Showing 3001 words to 6000 words out of 139707 words

Chapter 2 - Matar Damisa book Complete by Asmita .txt

Asmeetah   

16 Dec 2024

9940

shima Junaid mutuwa zaiyi"
Ayush kam tayi sumar zaune idon ta ya 'kame 'kam ko 'kifta su batayi,
Umma ce ta bubbuge kafad'arta sannan tayi firgitt ta dawo daga sumar zaunen,
Tsananin tsorone ya bayyana a fuskar Ayush jin yanayin da Junaid ke ciki duk da bata sanshi ba amma tana jin fargabar haduwa da shi "hatta idanunsa komawa yake irin na Damusa?". Tayi tambayar a ranta tareda jinjina kai ,
Ayush ce ta maido hankalinta kan mahaifiyarta sannan tace "Umma kenam bashida magani shi ciwon Junaid din?"
Wani irin murmushi Umma tayi mai 'kona rai sannan tace "akwai mana, warakar ciwon Junaid yana a jikin ki"
Wani irin had'iyar yawu Ayush tayi ido waje tace "Umma meyasa duk wani tsafinsu yake jikina, shin meye abun dake jikina?"
Tace "ba nace miki raunin mahaifinki yana jikinki ba, to haka shima Damusan tsafinsa yana jikin mahaifinki, da zarar kin cire wannan abun dake jikinki shikenam kin lalata komai, kin tarwatsa mahaifinki sannan kuma Damusan shima tsafinsa zai lalace da zaran tsafin Damusan ya lalace kuma shikenam Junaid zai samu lafiya, Damusan zai fita daga jikinsa,
Sai dai hakan zaiyi matukar wahala saboda dole saikin zubda jininki sosai kafin abun ya fita daga jikinki hakan kuma zai iya jawowa ki rasa rayuwarki"
Fashewa Ayush tayi da kukan gaske tana fad'in "Umma ki gaya mun abunda ke jikina, wallahi nayi Alkawari ko zan rasa rayuwata saina tarwatsa tsafin mahaifina sannan na ceto rayuwar Junaid" kuka takeyi sosai.
Cikin lallami Umma take fad'in "Zan gaya miki Ayush, badon zaki raunana ba dana dad'e da cire miki saidai mahaifinki bazai bari hakan ta faru ba, saboda hatsabibin boka ne,
Amma Zan gaya miki kodan saboda rayuwar Junaid",
Tana zubda hawaye tace " *AYUSHMAT* wannan abun tsafin ba komai bane face abunda ke jikin!!
Bata 'karasa maganar ba taji an sha'ko mata ma'kogaro, numfashi Sama-sama Umma take ta zaro ido waje,
Ji tayi daga sama ana magana cikin tsawa " *KEE* *BARA'ATU* *NI* *ZAKI* *CIWA* *AMANA* *A* *GABAN* *'DIYATA* *ZAKI* *TONA* *MUN* *ASIRI*, *ZAKI* *MUTU!* *ZAKI* *MUTU!!* *ZAKI* *MUTU!!!* *HAHAHA*, *HAHAHAHA*,
Dariya ne mai rikitarwa, nan take ta rasa hankalin ta,
Itama dariyar ta farayi, tana tafa hannayen ta biyu tare da fad'in " *Junaid* *Damusa* *wayyo* *Damusa* *kamoshi* *naan*" haka ta rinka Maimaitawa tana kwashewa da dariya, alamu sun nuna cewa Uma ta haukace.

Salati Ayush ta shiga yi tana fad'in "Uma meye haka? Dan Allah ki daina" kuka ne yaci raanta sosai, tazo zata rungumi mahaifiyar tatan. A haukace Uma ta cillata gefe guda tana fad'in "Damusa ce ke! Kar ki ta6ani, Damusa ce ke!! Ta tashi da gudun gaske ta nufi bakin hanya.
Itama Ayush binta tayi tana kuka tana fad'in "Umma Ina zaki je ki dawo dan Allah!.. Kafin Ayush ta sake magana wata karamar motor ce 'kirar Jeep brown colour ta taho da gudun gaske bata Ankara ba tayi sama da Umma, kanta ne yayi mungun buguwa a saman kwalta , kafin kace mai jini kamar anbaliya,
Innalillahi wa inna'ilaihi raju'un daman Umma mutuwa take jira Gashi kuwa rai yayi halinsa, sai ido a bud'e.
Wani irin 'Kara Ayush tayi mai rikitarwa, da gudun gaske ta nufi Uman wacce take kwance ...


