Showing 57001 words to 60000 words out of 112373 words
Chapter 20 - AGE MATE'S Complete Document book by Momy Fareesa .txt
 kunnah kallo"yayinda mamy ke kitchen tana miya"har 12: pm ta wuce yana nan yana kuma mamakin meyasa Ahyaan bata dawo ba?"yana so ya tambayi mamy kodai ta biya wani waje ,Amma kuma yana jin kar tayi zaton wani abu sbd yanzun ba sosai yake shiga sabgartaba saiya kama"to itama mamyn tayi mamakin ganin har 12 tayi bata dawo ba"sai ta bari idan d'aya tayi bata dawo ba zata kirata taji lafiya6?...."Dr darma kuma k'arfe d'aya na idawa ya fito tsakar gidan yayi Alwallah ya tafi masjeed....tun bayan ya gama sallar yana Azkhar yaji Alamar shigowar text message"har zaiyi biris dashi sbd wasu duk y'an mata ne masu turo tambayoyi"sai kuma zuciyarsa yaji tak'i nutsuwa"kawai saiya zaro wayar tafara dubawa....be bari yakawo k'arshe ba ya zaro Ido cikin tsinkewar zuciya had'e dajin wani irin k'aimi da tasowar mazan taka ya maida wayar cikin Aljihun wondonsa yana furta innalillahi wa inna ilaihir raju'un! "Arikice ya baro masjeed d'in harda gudunsa ya nufo cikin gidan sbd basuda Nisa da masjeed d'in ,Anan cikin layin yake"kai tsaye d'akinsa ya bud'e ya shiga ya nufi saman bed side drower ya d'auki laptop d'insa ya saka number nata ya fara treaking"cikin sa'a ya gano Anguwar da wajen da suke "yana huci yace"wane Abubakar ne inba mahuta ba?...."zan nuna masa cewa shi k'aramin d'an iska ne"yak'are maganar yana fitowa daga cikin d'akin, ko key be sakaba ya jawo k'ofar ya nufi wajen motarsa rik'e da laptop d'in ya shiga yajata Ahaukace da wani irin mahaukacin gudu...yana hanya mu'az ya kirashi "yaja tsaki yak'i d'auka"ganin yak'i dena kiran nasa ya saka ya d'auka "Abokinah irin wannan sharewa haka?madam ce babu lafiya shine nakeso kazo gida ka dubata pls l...."babu lafiya mu'az"Mr mahuta yasaka Ansace Ahyaan! Innalillahi wa inna ilaihir raju'un! wlh kuwa inama hanya zanje wajensu na gano inda suke danayi treaking"sbd ta turomun text message yanzun.... Amma darma kaje kai d'aya? bayan kasan yana tare da y'an daba"kamata yayi Ai kaje police station kayi report ko?"banida wannan lokacin mu'az"indai zan ceto rayuwar Ahyaan koda nizan rasa tawa rayuwar ba damuwa"na sanar maka ne sbd koda bandawo ba kasanarwa su  daddy....yana fad'in hakan ya yanke wayar.
