Showing 30001 words to 33000 words out of 112373 words
Chapter 11 - AGE MATE'S Complete Document book by Momy Fareesa .txt
 biye da ita"ko sallamarsu mamy bata Amsa ba tace"yaya jikin kun dawo ne??"fad'awa jikin mamyn tayi ta saki k'aramin kuka "da mamaki Dr darma ke kallonta saiya daure fuska"mamy ta bishi da wani irin kallo irin na tuhuma fuska Ad'aure tace"meye kamata da kuka fita?"ni kuwa meye zan mata mamy bayaga kyauta tawa?" shine zata kama kuka tamun sharri na mata wani abun ko?"ke kuma  kin kyauta"ya fad'a yana Ajiye ledojin yasa kai ya fita kota kan Abincin da yake nufin yaje yaci be biba"mamy kuwa rarrashinta ta dingayi ta zuba mata Ayabar cikin plate da raken"sannan ta kamata ruwa tasha magungunan...har Ahyaan ta gama ciye ciyenta tayi sallar magrib da isha'i uban gayyar be koma shigowa gidan ba "ranta ya bata yaji haushin Abinda ta masa jiya"wata zuciyar kuma na sanar mata k'ilan wajen wannan yarinyar ya tafi.....
         misalin k'arfe 9:48 pm ummah ce zaune Abed room d'inta tayi tagumi Abin duniya ya isheta"sbd kimanin kwana 6 kenan tana ganin Abba na nuna k'yank'yaminta ko girkinta baya ci,baya kusantarta ranar kwananta"sannan sai yace taje d'akinta ta kwana baya jin dad'in jikinsa"hankalinta ya tashi matuk'a "sbd itadai tasan tayima mama Asiri irin hakan yafaru da ita"Amma gashi taga yana neman dawowa Akanta?"saidai bata tabbatar da zaton nata ba"tana dai zaman jiran shigowar Abban sbd yau ta Amshi girki...Abba kuwa sai goma saura ya shigo cikin gidan"k'arar motarsa ta saka ummah luba fahimtar ya dawo gidan"hakan yasa ta mik'e tsaye ta fesa turare tana k'ara gyara doguwar rigar dake jikinta ta bacci ta fito tsakar gidan"tana fitowa ta samu mamah na tsaye daga bakin k'ofar parlourn ta tana masa sannu da zuwa "ya Amsa yana mik'a mata leda guda ,ta karb'a da hannu biyu tana masa godiya"tsaki ummah taja ,gaba d'aya suka juyo suka kalleta da mamaki"Abba na yamutsa fuska yace"zainab jeki ciki saida safe"to Alh Allah yabamu Alkhairi"ya Amsa da Ameen yana bud'e k'ofar d'akinsa ya shiga"ummah ta biyosa fuska bbu walwala"ko zama beyiba balle ta masa sannu da zuwa tafara da cewa"Alh na gaji da irin banbancin da kake nunawa Agidan nan"Akanme ranar kwanana zaka fara zuwa ka bata Abu?"kinga dan Allah bana son fitinah lubah, Agajiye nake"leda ce daiko ?to ga taki kema"daga yanzun idan kwanan nakine zan bayar Abata in har na shigo da Abu irin haka"idan kwananta ne zan dinga baki sbd nasan ba komai zainab ke k'orafi Akan saba"uhmm ! ba shakka, Ai gara ka ya beta gabana Ai "banza da ita yayi yak'i mgn "dama inaso muyi wata mgn dakai"Ina jinki"meyasa kusan sau biyu kwanana na zaga yowa kana k'in cin Abinci nah,sannan kace naje d'akina na kwanta??bayan kuma ranar girkin zainab nan d'akin take kwana?" cikin b'acin rai yace"sbd Ina jin kina warin jab'a ne "kuma ko yanzun haka warin kikeyi"sbd haka kije ki nemi magani zaki dawo kwana kamar da"wacce ta tsare miki gaba Arayuwa"ba sbd jin dad'in ta take kwana ba"saidan sbd nace ta dinga kwana"kuma duk ranar kwananta saita