Tsugunawa Ayush tayi gaban Uma tana girgiza ta " Dan Allah Uma ki tashi karki mutu ki barni, Idan kika mutu ban San ina zansa kaina baaa" wani irin kuka take na fitar hankali "wayyo Umanaa, ki tashi mana"


Duk kukan da take mai motar yana kallonta ta cikin madubin motarsa ko fitowa bai samu damar yiba,
Motarsa ya fara ja a hankali zai bar wajen!
Cikin 6acin rai Ayush ta mi'ke ta d'auki wani qaton dutsi ta wurga bayan motor da shi, nan take glass d'in motor ta fashe, kansa ne ya bugu da sitiarin motar tsabar burkin daya Danna,


Ransa ne yayi matukar 6aci, DA karfin gaske ya cankar da marfin motar da kafarsa ya fito yana huci.
Itama Ayush gabansa tazo tana fad'in "Kai wani irin Dabban mutum ne Wanda baka San darajan Dan Adam ba, mungu, Azzalumi Mahaifiyata ka buge amma kamar Wanda ka kashe kiyashi,"
Ya kasa juran kalamanta haka yasa hannu ya shaqo wuyanta da karfin gaske, ya d'agata sama da hannu daya, idanuwansa ne suka fara chanza colour,
Ta tsorita sosai da ganin shi haka, ido ta zaro waje tana kakakin mutuwa,
Wani irin shocking yaji yabi jikinsa kamar Wanda ya rungumi electric gass, jiyayi kamar wuta ne yake ci a jikinsa,
Da 'kyarr ya iya wurgar da ita gefe, sauran kad'an ya fad'i 'kasi badon ya ri'ke motarsa da karfi ba, a gigice ya shige cikin motarsa ya figeta da gudun gaske! Shi kad'ai yasan irin rad'ad'in da yake ji a jikinsa, ga hankalinsa ya fara barin jikinsa.


Ayush tashi tayi tangal tangal kamar zata wad'i kasi tayi gurin da mahaifiyar take kwance ta fad'a saman ta, numfashin ta ne ya tsaya cakk, lokaci guda ta sume a gurin.


Motar ce tasau hanya sakamakon ba'a cikin hayyacinsa yake ba, cikin jeji motar ta gangara wata 'katuwar bishiya motar ta daka, kansa ne yayi wani irin buguwa a take shima ya suma.........




Comments and share please ๐Ÿ™๐Ÿ™


*Littafi* *na* *daga* *farko* *har* *zuwa* *karshe* *kyauta* *ne*
Fatana Ku kasance cikin farin ciki ๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜


*ASMEETAH* โœ๏ธโœ๏ธ


Littafi na kyauta ne ๐Ÿ‘Œ๐Ÿ‘Œ๐Ÿ‘Œ


๐Ÿ… *MATAR* *DAMUSA* ๐Ÿ…
(the wife of tiger)


*MALLAKIN*
Asmeetahโœ๏ธโœ๏ธ


*NASARA WRITERS ASSOCIATION*
___________________________________
{{ *_Nasara abin so ga kowa, domin marubuta da cigaban rubutu, alฦ™alaminmu ฦดancinmu._* }}
___________________________________


https://www.facebook.com/103637491942644/


๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ *{{N W A}}* ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ




ุจูุณู’ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ู ุงู„ู„ู‘ู‡ู ุงู„ุฑู‘ูŽุญู’ู…ูŽู†ู ุงู„ุฑู‘ูŽุญููŠู’ู…


Book One
PAGES 11


Kwance take a saman gadon asibiti tana ta sumbatu "Uma! Uma!! Uma dan Allah karki mutu ki barni, Dan Allah Uma ki dawo gareni" tana cikin wannan yanayin hankalinta ya fara dawowa jikinta, ido ta fara bud'ewa a hankali tana ganin Dishi-dishi har idon ya washe
Wata farar Mata ta gani gefen ta tana zaune ta zuba mata ido sai kyakykyawar murmushi dake kwance a saman fuskarta
Tashi ta fara 'ka'karin yi, sai ji tayi matar tace "Sannu ko, ya jikin nakin?"
Tana shirin gyara mata zaman.
Juyowa Ayush tayi tana kallon matar daga bisani tace "Ina Mamana?"
Shafa sumar kanta matar tayi sannan tace "Am sorry my dear, ke kad'ai aka kawo asibitin nan, but mutanen da suka kawo ki sunce already sun sallace Mahaifiyarki bayan sun tabbatar da ta rasu, we're losses your mom"
Fashewa tayi da wani matsanancin kuka tana fad'in "shikenam kin tafi kin barni Uma, Ina Zansa rayuwata, bazan iya rayuwa ba tare dake ba Uma, bani da kowa innalillahi wa inna'ilaihi raju'un" kuka ne yaci raanta sosai.
Rarrashinta Matar take tana bata baki, da haka har Ayush ta samu da dawo hayyacinta, ajiyar zuciya ta shiga ja.
Murya a sanyaye Matar take fad'in "Allah yana tare da ke, insha Allahu bazaki tozarta ba"
Ayush murya Ciki-ciki tace "banida kowa sai Uma na, yanzu Ina zansa kaina"
Ajiyar zuciya Matar tayi ta jawo Ayush jikinta tana shafa bayanta alamar rarrashi sannan tace "meye sunanki?"
"Sunana Ayushmat" atakaice ta bada amsa!
"Shin zaki iya zama a tare da ni?" A cewar matar.
'Dagowa Ayush tayi ta 'kurawa matar ido daga bisani ta mayar da kanta saman jikin matar, batace komai ba.
Matar ce ta sake yin magana tace " no karki damu insha Allah Zan ri'keki tamkar mahaifiyarki, ni sunana *DOCTOR* *FATEEMAH* wannan asibitin da kike gani 's my own, inaso ki kwantar da hankalinki, zaki cigaba da zama dani a gidana". Kafin ta rufe baki taji wayarta tana ringing, d'aukar wayar tayi tare da karawa a kunnenta, ji tayi ance *HAJIYA* *KI* *DAWO* *GIDA* *YANZU* *AKWAI* *MATSALA* daga nan aka katse wayar!


