Showing 78001 words to 81000 words out of 99740 words
Chapter 27 - DUK KYAN TAKALMI COMPLETE BOOK 1 BY ESHAT.pdf
kiiyi min dk wulakancin da kika ga
dama. Ta zabura zata mike af ta riketa ta
mayar da ita ta zaunar. Tace, yo hkr gsky
nakeso na fada miki,ita kuwa gsky daci
gareta. Ummi,fada miki ne ban yi ba amma
jana gidan boka da kikaui kika zuga ni na
ranto kudi,kin jawo min bakar masifa a
rayuwata. Aikinsa bai min amfanin komai
ba,har kulle ni akayi a ofoshin 'yansanda
sbd wannan kudi,shi kuwa wanda akayi min
asirin dn yasoni saima ya sake tsanata.
Ummi bazan boye miki ba saida nayi kuka
da hawayena,nayi allah wadai da halayenki.
Ni mai yafiya ce, na yafe miki,amma fa kin
cuceni. Ummi ta harari af tace me kike so
kice min bayan nan kin samu,gashi nan yazo
wajenki? Af ta soko mata tata harara tace
har yanzu baki saduda bako, ba zaki daina
gasgata karairayin 'yan danfara bako? To
bari na fada miki wannan mu2min da kika
kaini wajensa macuci ne,kema kinsan da
haka,tawada ce ya zuba a ruwa ya bamu sai
laya aka rubuta alifun,ba'un da sauransu
tsabar ya mayar damu jahilai. Ke bari ma
na baki labarin dk abnda ya faru bayan
rabuwata dake. Kinci sa'a anti abida bata
nan, da yau saita wanke ki,sbd taki jinin
taga mace mai bin bokaye. Habba ummi
yanzu mai bin boka ya kara miki,kin kadar
da dk abnda kika mallaka a duniya kina
yawo a cikin tsumma keda 'yarki ko wanka
babu. Mai yassar zaiyi dake a haka kmr
tababbiya? Ai har abada ba zaki ga dai'dai
ba idan dai baki daina bin bokaye ba. Ummi
da nayi istigifari na mayr da gaba daya
lamurana wajen Allah a saukake. Ya kawo
min dr s cikin kwanciyar hnkl. Ina ma zaki
bi hanyar dana bi dakin samu yassar cikin
sauki ba tareda kin kashe ko sisi ba. Da
rayuwarki ta gyaru duniya da lahira,hnkli ya
kwanta,kin fita daga talauci dacin bashi.
Ummi tayi sororo da alama jikinta yayi
sanyi,ta fada cike da sanyin jiki. Aisha umar
fada min yadda kika yi. Af ta gyara zama ta
bawa ummi labarin dk abnda ya faru da
ita,2n daga ranar da suka rabu da ita,har
izuwa rana irin tayau. Ummi ta buga tagumi
tana sauraron af daga dukkan alamu tana
gasgata nasihohinta. Da af takai aya,sai
ummi tayi ajyr zuciya. Tace,aisha umar kinyi
gsky,to yanzu meye shawararki? Ta ina zan
fara? Af tayi dry tace, ta inda na fara zaki
fara,kum kema ki riki wadannan matakai
biyar da abida tabani, ki riki kissar malamai
nan da yasa matar na ta debo masa nonon
bauna. Ki rabu da bin 'yan tsibbu ba sai
wani ya fada miki ba,kema kin san babu
riba. Ummi ta sharce hawaye tace, gsky ne,
nima ina tsoron haduwata da
ubangiji,sannan ga sunanan ya baci a garin
nan dk wanda ya danni,yasan ina bin
bokaye,har da 'yan ina da kare nake bi.
Yanzu yaya zanyi aisha umar? Saita rushe
da kuka. Af tace, laifin da kikayi tsakaninki
da ubangiji zai yafe miki,idan kika tuba.
Laifin da kikayi wa wani ne Allah bazai yafe
miki ba saikin je kin nemi gafarar wadanda
kika yiwa laifin. Wannan shine mataki na
farko da zaki fara takawa. Kiyi ta istgifari da
lahaula kiyi ta addu'a akan Allah ya juyo
miki da hnklin yassar ya dawo gareki. Abu
na biyu ki zamo mai tsananin hkr, karki ga
idan kinga an sami jinkiri,bai kuyo gareki
bada wuri. Na 3 ki kama mu2ncinki,kija
ajinki kada ki sake binsa ko waninsa kina
rokonsa ya mayr dake. Idan kika rike guda
ukun nan zaki ga yadda Allah zai yi dake.
