Showing 69001 words to 72000 words out of 112373 words
Chapter 24 - AGE MATE'S Complete Document book by Momy Fareesa .txt
 Auren nasa yayi"Atake taji fad'uwar gaba data tuna zaiso wata harya Aureta "haka itama Aure zatayi....broth! juyowa yayi suka had'a Ido"ta turo baki, menene?"ba tambayarka zanyiba"to shikenan Ina ji"wai Akwai wacce kakeso ne?"Eh Akwai "ta tab'e baki tana fad'in Ai sai kaje wajenta tayi jinyarka"bestie baki gajiya"ita Ai bata san Ina sontaba"nine kawai na sani"may be ma tace bata sona idan na furta "hmmm ! Ai saika cigaba da b'oye mata"k'ilan ma mummunace ko?"Ai tafiki kyau yarinya"tsaki taja batace komai ba ta wuce "me makon yaji haushi saima dad'i yaji sbd dama tun jiya ya fara zargin yarinyar nan tafara kishinsa"ga kuma Abinda tayi yanzun ya k'ara masa k'warin gwiwar ta fara sonsa"saidai idan yatuna da Abdallah mashi sai yaji fargaba"da wannan tunanin suka shigo tsakar gidan "kasancewar ummah ce keda girki tana tsakar gidan zaune gaban murhun gawayi tana dama koko"ta d'ago kanta ta kallesu Amma bata Amsa sallamar tasu ba"su kuwa kallo bata ishesuba suka nufi parlourn Abba"bayan sun gaidashi suka nufi parlourn mamy "sunaji ummah na yada habaici tsakar gidan suka mata banza"Asma'u dake zaune tana shan tea da yunifoam Ajikinta tace"Anty Ahyaan Ina kwana?"broth yaka mata ki fara gaidawa kafin ni"hakane kuma"yaya nurah Ina kwana?"lafiya qlau Autar mamah"wai Autah yaushe ta zama Autar?"cewar Ahyaan tana ballo mata harara"itadai tayi murmushi batace komai ba"Dr darma dake kallonta yace"sarkin fad'a ni bana jin fad'an yau ki bari na samu lafiya"tana k'ok'arin mgn mamah ta fito daga cikin k'uryar d'aki tana fad'in koki so ko karki so husnah dai itace Autah nah"to wai mama ni wani Abu nace ne?"kince mana"rabu da ita nurah"ta fad'a tana zama duk suka gaisheta gaba d'aya "Ahyaan nata b'ata fuska yace"tashi muje "batayi mgn ba tabi bayansa suka fita"mamah tayi murmushi kawai....suna fitowa yace"zanje nayi bacci"toni Ina ruwana da baccinka?"harda lafiyata duk bakida ruwa da ita?"Eh mana kaje wajen budurwarka ka sanar mata bacci zakayi"nifa wasa nake miki banida wata budurwa"dan Allah da gaske kakeyi?"kansa ya gyad'a mata yana binta da wani irin kallon dataji kasala"sai yaga tana walwala"dukda bayajin dad'i saida ya saki murmushi "to yanzun kaje ka kwanta ,bara na wuce naga meye yaka mata na kamaka ka samu kaci kasha magani ko?"dato ya Amsa yayi tsaye "kaje mana bestie"to kuma sarauniya babuko rakkiya"tayi murmushi ta kallesa tace" muje to"na lura baka son yin Aski broth"inaso yau naje idan Amun jikin da sauk'i "shikenan idan da sauk'i sai muje na rakaka ko?"uhmm"yafad'a Adaidai lokacin da suka iso bakin k'ofar d'akin"da kanta ta murd'a handle d'in k'ofar cike da tausayi tace"Allah yabaka lfy"Ameen *Aminatu babbar budurwa*"ta saki murmushi me sauti ,shima yana tayata ya wuce cikin d'akin tajawo k'ofar ta rufe kafin ta wuce side nasu....tana shigowa cikin kitchen mamy ta kalleta tace "da yanzun zan tura Akiraki kizo kiyi shirin tafiya office har bakwai ta kusa ,baki gudun ki makara ne?"Ai mamy yau ba zanje office ba gaskiya"Akanbme kenan.....??��
wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
 Acc n  2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251
dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba 
Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn
Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba
#Mommyn fareesa 
#Dr Nura Darma
#Ahyaan 
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: ��♀� *AGE MATES* �
*51&52*
*Littafin kud'i ne!*
..........broth fa ke  bashida lafiya sosai mamy,zuwan meye zanyi a office ?"shiyasa da Asuba kikaga bezo ya gaisheki ba"shima bazai je office d'in ba"so nakeyi ma nasamar masa wani abun yaci yasha magani"ta fad'a fuska kalar tausayi tana k'ok'arin d'aukar tukunya ta tara gaban sink zata d'auraye....baki bud'e mamy ke binta da kallo sbd ganin Abin nasu daga ita har nuran Azimun ne"ta kalleta tace" Allah yabashi lafiya! Amma ki Ajiye batun baza kije wajen Aiki ba Ahyaan"dadai kece bakida lafiyar saiki k'i zuwa....pls mamy bazan iya zuwa ba broth na kwance haka "ko naje bazan nutsu ba sbd....sai kuma tayi shiru ta saki kuka"subahanallahi! Abin bekai hakaba Ahyaan "kiyi hak'uri ki dena kuka ki zauna Amma kin kira can wajen Aikin naku ki sanar musu kinada uzuri  ko?"uhmm zan sanar musu mamy "dato kawai ta Amsa tana jin wani iri"ita Abin nasu ya wuce ma iya tunaninta sai Addu'a kawai"damuwarta guda shine meyasa Abaya basu kasance irin hakaba ? saida yanzun Ahyaan ta kusan zama rabon wani suke shiri dason juna....har mamy ta gama Aikinta Ahyaan na cikin kitchen d'in na had'amun Dr Darma Abin break fast....."tsabtataccen kunun gyad'a ta dama masa ,sannan ta soya masa Awara da doya da k'wai"bayan ta gama ta fito daga cikin kitchen d'in rik'e da tray d'in data jera masa komai Asama.....kasan dai ba haka nan zaka kirata bata d'auka bako? Idan kayi hak'uri gata nan fitowarta daga cikin kitchen d'in kenan"tana fad'in hakan ta kashe wayar"Ahyaan ta b'ata rai tana fad'in kai mamy broth uzuri zaki masa baya lafiya fa"may be yakirani ne yanaso na kamasa wani abun ko kuma Aikena zaiyi"ke kuma kinata fad'a ko?"Akanme bazan masa fad'a ba tunda beda hak'uri"ke kuma yanzun gaba d'aya baki son laifin sa ko?to kirashi yazo nan ya karya bbu inda zakije"pls mamy dana kai masa zan dawo wlh yana jin jiki fa.....shiru tayi sbd jin tattausan muryarsa datayi k'asa "ta juyo da sauri suka had'a Ido"yana sanye da coffee brown d'in jallabiya me gajeran hannu wacce tad'an d'age masa"da Alama wanka yayi"idanun nasa sun rage ja"sbd yad'an sha Lipton da lemon tsami yasha wani magani"shine yad'an samu y'ar nutsuwa "ya gaji da jiran tazo shine daya kira mamy ta kama yimasa fad'a"sai ransa yabashi baza tabar Ahyaan d'in tazo wajen saba"sai gashi duk yaji kalamansu yanzun dazai shigo.saidai kayan daya gani Ajikin Ahyaan sun sakashi koma shiga cikin wani sabon yanayi"zani ne na Atamfa Ajikinta "sai rigar bacci me hannun vest,rigar ta kamata kuma wuyan nada girma"sau guda ya kalleta ya kauda kansa yana Amsa sannun datake