"Ikon Allah meke faruwa ne, kinga Ayush ki jirani Ina zuwa yanzu" ta shafa sumar kan Ayush tare da d'aukar hand-bag d'in ta tana tafiya cikin tsari duk da tana had'awa da Sauri-sauri sai takun takalminta da kake ji qwas qwas qwasss, dan'kararren less ne a jikinta tasha d'inkin Riga da zani sai gyalen data yafa, ko Ina sai 'kamshin turaren jikin ta yake, asalin er washh ce,
Ayush kallon ta take ba 'karamin burgeta Doctor Fatima tayi ba, har sai data 'kule mata kafin da dawo da kallon ta kan ledar ruwan da aka d'aura mata.


Da gudun gaske Doctor Fatima ta shige harabar gidanta da dan'kararren motor ta black colour mai taya ta bayan motar.
En Sanda ta gani su uku sunyi cirko-cirko suna jiran isowarta already mai gadi ya barsu sun shigo cikin gidan, cikin tashin hankali ta nufi gurinsa tana fad'in "lafiya kuwa na ganku a cikin wannan yanayin?" Ta 'karasa maganar tana kallon Ogan nasu.
Ogan ne ya bada umarni cewa "a fito da shi"
Doctor Fatima ce ta maida kallon ta kan Wanda za'a fito dashi daga cikin motor,
Lokaci guda ta furta "innalillahi wa inna'ilaihi raju'un *JUNAID* , maiya faru da shi? ya naga jini a saman kansa? mai kuka mishi? Wayyo Allah na Junaid, Allah yasa dai ba ciwon naka bane ya tashi" tana zubda hawaye tana sumbatu.
Wani daga cikin en sanda ne yace "Hajiya wad'annan tambayoyin nakin bazasu amsu ba anam sai mun shiga daga ciki tukun"
A gigice Doctor tace "to to toh mu je mana jini yanata zuba masa"




Ayush kuwa dake kwance saman gadon asibiti ta 'kudurta a raanta a cewa duk Wanda yayi sanadiyar mutuwar mahaifiyarta sai ta d'auki fansa,
Jinin mahaifiyata bazai zuba a banza ba.....






*ASMEETAH* โœ๏ธโœ๏ธ


*LITTAFI* *NAH* *KYAUTA* *NEH* ๐Ÿ‘Œ๐Ÿ‘Œ๐Ÿ‘Œ


๐Ÿ… *MATAR* *DAMUSA* ๐Ÿ…
(the wife of tiger)


*MALLAKIN*
*ASMEETAH* โœ๏ธโœ๏ธ




*NASARA WRITERS ASSOCIATION*
___________________________________
{{ *_Nasara abin so ga kowa, domin marubuta da cigaban rubutu, alฦ™alaminmu ฦดancinmu._* }}
___________________________________


https://www.facebook.com/103637491942644/


๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ *{{N W A}}* ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ




ุจูุณู’ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ู ุงู„ู„ู‘ู‡ู ุงู„ุฑู‘ูŽุญู’ู…ูŽู†ู ุงู„ุฑู‘ูŽุญููŠู’ู…


*BOOK* *ONE*
*PAGE* 12 to 13


Wani katafaren gado na alfurma aka kwantar da Junaid yayi Jina-jina goshin nan a fashe sai tsiyayar da jini yake, da gudun gaske Doctor Fateemah ta nufi d'akin medicine cikin gaggawa ta dawo hannun ta ri'ke da akwatin boxes, nan take ta fara treat dinsa, duk kayinsa sai data zagaye shi da bandeji tare da yi masa allurai,
Sai da ta kammala yimasa magani sannan ta maida hankalinta kan en sandan da suka kawo shi,


"Nagode muku da taimakon gaggawar da kukayi masa, ba karamin wahala yasha ba" ta 'karasa maganar tana goge kwallar da ya zubo Mata.