Ummi ta zauna shiru tana 2nani,ta kasa
cewa komai,canta dago ta dubi af. Tace,
yassar fa ya tsaneni, ya tsani ya ganni ko a
hanya. Sai naje nayi masa hayaniya nema
yake aiko min da dubu 1 ko 2 a wata na
abincin 'yarsa. Af tace,to saime? Bake kika
jawa kanki ba? Ai halin mu2m ke sawa a
tsane shi,ki gyara halinki ki gani idan baiso
kiba. Ki dinga wanka kina tsaftace jikinki
dana 'yarki,ki rage magana barkatai da
yawo a gari,ki zauna a gidanku ki riki sallah
da zumi da lazimi,kina ta addu'a kiga yadda
Allah zai sauya ki. Ummi tace, insha Allahu
zanyi duk yadda kik ce min, yanzu ma daga
nan gidan sirikata zanje na nemi gafararta
da facalata dashi kansa yasar din,nace
kuskure nayi dana biyewa zancen malamai.
Sai in koma gida in zauna in daina yawo in
dinga sana'a ina biya dimbin bashin dake
kaina. Aisha umar ngd,madalla sai kin ganni
kuma. Ta tashi ta dauko 'yarta ta goya a
baya,jikinta sanyi kalau. Af ta bude jakar
kayanta ta tsinto mata atamfofi kala biyu
tsofaffi ta bata,ta sake zaro nairi dubu 1
daga cikin kudin da dr s yabata ta hada
mata. Sai gdy ummi keyi tana murna. Ta
rakata har bakin titi ta hau acaba ta tafi. Af
ta dawo gida cike da tausayin kawarta mayi
mata addu'ar Allah ya shirye ta, Allah ya sa
abunda take fada a bakinta ya shiga har
cikin zuciyarta ASUBA TAGARI UMMIN
YASIR
BABI NA GOMA SHA SHIDA Yaya husainai
ne yaketa shige da fice tsakanin dakinsa
zuwa kfr dakin 2n kafin gari ya karasa
wayewa. Da duku-duku af ta tashi dn tayi
sallah ta kuma kai yara fitsari kasancewar
lahadi ce babu mkrnta,in yaso bayan sunyi
sallah saisu koma suci gaba da bacci. Tayi
mamaki da ganin y.h a tsakar gida yana
tsaye cak kmr mai 2nani. Mamakinta ya
sake karuwa alkcn data fito daga bandaki
har tayi alwalla bai koma daki ba,dai kai
kawo yake tayi tsakanin dakinsa zuwa
zaure. Ya shiga ya fita. Bayan tayi sallah
yaran dk sunyi sallah,saita sake kwantar
dasu sannan tayi wuf! Ta fito dn taga y.h
yana nan? Ta iske shi a tsaye daf da kfr
dakinta ya sakale hannayensa a bayansa ya
sunkuyar dakai kasa kmr mai 2nani. Saita
dafe kirji dn bugawar da zuciyarta keyi.
Yaya lfy? Ta tmbyeshi. Ya dago jajayen
idanuwansa ya dubeta da kyar ya iya bude
bakinsa yace,lfy? Ta tsaya a jkin kofa tana
kallonsa babu abnda zuciyarta bata aiyana
mata akan abida ba. Tasan tabbas wannan
damuwar tasa tana da alaka da abida. Yace,
aisha yaushe ne zaa yiwa yara hu2n
mkrnta? Muryarta na rawa tace, gobe litinin
zasu fara jarabawa, ranar juma'ar kuma za a
yi musu hutu. Lafiya? Sai yayi shiru, can ya
dago sai taga idanuwansa sharkab da
hawaye, yace, ina ganin su hkra da
jarabawar ki hada muku kayanku mu tafi
shagamu yanzu. Ta sulale ta durkusa ta
dora hannu aka ta fasa kuka mai tsananin
sauti da gigitar da mai sauraro. Tace,
Innalillahi wa inna ilaihi rajiun! Wayyo Allah
anti abida,wayyo antina, Allah ya
jikanki,Allah yayi miki gafara. Sai y.h ya
fisgota ya toshe mata baki ya grgza ta fadi
yace, rufe min baki,waye yace miki abida ta
mu2? Kan kace kwabo yaran abida suma
sun fito daga daki da gudu,suna kuka.