     tafiyar mintina 20 ta iso dashi Anguwar "ba mutane sosai sbd duk dajine sai gidajen da Aka fara gini Aka dena"gaba d'aya yama rasa Ina zaiyi?"sai Akaci sa'a wata had'ad'd'iyar zukek'iyar mota ta wuce ta gabansa"Atare ransa yabashi motar nan ta Mr mahuta ce"saida tayi Nisa saiya cigaba dabin sawun motar"daga bisani yayi parking yakoma treaking number"Adaidai nan wajejen Ake nuna masa Alamar number da yake treaking d'in tana nan"ya sauke Ajiyar zuciya gabansa gadi yafito daga cikin motar yayi lock nata"ya doshi get house d'in da ransa yabashi nan ne"cikin sa'a yaturo k'ofar get d'in saiya bud'e ya hango me gadi zaune,ga motar daya biyo fake a gefe"babu wani d'ar yanufi inda me gadin yake ya bashi hannu sukayi musabuha kafin yace"pls ko yallab'ai na ciki?"munyi waya yanzun yacemun yana hanya"Eh yanzun ya shigo Amma yasan da zuwan naka ne?"Eh yasani"dato kawai me gadin ya Amsa sbd bama yaro bane"Dr darma kuwa k'irjinsa keta bugawa babu wani tsoro yadoshi wata kwana da zata sadaka da hanyar  parlourn gidan"yana shan kwanar ya hango Mr mahuta tsaye shida wani saurayi yana mik'a masa wata roba ta swan suna mgn"saidai bejin me suke fad'a....tsaye yayi cak yana tunani"sai kuma yasaki wani Miskilin murmushi irin na tsantsar mugunta yaci gaba da tunkaro su "kan idonsa saurayin ya shiga cikin parlourn "Mr mahuta na juyowa yayi Arba da Dr darma na nufo inda yake"gabansa ya yanke yafad'i! ya zaro Ido yana yin wata zabura"Dr darma yakoma sakin murmushi Akaro na biyu yana zaro wayarsa da mu'az ke kira"hellow! sai kuma yace"ta wannan layin nawa zakubi diddik'i harku gane inda muke"dakun iso zakuga motata gaban get d'in gidan me orange d'in get"ya fad'a yana yanke wayar"saiga katti ukku sun fito daga cikin parlourn suna tunkarosa da manyan makamai Ahannunsu"yayinda Mr mahuta ya wuce ciki da sauri cikin tashin hankali yana tunanin yaya Akayi wannan gadararren yaron yagano inda suke??"yana shigowa ya sami Ahyaan da Ikkhee na dambe sbd tak'i yadda ta bata ruwan d'aya turo dasu Abata"wanda dama tun d'azun data sume , Ikkheen ta yayyafa mata ruwa ta farka shine k'attin suka nuna mata maka mai wai saita sha ruwan"shine tak'i yadda har suka fara dambe da ita"suna cikin damben Mr mahuta yakira k'attin"suna fita Ahyaan ta fisge face mask d'inta"Atake fuskarta ta bayyanah"Ahyaan ta kama murmushi ta matso ta finciketa ta d'auketa da wani gigitaccen mari "suka kacema da dambe"Adaidai nan Mr mahuta ya shigo yabisu da kallo sbd ganin Ahyaan ta haye saman Ikkhee tanata jibgarta cikin zafin zuciya "wanda ita kanta Ahyaan d'in bata san tanada wannan zuciyar ba....bilkisu !meye haka kukeyi?"da sauri Ahyaan ta d'agata ta juyo suka had'a Ido da Mr mahuta"gabanta yafad'i ta zaro Ido tana mik'ewa tsaye "Ikkhee tayi kukan kura zata cafkota Mr mahuta yadakar da ita"hakan yayi daidai da shigowar Dr darma cikin parlourn "daga tsakkiyar tafin hannunsa na d'igar jini"da Alama yasha Artabu da k'attin ne"Ahyaan na ganinsa ta saki kuka da gudu ta nufesa"tun kafin ta iso yabud'e mata hannayensa"tana isowa ta fad'a jikinsa ta k'ank'amesa tana fad'in broth kai kad'ai kazo?"ciwo suka jimaka ?"ta fad'a tana kama hannun nasa me zubar da jinin tana dubawa"be iya furta komai ba dukda suna cikin yanayin tashin hankali saida yaji tsikar jikinsa ta tashi da wannan rungumar da Ahyaan ta masa....saidai ya dake sosai ,yabi Mr mahuta da kallo sbd ganin yana sai tashi da bindiga"murmushi ya saki me ciwo kafin yace"Ina mazan suke?"daga kai har su duk lusarai ne banga namiji Acikin kuba"kaji kunya daka tsaya had'a kai da jahilar k'anwarka da shaye shaye ya gama burkitama brain"kai kana ganin zakaci nassara Akan mu ko?inaso kasani duk wanda yadogara ga Allah in sha