jiya
ba? 2nda nake ban taba jin irn wadannan
kalamai ba sai jiya a bakinki. Kin iya
hausa,sannan da wuya ki fadi marar
amfani,shiyasa kike kara shiga raina. Na
yaba da yadda kike sona sbd allah haka iana
jindadin yadda kike kula dani a kowanne
hali nake ciki,kina kula ki turo min sakon
tausayawa da tausasa zuciya. Duk da har
yanzu y.husaini baice min komai ba akn
hukuncin daya yanke a kaina. Idan na
kirashi ina jinsa faram2 nasan babu
matsala.idan ma akwai matsala ina addu'a
allah ya kawar da ita ya tankado mana da
alkhairai. Af ta marairaice ido tayi mrmsh
tace, amin ya allah. Tana rufe bakinta sai
taji an daka mata duka a baya ance,shegiya
aisha umar zance kikeyi da yamman nan?
Tayi sauri ta waiwaya cike da takaici sai taga
ummi kawarta ce. Al'amarin ummi sai
addu'a sbd ta zama abar a tausaya mata,
kai kace sabuwar mahaukaciya ce sbd
rashin kwanciyar hnkl da talauci ko zanin
daurawar kirki babu a jikinta,ita da goyon
bakikirin a cikin tsummokarai. Yadda dr s ya
kaikaice yana kallon ummi sama da kasa
shiyasa af jin kunya. Da kunya ta nuna
ummi tace kawarta ce,dk da ba zaman
karya suke yi ba ita dashi. Sai suru2 ummi
takeyi barkatai babu nutsuwa idan tayi
magana daya saita dakawa farida duka ta
dauko ashar ta kwararo mata,ta dauka
burge shuraim takeyi. Kokari take ta
tonawa farida asiri dn harta fara cewa badai
wannan mu2min an bane,yazo da kafarsa?
Suna shiga dakin af sai ummi tace,aisha
umar wanne malamin ne ya tsaya miki kika
sami wannan tsalelen,nima ki raka ni? Kada
dai kice min likitan nan ne da kikeso baya
sonki,wanda malam yayi miki aiki a kansa.
Kinsan aikin malamn nan fa yanaci,yanzu
gashi naki yaci yazo har kfr gidanku,gsky
mu2mn nan ya hadu nifa na zaci baya jin
hausa,na dauka farar fata ne,mu2min nan
kadara ne,ga kyau ga kudi harya fiki kyau
fa. Daman banda aikin malami yaya za a yi
mu2min nan ya kalle ki,kinga yadda yake
sonki kuwa naga sai wani kallonki yakeyi.
Nima dai ba laifi ina dan ganin cigaba a ckn
ayyukan dana rarrabwa malamai kashi-kashi
matsalar da ake samu ni inayi,budurwarsa
ma tanayi,uwarsu ma tanayi dn su raba mu.
Shiyasa bana ganin abubuwana suna tafiya
dai-dai. Dadin dadawa bani da kudi,kin san
aiki sai da siyen kayan sadaka,duk kayan
dakina sun kare,yanzu ko kmen zanyi ma
banida ko katifa dk na siyar. Kinga yanzu
ma daga wajen wani nake a lungun sharifai
makociyarmu ta hadani dashi,shima dubu 3
yace nakai za a yi aiki,sannan a yanka
kaza,shiyasa naji dadin dubu biyun nan daya
bani. Af tayi shiru dn takaici ko iya kallon
fskrta batayi na,tacigaba da kirga himilin
kudinta data iske a cikin ambulan din daya
bata. Sababbin 'yan dubu dubu ne har guda
ashirin,dubu ashirin ya bata hade da wani
dan karamin kati (greeting card) mai dauke
da kalaman soyayya dadada
2nda Allah ya halicce taba a taba yi mata
kyautar kudi mai dimbin yawa ba irin
wannan,dadin dadawa kyautar daga wajen
masoyinta ne. Ta gama karanata katin, saita
rungume shi a kirjinta, tace Allah srk
likitana. Kai Allah kaine abun godiya ngd
maka. Ummi tazo ta nanikewa af,tace,cafdi
dk wannan himilin kudin,ke ya bawa?