Mutanen gidan yaransu da manya,maza da
mata sun firfito a gigice suna tmbyrsu ko
lfy? Af dai bata ji bata gani,ba kuma ta gane
dk abubuwan da jama'ar da suka taru
akanta suke fada ba. Kuka take,faduwa
take ana riketa bata kakkautawa. Abida
bata mutu ba. Kalmar da y.husaini keta
ambato,amma fa shima din kuka yake yi
haikan. Mutanen gida maza da mata sai
suma suka dinga hawaye dn tausayawa su
AF. Af ki hada kayanku a babbar jaka da dk
wani abu mai amfani ki shiga dakina ki
harhada kayana dana abida kakaf gara mu
kaura shagamu meyi jinyarta 2nda har
yanzu bata warke ba,ni bance miki ta mutu
na. Bari naje na nemo mana tasi wacce zata
kaimu tasha. Ba dn ma tfyr ba ta shiri bace,
aida motar ofis zan aro in zuba mai mu da
kayan mu kakaf mu tafi, to ba shiri. Af ta
tsh tsaye daga kasan datake burgima jikinta
yayi bududud yayin da fskrta ta hadu ta
damule,bayan hawaye da yayi face-
face,idanuwan da fskr dk sun kumbura
luhu-luhu. Ta kade jikinta ta dubi yayanta
tace,yaya ina da magana dakai. Saita suce
daki, ya biyo ta a baya. Ta jawo jkrta ta
binciki,sai ta damko himilin kudi ta mika
masa har naira dubu goma sha takwas. Ya
karba cike da mamaki ya tmby,af waye ya
baki wadannan makudan kudi? Ta matse
hawaye tace, dr s ne ya bani dubu ashirin
wancan satin da yazo. Ya kalmashe ya zura
a aljihu yace,ki nutsu ki hada muku kayanku
a tsanake ni bance miki abida ta mu2 ba.
Ta fashe da kuka tace,haba yaya nima fa
musulma ce,kuma mai hnkli nasan
tawakkali. A gabana babana ya mutu ba a
dade ba uwata ta mutu,me yasa zaka boye
min mu2war abida? Yace,ni dai bance miki
ta mu2 ba. Ya ficce yabarta a drksh ta jawo
wayarta da sauri ta kira lmbr goggo
mahaifiyar abida taji a kashe. Ta kira
lambobin mutanen gdnsu har su 3 babu
mutum 1 data samu,dk sun kashe waya.
Wannan ya tabbatar mat abida ta rasu.
Saita kira kanwarta munawwara a lagos taji
muryar knwrta rangadau cikin fara'a take
magana. Af cikin kuka tace,baku da labarn
mu2war abida ne? Sai taji munauwara ta
kwalla ihu ta wurgar da wayar tana salati.
Aisha farisa ta tabbata lbrn mu2war bai isa
garesu ba. Ta kira yaya yahya sai tci sa'a
bugu daya ta shiga,nan da nan ya amsa. Ta
rushe da kuka,tace, yaya ka fada min
gsky,abida ta rasu ko. Hello,hello kawai
yake cewa,kasancewar yana cikin hayaniya
baya jinta. Yace aisha zan kiraki bana jinki.
Saiya katse wayar. Ta mimmike kafa ta ske
bude wani sabon shafin kuka. Kukan dako a
mu2wa iyayenta batayi irinsa ba. Bata
manta da ambaton innalillahi wainna ilaihi
rajiun ba. Babu anda tafi 2nawa sai irin
gudunmuwar da abida ta bata wajen yakin
neman soyayyar dr s. Allahu akbar,allah mai
yadda yaso,ga dr shuraim ya samu ita kuma
ta tafi. Tace a ranta, tabbas rabuwa da dr s
shine kwanciyar hankalina 2nsa babu abida,
muddin na kasance da shuraim babban
fami zai dinga yimin ina tunowa da ita.
matan gida suka biyo ta daki suka zagayeta
suna bata naki, su ma sun shiga rudani
kasancewar husaini yace bata mutu, to idan
bata mutu ba mai yasa xai tashi tfy a yau,
gashi kuma yana rusa kuka shima uwani ta
matse hawaye, tace AF tashi ki hada muku
kayan kafin yayanki ya dawo don ya tafi ya
samo mota" AF ta girgixa kai , tace"baxan
iya ba ku kyaleni kawai" taci gaba da rusa
kuka baji ba gani. nan matan gida suka
shiga hada musu kayayyakinsu suna durawa
a jakunkuna da buhuhunan kama daga
kayan sawarsu takalmansu da kwanukansu.
