Showing 39001 words to 42000 words out of 99740 words

Chapter 14 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf

ESHAT   

23 Mar 2025

5442

sanyaye.tana qirgawa a yayin da
idanuwan masu leqe suka fi nata firfitowa
masu kama baki sunayi haka masu susar
tsohuwar kwarkwata suka fara yi ba tare da
sun san ma abun da suke yi sunyi matuqar
mamakisun razana haka sun ji kunya uwani
da yan tayinta suka kidaya kudi naira 17k ta
cika cif-cif.
Uwani bata iya dago da ido ta dube ni ta
iya ce min komai ba sai nice tambaye ta
nace sun cika ko da saura kudin da farida ta
ranta?ta gyada kai tace sun cika haka suke
nace to ki kaiwa haj rabi kice tayi haquri ba
za'a sake ba yanzu ma qaddara ce Allah ya
aikowa Aisha tayi jihadi ne don ta ceto ran
qawarta data qoqarin mutuwa akan gadon
asibiti zata haihu saboda bata da jini kuma
ba zata iya haihuwa da kanta ba sai tiyata
shine tazo ranci kudin ta kai kafin mijin ya
aiko daga lagos anan aka sami matsala da
bai aiko da wuri har ta kai aka kai ta wajen
yan sanda aka daure.Allah yana bayan mai
gaskia. Allah yana taimakon wanda ya
nemi. Taimakonsa Allah yana duban zuciyar
na gari da mugu kuma yayi hukunci a kansu
tun daga nan dunia da qawar Aisha mai
jego taji labarin halin da Aisha ta shiga a
dalilinta tuni ta taso daga kan gadon asibiti
taje ta fito da farida ta kawo ta gida ta hado
kudin nan da aka ranta Allah ya dubi zuciyar
Aisha yaga kyakyawar niyyarta ya taimaketa
ya fitar da ita daga tozarci da abin kunya.
A gida aisha farida ta kwana, ta tashi da

safen nan ta tafi makaranta taci gaba da
karatunta. Yanzun abinda ya rage shine
idan ta dawo da yamma kuje wajen 'yan
sanda ku tabbatar musu da ta biya kun
janye kara, sai a soke shikenan a zauna
lafiya. Uwani mun gode da taimakon da
kikayi mana, akasi aka samu har ya zama
rigima. Kiyi hakuri, itama ba haka taso ba.
Su dukka suka yi shiru kamar wadanda ruwa
ya cinye su. Nayi murmushi na dube su
daya bayan daya nace ku gafarce ni, daman
ina da matsala daku bansani ba, kuma babu
wacce ta tare ni ta sanar dani? Ai da
tuntuni kun sanar dani halin da ake ciki don
ban san inayi muku laifi ba ma a tsawon
zamana daku, kusan shekaru goma. A
bangarena bani da matsala daku ko kadan,
ina taka tsantsan kada in batawa wani, ina
iyakacin kokari inga na fitar da hakkin
makotaka da Allah Ya wajabta a kaina shine
inyi muku sallama, in gaishe ku duk sanda
muka hadu a tsakar gida, in duba ki idan
baku da lafiya, inyi muku jaje ko gaisuwa
idan kun rasa wani dan uwa ko wani abu. In
taya ku murna idan aure ko haihuwa sun
same ku. Menene yayi saura kuma baya ga
duk wadannan? Ku gafarce, laifi daya ne da
nake muku, kuma ba zan daina ba shine ina
kula da mijina yadda ya kamata, ku kuma
ba kwa so. Nayi alkwari bazan daina tsafta
ba, haka ba zan daina ciwa 'ya'yana ado ba
da gwanjo, haka ba zan daina wankewa
mijina bandaki ba duk sanda zai shiga, haka
ba zan daina sanya curry ba ina dafa masa
dadadan abinci, koda kuwa ace mijinmu
daya ne daku, balle babu hadina daku.
DUK KYAN TAKALMI 2* 2
A gida aisha farida ta kwana, ta tashi da
safen nan ta tafi makaranta taci gaba da
karatunta. Yanzun abinda ya rage shine
idan ta dawo da yamma kuje wajen 'yan
sanda ku tabbatar musu da ta biya kun
janye kara, sai a soke shikenan a zauna