tabbatar Asma'u tayi bacci take zuwa mu kwanta" Asuba kuma nayi kafin yarinyar ta tashi zata koma d'akinta "taso ta dena kwana nine nan na hana"ke kuwa dayake kwanan ne Agabanki, dana dawo zaki kwaso jiki ki taho"da Asuba saima nadawo masallaci wani zubin nake tashinki ki koma d'akinki ko nauyin Khadija tasan nan kike kwana bakiji.... Abinda zakace kenan ko?"to nagode kaje kaida Allah "Allah ya Isa ban yafe muku ba"kullum kwanan duniya nice baka k'auna wacce bata yin daidai"zainab itace keyin daidai Awajen ka"shine yau harda sharri zaka jefeni dashi wai Ina warin jab'a....ba k'aramin sukar zuciyarsa maganganun ta suka yiba musammun Allah ya isan datayi"Amma da yake dare ne saiya barta"hakan yasa ta mik'e tsaye ta fita hankalinta tashe tare da tunanin zata je gun boka...Abbah ya sauke numfashi yana tunani"tunda ya Auri luba be tab'a jin sonta ko sha'awar taba "tunda dama mahaifiyarsa ce ta tursa sashi ya Aureta "yana dai sauke nauyine sbd ya fita hakkinta yake kwanciya da ita"tsawon zamansa da zainab ba zaice bata tab'a yimasa laifi ba sbd yau  da gobe sai Allah "Amma kyawawan halayenta ya saka ya jure cin zarafin da mahaifiyarta(Ammah) ke masa ya zaunah da ita" sarai yasan itace ke cusawa Ahyaan son ta Auri me kud'i"shi kuma yaci burin kowa ta kawo sai yayi bincike kansa yaga ya cancanci ya bashi ita ko kuwa??"shi yanzun fatansa tama samu Aikin.....ya jima a zaune yana tunani"in bacin wasu dalilai da tuni ya saki luba"saidai wlh lokaci yake bata"nan gaba saiya bata mamaki....washe gari da safe Ahyaan ta tashi k'afar da sauk'i harma ta k'ame"ga Aikin had'a break fast mamy ce keyi tace ita ta huta"gaba d'aya su khaleel sai nan nan sukeyi da ita sbd wai batada lafiya"ita dai saidai tayi murmushi tana jin dad'in hakan"tana lura koda Asuba mutumin nata be shigo ba"gashi har 7 am ta d'an gota be shi goba"can ta tashi ta saka hijab taje kitchen ta sanarwa mamy zataje ta gaida su mamah"bayan ta fito har zata wuce ta lura da d'akinsa bud'e yake"ga mashin nasa shima gefe Ajiye yasha wanki"tsintar kanta tayi da nufar k'ofar d'akin"sau biyu tayi knocking! waye ne?"shiru tayi ta turo k'ofar ta shigo da sallama.....da sauri ta juya k'irjinta na wani irin bugawa" sbd ganinsa tsaye gaban mirror sanye da dogon wondo na jeans"yana warware farar vest zai saka.... yad'an kalleta ya tab'e baki sbd ganin duk illahir jikinta rawa yakeyi tanama k'ok'arin fita...dama gulma ce ta kawoki kenan ko?"ya fad'a cikin taushin muryansa yana Ida saka vest d'in"kayi hak'uri bansan shiryawa kakeyi ba"ta fad'a cikin jin fad'uwar gaba"dukda dama ta fahimci yanada k'iran mazan taka Amma ta tsorata da k'iran jikinsa"musammun curarran uban gashin data gani saman faffad'an k'irjinsa "ga jikin nasa duk gashi Amurd'e"itafa wlh tsoron ganin namiji babba takeyi irin haka....ki jira! na gama saka rigar Ai"shiru tayi bata juyo ba"shi kuwa turarukansa yamatsa ya d'auka yafeshe jikinsa dasu"kafin ya d'auki Agogo ya zauna gefen bed d'in yana fad'in idan bazaki iya juyowa ba kije mana"Amasife ta juyo ta gallah masa harara