faruk ne yake ta jawo akwatinan mamansu
da babansu daga cikin dakinsu yana fitowa
dashi tsakar gida,matan suna ta harhadawa.
himilin kaya dauri dauri aka kawo zaure aka
himila, katifu ne kawai basu dauka ba
amma babu abinda ba'a harhada ba. ha
yanzu AF na zaune a daki ta hada kai da
gwuiwa, kukan da takeyi yaki ya kafe sai ita
tasan abinda takeji a cikin zuciyarta,
kuna ,suya da tafarfasa duk sun tabbata a
kirjinta. ta fada a baiyane" Abida.....abida
mutunce. muyane nagari basu cika dadewa
a duniya ba. sai yanzu na cika marainiya
nayi rashin yar uwata garkuwar jikina. dama
in mutu a yau in huta da takaici rayuwa.
bani da sauran farin ciki a rayuwata
kuma....
U.khairi ta rushe da kuka ta durkusa a
gaban af tace,ki yafe min, abida ta yafe
mana abubuwan da muka dinga yi muku a
zamanmu daku a gidan nan,hakika mun
zalunce ku,kullum muna cikin gulmarku,yi
muku kazafi,makirci kala2 ku baku sani ba.
Allah ya jikan abida mace mai hkr,sai a
zageta a gabnta ta juyo t kallemu tayi
mrmshi ta wuce ba zata rama ba,kuma
bazata tabayin gaba damu ba. Ban san
abida idan ta tafi ba zata dawo ba, dana
nemi gfrarta a ranar da za tafi da ita.
Farida, ki yafe min koke ma idan kin tafi kin
tafi ba zaki sake dawowa kano ba. Tabbas
nice nayita hada makirci a wajen mahaifiyar
musbahu dn kada ya aureki. Laure,uwani
yaya ku kayi shiru bayan daku mukeyi musu
komai. Suma sai suka gyara zama sukace
haka ne farida ki yafe mana, mun zalunce
ku, mun zalunci kanmu. Zazzafan hawaye
ne ya dinga tsattsafowa daga idanuwanta.
Ta tsura musu ido tana kallonsu kawaita
kasa furta kalma 1 sbd tsananin data ke
ciki. Kalamansu tmkr ruwan wuta suke fesa
mata,saita daga hannu ta dakatar dasu.
Tace,ya isa, dn Allah kubar fada min, dk
nasan abunda yake frauwa,kuma abida ta
fada min komai. Naji abnda kukace,kuma
na yafe muku,na tabbatar abida ma ta yafe
muku,dn bata taba kwana da wani a ranta
ba.
Su dukka suka cigaba da koke. Muryar yaya
hussaini suka jiyo a zaure dashi da maza
suna ta jidar kaya a zaure ana kaiwa mota
ana lufgawa. Har sai da aka kwashe kayan
tatas ya leko dakin yace aisha farida da yara
su fito su tafi. Sai da su uwani suka daga ta
tsaye wannan tana taro mata zaninta zai
fadi, wannan tana gyara mata hijabi.
Takalmi silifas sai da aka tura kafarta a ciki
don ta manta yadda yake sawa saboda
tsabar kidimewa. Wayarta ce kawai a
hannunta don ko kofofin dakunan sai da
yaya hussaini ya datso, kanta tsaye ta fice
ba tare da ta iya waiwayowa baya ba. Bata
iya amsa adduoin ta'aziya da fatan Allah Ya
kiyaye hanyar da jama'ar gida da makota
suke yi mata ba. Tafiya take tamkar kwai ya
fashe mata a ciki. Bata ma san inda take
jefa kafarta ba, 'ya'yan abida na nanike da
ita, idan ta kalle su sai taji wani gagarumin
tashin hankali ya sake taso mata.
"Faridah!!" Tattausar murya taji a gefenta
don haka ta waiga da sauri. Musbahu ta
gani idanuwansa sharkab da hawaye, itama
sai hawaye ya fara kwaranyo mata. Tayi
sauri ta sunkuyar da kanta kasa ta dinga
tafiya wurin mota. Yace Allah Ya jikan abida,
naji ance kun kwashe kayan ku kakaf kun
kaura shagamu. Yanzu shikenan ba zan sake
ganinki ba? Ki sani har abada ba zan daina
sonki ba, babu yadda zanyi ne. Sai ta sake
rushewa da kuka, shima haka yana biye da
ita har ta shige mota ita da 'ya'yanta. Yaya
hussaini ya shiga gaba shi da direba, su
kuma a gidan baya. Kaya kuwa suna can
baya irin motar nan ce mai kama da na 'yan
sanda bayanata kamar a kori kura.