masa ya zauna kan carpet "gabansa ta Ajiye tray d'in ta juya ta koma d'aki"mini hijab ta sako zata fito taji mamy na masa fad'a da cewa"meyasa kake son kiran yarinyar nan idan kana d'akinka?"basai na sanar maka illar hakan ba sbd kasani kai me hana wasu ne"kiyi hak'uri mamy tunda bakiso bazan koma kiran na taba"har gyaran d'akinma ta dena zanyi da kaina"ya fad'a cikin wani yanayi na damuwa" ita kanta Ahyaan d'in tasan gaskiya mamy ta fad'a, Amma Aganinta tunda ta yadda dasu bashi kenan ba."saidai itama zata dena shiga tunda mamyn bata so"Ahankali ta shigo cikin parlourn Idanunta har sun ciko da k'wallah na tausayinsa"ita kanta tasan yanzun ya damu da ita fiye da zaton me zato "broth sannu ya jikin?"da sauk'i "batace komai ba ta zuba musu kunun gyad'a d'in cikin cups biyu sbd tasan Idan ta zuba banda ita zaice itama saita zuba tasha"doyan da Awarar suma duk plates biyu ta zuba"tana d'ago kanta da nufin tace gashi taga Ashe ita yake kallo"saita sakar masa wani tsadaddan murmushin daya kusan zautar dashi tana tura masa cup da plate d'in gabansa tace Bismillah broth.thank you bestie"batace komai ba ta gyara zamanta A gefensa ta d'auki cup d'in nata ta kurb'a kusan sau biyu "sai ta lura be d'auki nashi ba"ta saci kallon mamy taga tana kallon sunnah TV "murya can k'asa tace"pls bestie nah kasha kaji?"ni naki nake so"da sauri ta mik'a masa"ya Amsa yana d'an murmushi "Adaidai inda ta saka bakinta Adaidai nan shima yasaka nasa bakin ya fara sha"sannan ya d'auki doya guda yad'an gutsura ya rik'e sauran ga hannunsa"broth! ta kirashi murya can ciki,ya kalleta"bani sauran"murmushi ya mata ya mik'a mata ta Amsa ta nufi bakinta dashi.....dukda ba cikin sakewa suke break fast d'inba Amma kowa nan su na jinsa cikin farin ciki ...saidai Abinda basu saniba mamy na lura da duk Abinda sukeyi"bayan ya gama yafara danna waya"Ahyaan kuma tafara k'ok'arin tattara kayan sbd kusan Atare suka idar"murya can k'asa yace"bestie duba wayarki"uhmm kawai ta fad'a"shi kuma ya mik'e tsaye ya fita"bayan ta kwashe kayan ta dawo ta zauna kan kujerah tana duba wayarta taga text message nasa kamar haka *bestie nah ! zan fita tsakar gidan ki biyoni karki bari mamy ta gane*"kanta ta d'ago bayan ta gama karanta text d'in ,tana yamutsa fuska taja tsaki tace" na rasa meyasa Asma'u ta rainani mamy? Me kuma tayi miki?"hijab d'ina ta d'auka wai za'a mata irinta sai yanzun na tuna bata kamun ba kuma ita zan saka Anjima"Ina zakije Anjiman?"matar mu'az zanje na gaida da jiki idan kin barni"to na hanaki zuwa"wayyo Allah mamy pls"tayi murmushi tace yanzun kije ki Amso hijab d'in "dato ta Amsa ta mik'e tsaye"Adaidai lokacin text message nasa yakoma shigowa "ta kalli wayar tana d'an murmushi batama karantaba ta fita daga cikin parlourn...yana tsaye bakin k'ofar shigowa ya zubama bakin k'ofar parlourn mamy Ido"ta kallesa ta Aiko masa da murmushi..... bestie nah! da baki fitoba wlh shiga zanyi ciki" daka kwafsa mana broth"gani yanzun, kasan dubara nayiwa mamy? ta labarta masa yadda sukayi"yakama y'ar dariya yace bestie ta koma mak'aryaci