tana fad'in dan kama samu nazo na gaisheka shine zaka gayan bak'ar mgn?"kece dai kika d'auka bak'ar maganar ce"sai tayi shiru ta zauna saman sofa tana fad'in Ina kwana?"ya d'auki kusan second 5 kafin ya Amsa da lafiya qlau ya jikin ?"itama biris tayi dashi saida ta mula tasha iska harma ya mik'e tsaye yana dai binta da kallon k'asan Ido,kafin tace"daka damu da sanin ya jikin daka je tun d'azun ka duba kaji"zan wani gaida kai ka Amsa mun irin haka" sai kace irin y'an matan dake cusa kansu mararsa Aji"Amamakinta saiya saki d'an murmushi ya matso gefenta ya zauna"tad'an lumshe Ido sbd yadda k'amshin turarensa ke dukan hancinta....kin gama?"ah ah"ke matsalata  dake masifa"Amma Ai kaine kamun k'orafin bana gaisheka bana girmamaka"shine nazo zaka wani d'auke mun kai"hmm! ke yanzun Abinda kika mun jiya kin kyauta?"oh ban kyautaba fa tunda ban bari kayi zance da budurwarka marar class ba ko?"baki canka daidai ba"wannan yarinyar bata daga cikin irin tsarin macen dana ke so"okay to wacece k'anwar tawa?"kaga ranar friday sai muje na rakaka zance"saidai wlh kama sanar mata ni Antyn tace ko kuwa yasin na baka kunya Agabanta ba ruwanah....Uhmmm!  shafawa kanki ruwan sanyi ni banida wata budurwa"saidai ko kece keda saurayin ko?"Allah yasawak'a"ta fad'a cikin jin haushi tana mik'ewa tsaye"shiru kawai yayi sbd Al'amarin nata har tsoro yake bashi ,saidai zasu cigaba da Addu'a da bata taimakon har Allah yasa Adace"Ina zakije?"mama zanje na gaido"jirani muje"nidai gaskiya ban zuwa dakai"kaje kai d'aya daga baya nina je"kuma saina maka gami da mamy "ta fad'a tana d'an murmushin da yayi mata masifar kyau"sai kuma ta wani marairaice murya tace" broth bani turarukan naka na fesa"bazan bayarba ke Ina naki?"banza ta masa ta fice daga cikin d'akin"ya bita da kallo yana sauke numfashi "Anutse ya fito daga cikin d'akin ya rufe yana duba wristwatch d'insa sbd karya makara"yaso ya bata keys ta gyara masa d'akin ,to yasanta da shegen Lambo zatace bata lafiya "sashen su mama ya wuce yasha Lipton be sami Ahyaan Acan ba"wato sbd nace zanje shine tak'i zuwa?"ya fad'a Aransa yana wucewa sashen su mamy"Ahyaan na kwance saman kujerah, kanta na saman cinyar mamy tanata shagwab'a"kallo d'aya Dr darma ya mata ya d'auke kansa ya shigo ya duk'a fuska bbu walwala yace mamy Ina kwana?"lafiya qlau.....Ina d'an kwalinki ko hula?batayi mgn ba sai mik'ewa tsaye da tayi ta wuce d'aki "wai mamy meyasa kike gani tana yin Abinda ba daidai ba fisabilillahi baki tsawatar mata?"dubi kayan dake jikinta ?"bayan maza na shigowa kuma....sai yayi shiru "ita dai mamy kallonsa takeyi sbd ganin yadda yake maganar cikin nuna jin zafinsa"saidai bata samu damar yin mgn ba Ahyaan ta fito sanye da hularta ta gifta shi ta wuce"ya d'an lumshe Ido sbd jin k'amshin turarukan jikinta"be koma mgn ba ya mik'e tsaye yana jin mamy na cewa Adawo lafiya yayi kamar be jiba ya fita"da dabara mamy tayi mata nasihar ta rage saka k'ananun kaya sbd mazan dake shigowa musammun dangin daddy irinsu sadeeq"dato ta Amsa tama wuce d'aki ta canza kayan....