Ogan cikinsu ne yace "ki godewa Allah Hajiya, Allah ne ya kaimu gurin da yake har muka tsinto shi,
Munje yawon patrol ne cikin wani daji, munga bayan glass din motor a fashe sannan ya daki wata 'katuwar bishiya, a gaskiya bamuyi tunanin zamu ga Junaid ba a wannan yanayin" anan Dan Sandan ya tsayar da maganar sa saboda bayan haka basu San maiya faru da shi ba.


"Ni daman nasan za'ayi haka, Junaid baya jin magana, duk abunda ya 'kudurta a ransa cewa zaiyi to ba wanda ya Isa ya hanashi, hakan zaiyi sanadiyar tashin hankalin kowa,
Yace mun zaije gidan Barrister Ahmad abokin Mahaifinsa! Na dakatar da shi akan kar yaje amma yayi kunnen 'kashi, gashi yanzu abunda ya faru dashi,
A tunani na duk kwana biyun nan a gidan Barrister yake ashe yana jeji rai a hannun Allah..."
Lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka "yaaa Allah ka magance mun ciwon dake jikin yarona, shi ba DAMUSA ba, shi ba MUTUM ba".
Magana take a cikin kuka, ta kafa gwiwowinta 'kasi Kai a sunkuye take kuka mai 'kona zuciya.
(Ko ba'a gaya muku ba Doctor Fatima tana cikin mawuyancin hali na rashin lafiyar Junaid).


Duk en Sandan dake waren ba wanda baiji tausayin Doctor Fatima ba
Cikin Rarrashi Ogan yake fad'in "kiyi hakuri Hajiya duk tsananin ciwo yana da magani, insha Allahu Oga Junaid zai samu sau'ki,
Shawaran da zamu baki shine, ki ringa kula da shi sosai , duk yanda za'ayi kar kina barinsa yana fita, tinda a kowani lokaci ciwonsa zai iya tashi.....

Sufa d'aya *JUNAID* yayi daga kwance ya cakko wuyan Dan Sandan bai 'karasa maganar ba.
A wani irin yanayi Junaid yake kallon cikin idanun Dan Sandan da ya zaro ido waje tsabar sha'kar da yayi masa,

Idon Junaid ne ya koma kalar ta Damusa, ba alamar d'igon ba'ki a cikin idon, gurnani yake irinta zakunan da suka samu nama, jijiyoyin jikinsa ne suka tashi tin daga saman kansa har 'kasin sawayensa sunyi tsirbo-tsirbo, sumar kansa dake kwance duk sun tsaya Cirko-cirko, da iya 'karfinsa ya d'aga Dan Sandan nan sama da hannu d'aya, still hannunsa yana sha'ke da wuyansa,
sai 'Kafar Dan sandan da yaketa lilo yana 'ko'karin ceton kansa amma ya kasa hakan, numfashinsa ya tsaya cakk 'karfinsa ya sake babu wani 'karfi a tattare da shi.


Tin farkon al'amarin sauran en sandan da sukaga hakan suna ja da baya har suka fece kowa 'ko'karin ceton ransa yake,


Ita kuwa Doctor Fatima ba abunda take sai ihu, tana 'kwalla 'kiran security na gidan amma basu jiyota ba,
Su dai sunga en sanda sun fita da gudu ko motarsu basu tsaya d'auka ba,
Amma kwata-kwata basuyi tunanin dubowa mai ke faruwa ba,
Domin sune masu aiki akan Junaid da zarar ciwon nan ya tashi,
B-guard ne Doctor Fatima ta samosu saboda Junaid tana biyansu salary duk wata,
Wasu Mazaje ne Manya-manya masu 'kirar 'karfi, irin American man din nan ba'ka'ke ne wuluk ga tsayi ga 'karfi, idan suna tafiya jikinsu har rawa yake,
Kana ganinsu kasan ba 'karamin motsa jiki suke ba.
Irin yasu su hudu ne a cikin gidan, amma duk 'karfin su da 'kyar suke danne Junaid 'kasi idan zasu d'aure shi muddin in ciwonsa ya tashi.


Junaid fa ya kusan yin kisan kai,
Daga gurnani har ya koma ihu irin na Damusosi,
Wani Dabara ne yazo wa Doctor Fatima jiki na rawa ta d'auki Allura ta zu'ki magani mai sa bacci cikin en mintina,
Hakan kuwa tayi cikin 'karfin hali ta caka masa wannan alluran ta bayansa,


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login