ko?"to Ai sbd kaine kaga banyi lafiba ko?"hakane dama kawai so nakeyi na ganki muyi fira shine nace kizo"ko ban kyauta ba?"ya fad'a murya can k'asa yana tsareta da Ido"Ahankali tace"ka kyauta *sarki*! wai bestie wannan wace irin sarautace babu dogarai babu rawani ??"ta kama dariya me sauti kafin tace"sannu Ahankali duk zan had'aka dasu suyi gadinka"to shikenan sarauniya"ta lumshe Ido "Allah ka sami sauk'i"Eh to Alhamdulillah "samun sauk'in duk na ganinki ne da kuma fira dake"kai broth kamar gaske"uhmmm kin d'auka wasa nakeyi?"tayi shiru"yanzun kije ciki ki hau online zamuyi mgn zuwa Anjima tunda mamyn tabarki sai muje gidan mu'az d'in "karma ki nuna mata tare zamu fita"to shikenan batun zuwa askin fa?"Abari sai gobe bestie"nidai Allah yau za'a maka"kabar k'asumba duk ta cike maka fuska ba gyara"idan Aka gyara zakafi yin kyau"duk tayi maganar cikin shagwab'a"yad'an lumshe Ido sbd shine kawai yasan meye yakeji idan tana wannan shagwab'ar "shikenan zanje bestie tunda yau kikeso Amun ko?"kanta ta gyad'a masa "ya zaro wayarsa yana fad'in zo muyi photo"niko pics ma baki tab'a yi dani ba ko?"to Ai lokacin cutata kakeyi ko?"yakama dariya yana fad'in ni kuma kina b'ata mun rai Alokacin"yanzun kuma kina faranta mun"batace komai ba ta matso daga bayansa shi yana daga gaba tad'an dafa kafad'arsa suna murmushi ya dinga musu vedios da pics"ganin ta jima yasaka shi cewa broth bara naje zancema mamy na duba hijab d'in Adak'in mamah banganiba"shikenan ki hau online muyi mgn kinji bestie karfa kik'i hawa?"zan hau yanzun fa *sarki*,ta fad'a tana masa gwalo ta wuce ciki"lokacin data shigo mamy ma bacci ya kwasheta"saita zauna suka dinga chats dashi har tayi bacci.....
      misalin k'arfe 4:47 pm"tafe suke saman titin hanyar goruba road"baka jin komai cikin motar sai sautin wak'ar music ,sai kuma sanyin AC da k'amshin turarukan jikinsu"Ahyaan na zaune gefensa Tasha gayunta cikin doguwar rigar Atamfa  navy blue me zanen coffee brown"An k'awata rigar da Adon stones"ta yafa mayafi coffee brown me net saman kafad'a "yayinda mutumin nata ya cakare cikin k'ank'anin kaya da hula p cap da takalmi boot"sunyi masifar yin kyau"darma yayi y'ar rama,yayinda gyaran fuskan da Aka masa ya k'awata kyawun fuskar tasa,yafito masa da tsantsar kwarjininsa da kamalarsa"dukda fuskarsa Ad'aure take sbd sadda suna shagon data rakasa Ana masa Aski wani ya nuna yana sonta"shi kuma ya masa wani mugun yarfi yace"ta koma mota ta jirashi "shine ta kama shagwab'a"ga me Askin A wajen "shine ta bashi haushi"tunda suka shigo yak'i yin mgn "da farko taso ta sharesa Amma sai taji bazata iya ba" Ahankali cikin shagwab'a tace"broth shine kaketa d'aure fuska ko?"yayi shiru yana cigaba da driving d'insa "mlm ka tsaya na sauka idan bazaka kula niba..... Ahyaan wai meye haka?"Abinda kikayi d'azun kin kyauta ?"wlh duk ranar dana koma miki mgn ki dena Abu kika k'i saina b'ata miki rai"kin wani kama shagwab'a gaban wancan wawan "meyesa bazaki bari daga ni saike ba kimun?"shikenan kayi hak'uri Allah ya huci zuciyarka"daga haka tayi shiru"shiru