      yau daya taso daga Asibiti be biya ta chemist ba sbd yau laraba zaije wajen wa'azi"kasancewar 2 pm ne lokacin tashi sai kuma wata safiyar"saidai dayake babban likitane idan Ansami patient emergency za'a kiransa ko wane lokaci yazo"hakan yasa wajen biyu da rabi ya dawo gidan cikin wata had'ad'd'iyar zukek'iyar sabuwar mota bak'a"Mercedes Benz k'irar E350 "wacce zatayi million 8"yana isowa bakin get yayi parking ya fito yana d'an murmushi ya bud'e get d'in gaba d'aya sannan ya dawo cikin motar ya shigo cikin gidan yana danno horn"kafin yayi parking ya koma fitowa ya rufe motar"yana d'ago kansa ya lura da Mubarak na tsaye yana kallonsa shida motar"sai yaga ya juya da sauri ya wuce sashen su"ya tab'e baki sbd yasan uwarshi zaije ya kaima labari"d'an murmushi ya saki daya tuna tsiyar daya saka Aka mata....p cap d'in saman kansa yaja baya"Atake kyakykyawar choko face d'insa ta fito sosai"ya saki d'an guntun murmushi sbd tuna koya Ahyaan zataji idan yace wannan motar sace??"cikin gidan ya wuce "tun kafin ya shigo cikin parlourn yake k'wala mata kira" Ahyaan! Ahyaan!! ya furta cikin nutsatstsiyar muryansa data rage sauti sbd gajiya da rashin sabo da duba patient.....Oh yah rabbih broth! "wannan wane irin kira ne kuma?"ta fad'a tana lek'owa suka had'a Ido dashi"sosai yaji sanyin ganinta da riga da siket na Atamfa kuma ba sosai suka kama taba"wai baza kayi mgn ba?"ta fad'a cikin shagwab'a "zo muje kiga wani Abu"saida ta turo baki sannan ta kallesa saiya harareta yace"idan bazaki zoba ki koma mana"sbd kinga na damu dake ko?"to Amma broth basai...shiru tayi sbd ganin ya juya zai tafi"saita biyosa Abaya"suna isowa bakin get d'in taga motar"wow ! motar waye pls?"ta fad'a tana matsawa gefen motar ta shafeta tana sakin murmushi "shima murmushin ya saki yace"tamuce ! Ihun murna tayi harda d'an tsalle"taji dad'in da yace tamuce"ta d'auka zaice tawa ce"gaskiya tayi kyau broth "Allah ya tsare yasa Alkhairi "cikin jin dad'in kalamanta ya Amsa da Ameen"kafin yayi mgn ta wuce da gudu sashen su mamy,shidai ya girgiza kansa tare dashan Alwashin zai mata Jan Ido ta dena guje guje "be gama wannan tunanin ba ta fito ta wuce sashen su mamah"ba tafi mintina 5 ba saiga mamah da Asma'u da Khadija da luba sun fito"Ahyaan na gefen mamah tana fad'in kunga motar nan mama"kai Masha Allah! Allah yasa Albarka ya tsare yasa rabo ce nurah"Ameen mamah"saidai yana lura da ummah luba na ganin motar ta juya ta koma ciki"dama sbd ta tabbatar da Abinda taji Ahyaan ta shigo cikin murna tana fad'i "kuma duk suna tsakar gidan"d'age kafad'a yayi sbd dama baya buk'atar Allah yasa Alkhairin ta"Allah yasa Alkhairi"cewar Khadija "yayi banza da ita"saidai Ahyaan ce ta Amsa "ya matsa ya bud'e k'ofar motar"Ahyaan tayi saurin shiga driver sit ta zauna "mama ki matso ki gani mana"ya fad'a yana d'an murmushi yana satar kallon Ahyaan " Ai na gani ma ,abu yayi kyau kam"Ina mamy?"tana ciki nace tazo ta gani kinga bata fito ba "wai naje na kiraki kece