lafiya. Uwani mun gode da taimakon da
kikayi mana, akasi aka samu har ya zama
rigima. Kiyi hakuri, itama ba haka taso ba.
Su dukka suka yi shiru kamar wadanda ruwa
ya cinye su. Nayi murmushi na dube su
daya bayan daya nace ku gafarce ni, daman
ina da matsala daku bansani ba, kuma babu
wacce ta tare ni ta sanar dani? Ai da
tuntuni kun sanar dani halin da ake ciki don
ban san inayi muku laifi ba ma a tsawon
zamana daku, kusan shekaru goma. A
bangarena bani da matsala daku ko kadan,
ina taka tsantsan kada in batawa wani, ina
iyakacin kokari inga na fitar da hakkin
makotaka da Allah Ya wajabta a kaina shine
inyi muku sallama, in gaishe ku duk sanda
muka hadu a tsakar gida, in duba ki idan
baku da lafiya, inyi muku jaje ko gaisuwa
idan kun rasa wani dan uwa ko wani abu. In
taya ku murna idan aure ko haihuwa sun
same ku. Menene yayi saura kuma baya ga
duk wadannan? Ku gafarce, laifi daya ne da
nake muku, kuma ba zan daina ba shine ina
kula da mijina yadda ya kamata, ku kuma
ba kwa so. Nayi alkwari bazan daina tsafta
ba, haka ba zan daina ciwa 'ya'yana ado ba
da gwanjo, haka ba zan daina wankewa
mijina bandaki ba duk sanda zai shiga, haka
ba zan daina sanya curry ba ina dafa masa
dadadan abinci, koda kuwa ace mijinmu
daya ne daku, balle babu hadina daku.
Menene laifin aisha farida kuma a cikin
gidan na, ko kuma ince a cikin unguwar
nan? Hana idanuwanta baccin da take yi ne
take zuwa karbar haihuwarku komai dare?
Ko kuwa allurar da takeyi muku idan likita
ya rubuto muka ta hutar daku zuwa
chemist? Kitson da take yi muku kyauta ko
kuwa ko yawa 'ya'yanki karatun da takeyi,
duk sati ba tare da ko sisinku ba? Taya ku
girki da takeyi, ko kuma rainon 'ya'yanku
da take yi muku koda yaushe shi ya zama
laifi? Gaishe ku da takeyi koda yaushe, ko

hirar da take zama kunayi da ita shine
laifinta? Allah sarki rayuwa, ai kuwa Aisha
farida mutum ce babu wacce bata morarta
a cikin gidan na, koma nace a layin nan
gaba daya. Ummulkhairi na dade da sanin
cewar ke kike wanke kafa kike zuwa ki sami
mahaifiyar musbahi ki caccaka mata karya
da gaskiya don ta tsani aisha farida a
matsayin surukarta, burinki ya cika har sai
da kika haddasa wannan gaba a zuciyar
uwar musbahu, ta tsinewa aurensa da aisha
farida, tace idan dai tana raye ba zai aure ta
ba. Na sani aisha farida ta sani, musbahu ne
ya fada mata shima ya sani. Sai
ummulkhairi ta mike tsaye ta hau
bambamin fada mai tafe da borin kunya
tsagwaronsa. Tana jan Allah Ya isa ba zata
yafe sharrin da nayi mata ba. Na mike
tsaye nima na nuna mata ruwa ba sa'an
kwando bane, haka shiru shiru ba tsoro
bane gudun magana ne. Kalmar da na fada
mata ta karshe daga ita na gaggauta barin
wajen itace kinji dadi, kin raba auren
musbahu da farida, amma baki isa ki hana
Allah Ya bata wani mijin ba, daga wani
bangaren, bangaren da baki sani ba. Kuma
wanda baki da matsayin da zaki taka kiyi
gulma. Ummulkhairi ke da sauran makiya,
ku bude idonku sosai zaku sha mamaki,
zaku sha kallo, zaku ga irin mijin da aisha
farida zata aura idan har muna raye.
Insha'allah sai Aisha farida tayi auren da
babu wacce ta taba yin irinsa a gaba daya
unguwar nan bana a layin nan ba ko gidan
nan Allah yana tare da mu kuma da shi
muka dogara yan gulma suka hau gasgata
maganata suka hau nadama suna fadar
alkhairin Aisha farida data taba yimusu a
rayuwa nan da nan na bar wajen na kyale
su suna ta kame- kame kanka ce kwabo
dandali ya rore ya qare daya bayan daya
suna ta sulalewa suna guduwa saboda
kunya Aisha farida ta riqe baki don mamaki