Daman ance ana yin asirin bada kudi sai
kaga mu2m yanayi maka kyauta ba a
hayyacinsa ba,irinsa nake so a yiwa yasar.
Dn Allah farida ki raka ni wajen
malaminki,kinga tsakaninmu dake babu
boye-boye. Takaicin abn data ke fada da
warin dattin bakinta,dana 'yarta ne suka
addabi af,taji kmr zata yi amai,tmkr
xuciyarta zata hautsuno ya fito waje. Ta
daga ido tana kallon ummi dn takaici ta
kasa ce mata komai. Ta mike tsaye ta daga
labulen kofa dn iska ta shigo,ta kade kauri
da karnin da dakin ya kidime. Ta wuce taje
kwandon kayan wanke wanke ta dauko
kwano da kofi ta zubo mata abnci da ruwan
sha ta kawo mata. Taga alamar yunwa
sukeji daga ita har 'yarta. Tana kawo musu
suka hau ci hannu baka hannu kwarya tmkr
wadanda suka kai azumi a lkcn rani. Af ta
koma gefe taci gaba ga rangadawa
masoyinta sakon gdy a cikin wayarta,ta
tuttura masa. Ummi zata sake yi mata
maganr bokaye af ta dakatr da ita da
hannu. Tace ummi dn Allah kici abincinki
kiyi shiru,kada ki kware idan kin gama kya
yi mun tatsuniyar. Ummi ta maimaita,
tatsuniya kuma?
DUK KYAN TAKALMI 3* 6
Af tace,ai gara ma tatsuniya,yara suna
karuwa sbd dk tatsuniya gargadi ce,amma
wannan lbrn naki gara in saurari kidan
garaya da in cigaba da sauraronki.allah ya
shrye ki ummi. Ummi ta koma ta zauna tayi
kulas tana ci tana gyada kai tana fadi a
ranta,lallai dan adam, wulakanci aisha umar
zatayi min dk irin halaccin danayi mata na
rakata inda aka jawo mata hnklnsa yazo
yana sonta,har yake cusa mata kudi,shine
na zama abar kyara a wajenta? Da ummi da
'yarta suka gama con abinci aisha farida ta
kwashe kwanunkan ta dawo ta zauna, ta
dubi ummi wacce 2ni alamomin bacin rai
sun bayyana fskrta. Af tace, ummi yaya su
hjyrki? Ta tabe baki tace, suna na kalau.
Keda naki sake nemana ba 2n ranar da
muka rabu dake daga gidan malam. Ai kya
zo kice min wannan bukata ta samu kiyi
min godiya. Amma shiru babu ke babu
labari. Koda yake ba zaki zoba dn kin fara
samun daula,gashi harda waya a hannu kina
daddannawa ai dole ki guje ni.af tayi
mrmshn krfn hali tace, naje nemanki mana
na tarar ba kya gidanki,facalarki tace an
sake ki. Har kinyi rshn m2mci kala2 kince
asiri sukayi miki ke ma saikin ga bayansu.
Haba ummi me yake damunki ne,kina abu
kmr baki taba shiga aji ba?
Ummi ta fusata tace, dole mana kice
haka,ai ke aiki yaci ni da baici ba sai in
zauna in zura ido? Kina ganin har yassar
yayi aurensa yaki ya mayar dani ko ganina
baya son yi. Af tace, yayi min dai-dai gsky
ba dn kin tako kinzo gidanmu ba har aba
bana son ganinki,kuma koda kuskure bazan
kara taka gidanku ba. Sbd kin kusa halaka
ni,kin tozarta ni duniya da lahira. Ke ba
kawar kirki bace ummi,dk mai yawo dake
ma sai ya halaka. Ummi ta fusata tace, to
naji kuma dk wulakancin da kika yimin nina
tako nazo gidanku, dk ranar da kika ganni a
gidanku