mamansa in kin gani ya wadatar"cewar Ahyaan "ah ah itama yaka mata tazo ta gani ta sanya Albarka ko? cewar mama tana nufar sashen mamy "Asma'u tayi masa Allah yasa Alkhairi itama ta wuce ciki"broth in kunna tah?"ta fad'a tana d'an lek'owa suka had'a Ido"saidai kafin yace" wani Abu sunji muryar mamy na cewa ". na gani mama Allah yasa Alkhairi yasa rabo ce"ya Amsa da Ameen su kuma ko wace ta wuce ciki"zagayowa gefen me zaman banza yayi ya zauna"Ahyaan kuwa kunnah motar tayi"kina nufin kin iya driving dama?"da meka d'aukeni?"ta fad'a tana rufe k'ofar ta zuge glass d'in tana murmushi "cike da k'warewa ta fara zagaye haraban gidan tana murmushi"shidai yana kallonta,sai kuma tayi parking daidai get"Allah broth kanada kud'i nima saika siya mun tawa motar"Allah ya hore Abinda yafi motama zan siya miki Ai"kuma wannan Ai tamuce ko?"sannan duka million biyu da rabi  na biya cikin Albashina duk month zan dinga biyan su har na biya 8 million"to nidai dan Allah karka sanarwa da kowa broth "kawai dai kaci gaba da biya in sha Allah harka Ida cika musu d'in"kinsan dai bana yin k'arya ko?"Allah ko?"to rantse tunda kake baka tab'a yiba ustazah "yayi shiru shima kansa beda tsarin ya sanarwa kowa itama besan meye yasa ya sanar mata ba?"muje ciki naci Abinci ya fad'a tamkar bayaso yana duba time"gaskiya naji dad'in motar nan "dama nayi rantsuwar na gama hawa mashin naka duk rintsi "saida ya tab'e baki kafin yace"saiki shirya yin kaffara kuwa yarinya "dan hawa mashin d'ina yanzun kika fara"wacece yarinyar?"dama Anan mu nawane?"kaje kaida Allah"murmushi had'e da dariya ya saki"ta masa banza ta fito daga cikin motar rai b'ace"shima fitowa yayi ya rufe Adaidai lokacin kuma mu'az ya shigo cikin get d'in gidan"Ahyaan sarai ta gansa Amma sbd Abokin sa ya b'ata mata rai kallo be ishetaba ta wuce ciki.....��
wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
 Acc n  2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251
dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba 
Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn
Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba
#Mommyn fareesa 
#Dr Nura Darma
#Ahyaan 
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: � *AGE MATE'S* ��♀�
*23&24*
*Littafin kud'i ne!*
...... tab'e baki Dr darma yayi yana gyara zamansa saman motar"Azahiri babu wata Alamar ya damu da rashin gaida mu'az da bata yiba"Amma A bad'ini yaji haushin Abin "ya kuma lura da mu'az d'in ya fahimci ta gansa Amma ta basar ta wucesa....kace nazo A Asa'a kenan Abokinah?"irin wannan zazzafa haka"ya fad'a yana murmushi ya iso gefensa yana kallon motar"Dr darma dai yana kallonsa harya juyo sukayi musabuha "gaskiya tayi kyau Allah yasa Alkhairi"Ameen Angon nanda wata biyu"uhmm ! kamar na jawo lokacin haka nakeji wlh "ko yanzun haka wasu drugs nazo ka rubutamin naje na siyo pls"idan kuma kana dasu ka bani"ciwon mara ya taso ni gaba"ya mutsa fuska Dr darma yayi yana fad'in banza jarababbe"uhmm! naji