gami da farin ciki abunda abida tayi.tayi
mata dai-dai ta burgeta tayi murmushi tace
anty abida dama ke iya fada?amma
bantaba ganin kinyi ba?abida tace habah
meye abun burgewa a iya fada kuma?ni
zubar da mutunci ne fada dole ce tasani
sun kaini qarshe ina ruwansu da tsakanina
da mijina idan zancen kudi ne zasu suyi duk
zagin da zasuyi suyi akan haqqinsu ne mu
muka taba su haqqinsu ne muka jawo wa
kanmu amma ace tsaftar dana keyi da girki
dana keyi da tsaftace 'yayana duk laifi ne
ina ruwansu?aida haushi mu ba mijinmu
daya ba balle suce nazo zan kwace musu
miji banzaye,qazamai maimakon suyi koyi
dani saina na zama abar zagi,abar kyama
daqa-daqa dasu sai suyi kwana 3 ba wanka
suna yawo da dauri qirji a tsakar gida ba
kitso bare yankan qumba,bare ayi zancen
su qunshi da turaren wuta ko turaren jiki
basu gyara jikinsu ba ina zasu gyara yara
bare wani miji?
Insha'allah sai Aisha farida tayi auren da
babu wacce ta taba yin irinsa a gaba daya
unguwar nan bana a layin nan ba ko gidan
nan Allah yana tare da mu kuma da shi
muka dogara yan gulma suka hau gasgata
maganata suka hau nadama suna fadar
alkhairin Aisha farida data taba yimusu a
rayuwa nan da nan na bar wajen na kyale
su suna ta kame- kame kanka ce kwabo
dandali ya rore ya qare daya bayan daya
suna ta sulalewa suna guduwa saboda
kunya Aisha farida ta riqe baki don mamaki
gami da farin ciki abunda abida tayi.tayi
mata dai-dai ta burgeta tayi murmushi tace
anty abida dama ke iya fada?amma
bantaba ganin kinyi ba?abida tace habah
meye abun burgewa a iya fada kuma?ni
zubar da mutunci ne fada dole ce tasani
sun kaini qarshe ina ruwansu da tsakanina
da mijina idan zancen kudi ne zasu suyi duk
zagin da zasuyi suyi akan haqqinsu ne mu

muka taba su haqqinsu ne muka jawo wa
kanmu amma ace tsaftar dana keyi da girki
dana keyi da tsaftace 'yayana duk laifi ne
ina ruwansu?aida haushi mu ba mijinmu
daya ba balle suce nazo zan kwace musu
miji banzaye,qazamai maimakon suyi koyi
dani saina na zama abar zagi,abar kyama
daqa-daqa dasu sai suyi kwana 3 ba wanka
suna yawo da dauri qirji a tsakar gida ba
kitso bare yankan qumba,bare ayi zancen
su qunshi da turaren wuta ko turaren jiki
basu gyara jikinsu ba ina zasu gyara yara
bare wani miji?
Aisha farida kwarai kuwa hakane ai ana
zuba qazanta a gidan nan dukansu qazamai
ne duk dakin daka nufa warin datti ne abida
tace kece ma mai iya shiga dakunansu har
ki zauna ki cakumi gashinsu ki kitse ni ina
zan iya jure wari?ai shi yasa. Nakeso kici
gaba da dagewa har sai kin sami dr shuraim
shi kadai yafi dacewa da rayuwarki wani juyi
Aisha farida tayi tashin farko ta kifa ta
kwanta ta juya baya bata sake cewa komai
ba saboda bata da abun fada taki jinin a
ambaci sunan dr shuraim a halin yanzu
balle ayi hirarsa.Abida tayi dariya tace au
kiran sunan shuraim ma ba kya so shi ne
kika juya mun baya? masoyin naki ne ya
zama haka yanzu a wajenki?haba farida
kada kiyi fushi kada ki sare da wuri mutane
suna rasa ransu wajen neman abinda
zuciyarsu keso ke yanzu wacce wuya kika ji
har da zaki zame?keda shuraim kuna nan
daram ba gudu ba ja baya ina nan akan
bakana duk kyan takalmi qafa ce zata
tattaka shi''Aisha farida ta jawo filo ta dora
kanta ta toshe kunnenta sabida bata
buqatar ci gaba da sauraron abun da abida
ke cewa tamkar tana zuraro mata tsohon
gyambon data dade da warkewa bata fatan
gyambon nan ya dawo mata danye tafi son
idan ya warke ya warke kenan har abada
bata buqatar dayen ciwo ko maqiyinta bata