yayi beyi mgn ba har suka iso bakin get d'in gidan mu'az ya dannah horn"get man yabud'e musu get suka wuce"bayan sun iso Ahyaan tayi zaune tak'i fitowa"ya kalleta yace zaman meye kikeyi?"kaje ka fito muje ni baranjeba"daga Abu kad'an shine sai fushi da fad'a meyasa bakada hak'uri?"sai kuma tayi shiru"bece komai ba yazaro waya ya dannawa mu'az kira"yana d'auka yace"mijin tace"gamu nan a parking lot"Amma fa sarauniyar tace"bazata shigo ba.....broth had'ani dashi zakayi?"sai taga yakama murmushi ya maida wayar cikin Aljihu yace"muje kona d'aukeki wlh kinji na rantse"batace komai ba ta fito suka jera Atare suka wuce ciki"mu'az na kwance saman cinyar Fatima"sunsha k'ananun kaya"Amma da mini hijab Ajikinta"Dr darma ya saki murmushi sbd sun bashi sha'awa "Atake yaji inama shine da Ahyaan Ahaka?...... Abokinah ku shigo mana"basuyi mgn ba suka shigo da sallama"sosai Ahyaan taji kunyar ganinsu Ahakan"lura da mu'az yayi yasaka ya janye kansa yatashi zaune suka gaisa"Fatima ta tashi ta cika gabansu da Abin motsa baki suna fira" can Fatima tace" tashi muje ciki mubarsu suyi firan su"Dr darma na murmushi yace Abokinah Allah yasa ba gulmarmu za'ayi ba.uhmm ! kundai tsargune shiyasa"cewar Fatima suna shigewa cikin d'aki.....sai yamma lik'is suka baro gidan mu'az "Dr darma na janta da fira yana driving,sai wani shan k'amshi take masa"shi saidai yayi murmushi kawai "can yace"su mu'az basu burgeki ba bestie? Eh"Allah ko?"to wai bestie miye na wani kawo zancen su kuma?"sun burgeni ne shiyasa nayi zancen nasu"sbd soyayya Abin koyi ce ga kowa indai me kyau ce "kuma yinta da matarka koyine da manzon Allah S A W "sbd yana soyayya da matansa musammun nana Aisha Allah ya yarda da ita.yana wasa da dariya dasu,yana wanka dasu,yana tayasu Aikace Aikace"kema kina so kiyi koyi dasu?"tayi shiru Aranta tana cewa mike damun mutumin nan?banida Amsa ne?"nidai broth ka k'yaleni da tambayar nan taka"shikenan tunda bazaki fad'amun ba "toni na fad'a miki?"ah ah dan Allah "yakama murmushi sbd ya fahimci kunyar zancen takeji"sai yaji ta burgesa"da wannan rahar suka iso gida"shi yatafi masallaci ita ta shigo ciki.....
             ************
Ahaka rayuwar taci gaba da wakana Dr darma na hidimar Ayyukan gabansa cikin samun nassara shida Ahyaan "Ayanzun haka Aikin gidansa ya kusan kammalawa"babu kuma wanda yasan da gidan sai  khaleel da Abdul Aziz da mu'az"sune kawai suka sani"ko Ahyaan be sanar mata ba ya bari saiya Ida saiya kaita ta gani"kullum soyayyar su da juna k'aruwa takeyi"tun Ahyaan bata fahimci sonta yakeyi ba harta fahimta"ita kuwa tuni yajima da sanin ta fara sonsa"saidai basu sanarwa juna ba har yanzun"mamy dai ta zubama sarautar Allah Ido"gaba d'aya daga shi har ita suna cikin fargaban Auren da zatayi"ummah kuwa bata zaunaba taci gaba da biye biyen malamai sun kuma tabbatar mata da cewa" Ahyaan bazata Auri Abdallah Mashi ba.Awajen Aiki idan sun had'u ta dena gaidashi sbd baya Amsawa sai mugun kallo dayake watso mata"gashi tun zuwan da yayi sukayi baran baran be koma zuwa ba"hakama baya kiranta ta waya"tun