Cincirindon mutanen unguwa ne suka firfito
yara da manya, maza da mata suna ta daga
musu hannu har suka ja motar suka tafi.
Sabon kuka ne ya sake sarkewa aisha
farida. Sun fita daga kano kenan sai dr
shuraim ya kirata, da farko tayi kamar ba
zata dauka ba, sai dai ta daure ta amsa.
Magana yake cikin shaukin soyayya. My
love kin tashi kalau? Jiya kuma muna
magana sai kikayi bacci ki ka barni ko? Ta
runtse ido dan tsananin tashin hankali yayin
da hawaye ya dinga tsartuwa daga
idanunta. Bata iya bashi wannan amsar ba.
Yayi murmushi yace banji kinyi magana ba
tun dazu, ko baki jina ne? Tayi magana cikin
sansanyiyar murya tace dr muna hanyar
shagamu. Abida ce ta mutu. Innalillahi wa
inna ilaihir rajiun dr shuraim ya sake
maimaitawa har sau uku. Yayin da kuka ya
barke mata. Dai dai lokacin kuma yaya
hussaini ya hasala ya juyo a fusace ya fizge
wayar, ya murtsike ya kashe ya rufe ta
bambamin fada. Waye yace miki mutuwa
tayi har kike yadawa a waya? Wai ke wace
irin yarinya ce mara jin magana? Cikin kuka
tace haba yaya me yasa kake boye min
mutuwar anti abida? Ya ja dogon tsaki ya
girgiza kai ya juya ya cigaba da kallon haya,
ya saka wayar ta ta a aljihunsa. Dr shuraim
yayi ta gwada kiran aisha farida ji wayar a
kashe , sai hankalinsa ya kara tashi matuka.
Yasan duk inda take yanzu bata cikin
hayyacinta, kuka kuwa yau ko kogin maliya
sai haka. A gigice ya tashi zaune ya fizge
bargon da ya lulluba ya diro daga kan
gadonsa yafito falonsa ya zauna ya cigaba
da kiran wayarta a kashe.
Ya kira dr lukman shima har sau uk bai
amsa ba ,sai na hudun ne ya dauka yana
magana cikin magagin bacci. Dr shuraim ya
fada a dimauce, lukman ka wartsake daga
baccin nan ka saurareni. Farida ce take
cikin wani hali gashi kuma na rasa ta waya.
Ka kira yayanta yahaya umar ka tambaye
shi dan inji halin da take ciki. Dr lukman
yayi firgigit ya tashi zaune yace ban fahimce
ka ba, meya samu farida? Yace yanzu na
kira ta tana kuka ta shaida min suna hanyar
shagamu Allah Ya yiwa antinta abida
rasuwa, mara lafiyar nan. Dr lukman ya
zabura ya dauki doguwar salati yace kashe
wayar ina zuwa barin kira yahaya umar.
Bayan mintuna 15 dr lukman ya kira dr
shuraim yace ka kara hakuri dai zuwa
anjima don yanzu nayi ta kira ba dauka ba.
Daya dauka ma sai naji shi a cikin hayaniya
yake, yace na kashe zai kira ni anjima. Kaga
kenan suna makabarta ko wajen zaman
makoki. Dr shuraim ya dafe kai ya cije lebe
yace halinda farida zata shiga shine babbar
matsalata. Idan ka duba yadda kullum take
kuka saboda rashin lafiyar nan inaga idan ta
mutu? Lukman yaya za'ayi kenan? Dr
lukman yayi ajiyar zuciya yace babu abinda
sai dai muji ra zuwa anjima muji ta bakin
yayan nata tukunna. Nayi maka alkwari
yana kirana zan kiraka kaji halin da ake ciki.
Dr lukman yayi godiya suka kashe wayan.
Har yanzu kiran wayar aisha farida yake yi
taki shiga. Sai ya tuno yana da lambar yaya
hussaini don haka ya cire kunya ya kirashi.
Yaci sa'a kuwa yana kira ta shiga, nan da
nan yaya hussaini ya amsa. Ya ambaci
sunan shi tangararau dr shuraim ne? Caraf
aisha farida ta dago ta dubi yayanta. Dr
shuraim yace sannu yaya, ya akaji da
hakuri? Sai yaya hussaini ya gallawa aisha
farida harara yace af! Kai ma ta fada maka
anyi mutuwa ne? To wannan fadarta ne
kawai, ni