masa fatan ya shiga halin data shiga.
Abida ta fice tana daria ciki-ciki fitar abida
ke wuya sai ta tashi zaune ta jawo jakar
makaranta ta zubo littafanta da manyan
text books dinda ta aro daga wajen khadija
isma'I'll don ta karanta abubuwan da akayi
bata nan.tabbas an wuceta. Da yawa sai
tayi da gaske zata kamo su tana karatu
zuciyarta na zogi idan ta tuno dalilin daya ja
mata wannan matsalar sai taji haushin
kanta da kanta ta qudiri niyyar ba zata sake
bawa zuciyarta wannan dama ba balle takai
ta ta baro ta.bata fito ba sai data ji ana
kiran sallar magrib fitowarta keda wuya tayi
kicibis da yayanta ya dawo daga aiki ya
kuwa wurgo mata harara sai ta zube a qasa
ta kwashi gaisuwa ko amsa mata baiyi ba ya
shige dakinsa Aisha farida ta sake
gasgatawa har yanzu da sauran rina a kaba
maganar bata wuce ba kenan da saura?ta
miqe a sanyaye taje tayi alwala ta dawo
daki tayi sallah kafin ta idar taji motsin
shigowar abida daga dukkan alamu wajenta
tazo don har yanzu tana tsaye a kanta sai
da ta idar da wuri taji abinda ke tafe da ita
tana idarwa ta juyo ta dubi abida tace
aunty lafia? Abida tace ki zo inji yayanki
amma kada ma ki damu ba wani abu bane
kinsan dai duk abubuwan dana shirya to
duk abunda ya tambayeki ki haka zaki tsara
masa yanzu ya du da mijin uwani a qofar
gida suka tattauna suka wa juna haquri
shine zasu je wajen yan sandan su sunar
musu cewar an sulhunta an janye qara ba
sai kun je ba.Aisha farida ta miqe da sauri
dafe da qirji tace anti abida me zance masa
game da cikon 5k dinsa da kike ce zasu ciko
min?Abida tace a hakan zaki barshi zasu
ciko din,idan basu ciko ba ai laifinki bane
kuma ba zai kai ki qara ba dai shima sai ya
dauki asara daba ki samo 12k bama ai dole
ya nemo yayi belinki ba tunda ba zai bari a
daure ki ba wata da watanni.nasan dai zaki