komai zaka fad'a "gara ni na nuna tawa jarabar"wani ko b'oyewa yakeyi saidai yayita faman yin Azumin litinin da Alhamis "fatana dai sadda Fatima zatazo ba period takeyi ba...kaga pls mu dena wannan zancen"bakada wata fira saita mata"dariya mu'az ya dinga b'abb'akawa kafin yace k'aryar banza kakeyi wlh, Akwai wacce kakeso ka b'oye ne dai kawai sbd ai ba dutsi bane kai"mata kuma dole nayi zancen su sbd sune jin dad'in rayuwa ustazah "laifin meye ka yiwa Ahyaan ta wuce tana ganina bata mun mgn ba?"wato laifinka ya shafeni kenan ko?"wai Darma sai yaushe zaku dena irin haka kaida ita?"banza ya masa yana dannah waya"kafin ya diro daga saman motar yana fad'in haushi taji sbd nace mata yarinya"ta kasa d'aukar mataki sai cewa Akayi nida Allah"ya fad'a k'ayataccen murmushi na sub'uce masa "tayi daidai Ai ,tunda Al'amarin naka yak'i sauk'i saita koma barinka ga Allah d'in"kaga ni ciki zan wuce Abinci zanci muje idan mun fito muje shago na baka drugs d'in sarkin jaraba"An sanya maka Rana Amma har yanzun kana fama da ciwon mara "ya k'are maganar yana yin gaba"hmm! kaima kana fama dashi kana dai b'oyewa ne tunda kai likitah ne"sharesa yayi yak'i mgn"tun kafin su shigo cikin parlourn yaji muryar Ahyaan nata yiwa mamy shagwab'a "sai yaji dama be shigo da mu'az ba"sai kawai ya fara sallama tun daga nan kafin suma shigo"Ahyaan najin sallamar sa ta had'e rai"duk mamy na lura da ita"saidai muryar mu'az dataji ya saka ta kalli bakin k'ofar ta gansu sun shigo Atare"ta Amsa sallamar tasu da fara'a tare da cewa mu'az kaine Agidan?"nine mamy Ina wuni?"ya fad'a yana russinawa"lfy qlau yasu hajiyar taku?"Alhamdulillah"Masha Allah "daga  haka suka wuce dining area"sai bayan sun zauna Ahyaan ta gaidashi"yana tsokanarta tak'i yin mgn sai harara da take wurgoma mutumin nata"duk yana lura yadai shareta"mamy dai barin parlourn tayi........tashi ki kamana ruwah"cewar Dr darma tamkar bashi yayi maganar ba"tayi banza dashi"bakiji ne wai?"kin tankashi tayi ta mik'e tsaye fuska Ad'aure ta nufi kitchen"bata jimaba ta dawo rik'e da goran ruwa guda da cup"Anutse ta matso gefen mu'az ta Ajiye masa gabansa ,shiko doctor be isheta kallo ba"saidai bata saniba gaba d'aya idanunsa na kanta"sai wani tsuke lips takeyi tana Ajiyewa tabar wajen"mu'az yace" thanks"yaji haushi saidai be nuna ba"bayan sun gama cin Abincin Atare suka sha ruwan suka fita gaba d'aya sbd lokacin sallar la'asar yayi....Ahyaan kuwa itama sallah tayi ta canza sabon wanka"ta shirya cikin riga da siket na lace pink"sun kamata sosai kayan ,dan sun bayyanah suran jikinta"ta d'akko hijab me hannu tiyebo gogaggiya, ta fesheta da turare ta fito parlourn ta zaunah"mamy ta dubeta da murmushi saman fuskarta sbd ta mata kyau sosai"saidai tausayinta ne fal Aranta sbd yanzun tasan matsalar Ahyaan d'in game da k'in son Aure da nuna k'in mazama gaba d'aya data keyi."y'ar gidan mamy sai Ina kuma?"broth nake jira yazo muje gun wa'azin islamiyar su"ta fad'a tana duba time"4:5