Abin baya damunta harta fara shiga damuwa"sau tari mamy na tambayarta meyasa yadena zuwa? zatace baya gari,waya kuma ta nuna sunayi"hakan yasa mamyn bata tsaurara bincike ba"Ahaka Al'amarin yaci gaba da tafiya har lokacin biki yafara karatowa "tun saura sati biyu Abdallah Mashi yaturo mata text message bak'i maza zasuzo su kawo lefe ta sanar a gida"tayi shiru tak'i fad'ama kowa sbd Aganinta ya rainata over"ita yanzun wani irin haushinsa da k'insa takeji"gaba d'aya yanzun batada Aiki saina tunani"Aranar saidai kawai su Mamy sukaga bak'i sun musu zuwan bazata"saidai Alhamdulillah Am musu tarban  mutunci"sun kawo Akwati 12 da kaya na Alfarma Aciki "ko kallon kayan Ahyaan bata yiba"hakama Dr darma "dan Aranar kasa gane yanayinsa mutanan gidan sukayi.washe gari kuma Ammah ta Aikoma Ahyaan da kaya sabbi kala 6 d'in kakku na fitar biki"lace kala 2, Atamfa kala2, shadda ma kala2"kowanan su da gyalensu"manyane masu tsadar gaske "Acewar Ammah idan Ahyaan ta shiga gidanta tayi Amfani da kayan lefenta Amma wa'annan sun isheta ta saka Ayi hidimar biki a gama.ga million 5 kakanta ya Aikoma mamah dasu Asiya mata kayan d'aki"ta kuma damk'asu ga hannun Abba ya had'a da million 2 dake wajensa zasuyi mata kaya masu tsada irin na y'an gayu�"mamy kuwa itada daddy sun tara kayan kitchen na gani na fad'a masu tsadar gaske"wasuma da kad'an kad'an tafara tarawa "wasu kuma Aka k'ara Ayanzun"sun bari sai ranar jere su bayar"mamy kuma ta sanar ma mamah Abarta da kayan kitchen sbd itace uwar d'iya"dukda kayan da suka siya saida daddy ya siyama Ahyaan fridge LG da washing machine "mamy kuwa duk idan tayiwa Dr darma mgn meye zai siyawa Ahyaan yabata kyauta sbd Auren da zatayi? be cewa komai sai dai taga yayima gidan yaji na kwana 2.
     Ayau yakama Friday wanda yayi daidai da  biki saura 12 days ya rage"gyaran Amarya An barsa sai zuwa jibi za'a fara yimata"misalin k'arfe 4:39 pm"Ahyaan na zaune a parlourn mamy tayi tagumi Abin duniya ya isheta"ta rasa mafitah"tana tsoron sanarwa iyayen nasu matsalarta da Abdallah musammun dataga yadda Aketa shire shir."ga wata iriyar soyayyar Dr darma dake dawainiya da ita"rabonta dashi tun safe"shima bata gansaba muryansa kawai taji"ta fahimci fushi yakeyi da ita sbd yakirata sau 3 jiya bata d'auka ba.Ajiya tasha kuka da tsayuwar dare Akan Allah ya kamata mafitah yazab'a mata Mafi Alkhairi.tana Anan zaune Khairiyyah ta shigo cikin parlourn da sallama tana fad'in Amarya bakya laifi"hmmm ! kece da yamma nan?"wlh kuwa ba dole nazo ba"biki ya rage  saura 12 days ba'a bugo invitation card ba da zamu rabama friends d'inmu"kuma yaka mata nayi mgn da Abokinsa "muji dame dame zamuyi na biki?"shiru Ahyaan tayi ta wuce kitchen ta kamata ruwa da lemo...byn kusan shud'ewar mintina 10 Ahyaan batace komai ba har mamy ta fito suka gaisa da Khairiyyah ta fita ta basu wuri.wai ni kuwa k'awata lafiya ne baki ce komai ba na miki mgn game da Abdallah?? me kiceso nace miki Khairiyyah?"mutumin da rabonsa da yazo wajena wata biyu kenan,rabon daya kirani Awaya yafi wata biyu"idan mun had'u