sha fada ne da zagi kawai zagi kuwa baya
qari idan da sabo ai kin saba''
Abida ta wuce gaba Aisha na biye da ita a
baya ta sunne kai a cikin hijabi hannayenta
kuwa dukka 2 na dafe da qirjinta sai
karanto addu'io take iri-iri ba adadi tana
mai neman agaji daga wajen rabbil
samawati duk abun da zai zo yazo mata da
sauqi.Allah mai amsar addu'ar bawansa sai
ya sanyaya zucia yaya husaini maimakon
yayi mata fada data bayyana a gabansa sai
ya shiga yi mata nasiha yaji tamkar shima
ya fashe da kuka lokacin daya ga hawaye a
idon qanwarsa sai yaji tausayinta ya shiga
nasiha mai hade da rarrashi yace farida
haha farida kefa mai hankali ce mai sanin
ya kamata ga natsuwa nayi mamakin yadda
kike jefa rayuwarki cikinmatsla don kawai ki
fitar da wasu daga matsala ba'a hana
taimako ba amma kina so kina so kice min
bata da dangi ne ko dangin mijin sai ke kika
fiso sonta dasu?suna raye zasu bari ta mutu
ne basu samo kudin da za'ayi mata tiyata
ba sai ke?farida kinsan halin da muke
ciki,ta kanmu muke yi,bamu da wani
mataimaki sai Allah kullun hade-hade da
kame- kame mukeyi sannan muci abinci sai
naji tamkar na bar garin nan saina tuna
talauci dana baro a shagamu har gara nan
ma.ki riqe maraicinki ki riqe talaucinki ki
riqe matuncinki ki riqe karatunki ki lallaba
ki gama ki fara aiki ko zamu sami sa'ida
babu ke babu sake cin bashin wani babu ke
babu katsalandan akan matsalar wani ki
tashi ki tafi Allah ya kiyaye gaba Aisha
farida ta rushe da kuka tace nagode
insha'allah zan kiyaye ta fice ta nufi dakinta
ta shige ta takure tayi ta rusa kuka tana nai
tuno iyayenta da suka rigamu gidan gaskia
tabbas husaini ya fada mata gaskia dole ta
nutsu tasan me ye a gabanta kuma ita wace
ce a rayuwa?hawaye ya surnano daga
idanuwan husaini yasa hannu ya goge abida

ta matso kusa dashi ta fada cikin
sassanyiyar murya tace yaya kaima kukan
kake yi?kada ka damu fa kada ka saka
damuwa a ranka ciwo ya same ta tsautsayi
ne qaddara ce komai yazo qarshe ba za'a
sake ba insha'allah.
DUK KYAN TAKALMI 2* 3
Husaini ya girgiza kai yace ina son Aisha
saboda babanmu yana sonta tayi kama
dashi don haka idan na dube ta ina yawan
tunawa dashi hawayenta ne yake tayar min
da hankali.farida abar tausayi ce marainiya
babu uwa ba uba nida nake riqe ta talaka
ne ina matuqar tausayinta idan na ganta a
cikin qawayenta yan gata masu mota
baiwar Allah bata damuwa a haka take
daurewa tayi karatu sai naji tamkar dama
ina da yadda zanyi farida mata sami duk
abubuwan da yan mata suke buqata kamar
kayan kwalliya da dinkuna to babu
misbahun ma da yake sonta yake
taimakonta shima an raba su fatana Allah
ya fito mata da miji na gari inda zata huta
ko bayan raina ta taimaki kanta kota riqe
min 'ya'yana ba''Abida tayi shiru tana
tunani a ranta tace babu mijin daya dacewa
da ita irin dr shuraim insh'allah farida saita
sami shuraim ko don na hucewa mijina
takaici a ransa ko don in cika masa burinsa
na ganin farida ta sami gidan hutu nayi
alqawalin zan yaqi zuciyar shuraim da
addu'a da kuma kyautatawa har sai yaso
farida yaya husaini ya katse tunanin da
abida keyi yayi cimak ya miqe tsaye yace
zanje waje malam yusha'u na jirana mijin
uwani zamu je wajen yan sanda nan don a
janye casa dinsu Aisha.Abida tayi masa
fatan ya dawo dashi lafia ya fice da sauri.da
Aisha ta idar da sallar isha'I ko abinci bata
ci ba wajen datayi sallak kan tambarmarta a
wajen ta kudindine ta kwanta babu abin da
take yi sai sheshekar kuka da ajiyar zucia
har barci ya dauke ta.

Babu irin tashin da abida bata yimata don
taci abinci taqi tashi tace ta qoshi a haka ta
kwana saboda gajia da barcin data keji basu
bari taji yunwaa ba bata farka ba sai da
asuba kiran assalayu a kunneta ta miqe a
nutse tana mai addu'io taje tayi alwala tayi
sallah sannan ta shiga cuku-cukun yin
wanka da saka kayan makaranta so take
gari ya waye ta fice saboda gidan ya zama
mata tamkar kurkuku haka tunaninta da
hankalinta kakaf ya koma kan karatunta
bata da wani buri illa taga ta gyara inda ta
kuskuren kuma ta kamo yan ajinsu inda
suka wuceta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login