Allah saiya isar masa da komai"wannan bindigar banzan bazai saka na fasa fad'an Abinda nayi niyaba"nan gaba kad'an zaka san lallai kayi kuskuran had'o wasanka da d'an karamin yaro,kuma yaronma talaka"karka manta last time daka saka aka saceni na barka"saidai tunda har Abin naka yazo kan bestie nah! Uhmmm"ya k'are maganar yana d'allah yatsun hannunsa guda biyu cike da izzah yana hura hanci"itadai Ahyaan na mak'ale Ajikinsa tana mamakin izzarsa da rashin tsoronsa"dukda dama tasan jarumi ne beda tsoro Amma tayi mamaki dayaga bindiga be tsorotaba....ke kuma tunkiya dak'ik'iya muna mata"dake za'a had'a baki Aci mutuncin y'ar uwarki mace"saidai banyi mamaki ba sbd dama duk d'an shaye shaye beda maraba da Dabba.....kaiiiiiiii! ya isheka haka"kana zaton ka Isa ka shigo har nan ka sameni kana mun wannan burgan banzan ka kuma fita salin Alin?. Idan ma kana wannan tunanin to kayi gaggawar denawa"da kai da ita Ayau....shiru yayi ya kama b'abb'aka dariya dukda maganganun Dr darma na sukar zuciyarsa "Amma saiya basar yakama dariyar k'eta sbd ganin wasu y'an daba su biyar sun shigo cikin parlourn"wanda yanzun yamusu flashing suka iso"yayinda Ikkhee ke zaune tana kallonsu tana kuma tuninin dama yayanta yasan Dr darma kenan?"shine yayi Amfani da ita sbd yacimmah wata manufarsa.....me kuke jira dashi ne?"inaso ku farka mun cikin banza"kuyi gutsi gutsi da namansa"Dr darma yayi saurin cika Ahyaan data fara kuka sbd Azatonta bazai iya da k'attin ba "suna da yawa ga ciwo yaji ga kuma bindiga Ahannun Mr mahuta"wani irin mugun kallon tsana ta watsoma Mr mahuta tare da fad'in ban tab'a jin tsanar waniba kamar yadda nakejin taka" in sha Allah saika wulak'anta a idon duniya"mugu ! Azzalimi.....shiru tayi sbd ganin Dr darma da k'attin suna Artabu"Mr mahuta na tsaye yana kallonsu gabansa na fad'uwa tana mamakin jarumtar yaron"yayinda Ikkhee ke zaune tana binsa da kallon tuhuma"Adaidai lokacin sukaji Harbin bindiga da jiniyar motar y'an sanda"Antar cikin Mr mahuta ta kad'a"yayinda k'attin suka saki makamansu zasu gudu"da sauri Ahyaan ta duk'a ta d'auki wani k'arfe ta jefi Mr mahuta dake k'ok'arin bud'e wata k'ofa shida Ikkhee zasu gudu"Adaidai  gwiwar k'afarsa ta dama k'arfen ya sauka"yasaki k'ara yafad'i "yayinda Dr darma ya rik'e k'atti biyu"sauran suka fita da niyar su gudu"sai sukayi clashing da polices kusan guda 12 dake k'ok'arin shigowa cikin parlourn ,Atake suka sai tasu da bindiga"yayinda wasu suka shigo tare da mu'az"Dr darma ya hankad'a k'attin suka fad'i k'asa "mu'az kuwa da hannu yanuna musu Mr mahuta dake yashe k'asa rik'e da gwiwar k'afarsa"yayinda Ikkhee keta zare Ido gabanta na dukan Tara Tara.
      gaba d'aya Aka kamasu suka fito daga cikin parlourn "Ahyaan kuwa hijab nata Dr darma ya matso gabanta  ya gyara mata suna kallon cikin idon juna cikin wani yanayi "Idanunta cike da k'wallah"saiya girgiza mata kansa Alamar kar tayi kuka"ta lumshe Ido ta koma bud'ewa"murya can k'asa tace"broth sannu da k'ok'ari kaji?"yanzun sai muje kayi dressing d'in hannun naka ko?"kansa kawai ya gyad'a mata beyi mgn ba"haka kawai ta rungumesa ta rushe da kuka"shidai mu'az na tsaye yana kallon su yana d'an murmushi"Adaidai lokacin kuma AA Mashi da wasu police suka shigo cikin parlourn.....��
wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
 Acc n  2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251
dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba 
Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn
Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba
#Mommyn fareesa 
#Dr Nura Darma
#Ahyaan 
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: ��♀� *AGE MATES* �
*43&44*
*Littafin kud'i ne!*
.........da wani irin kallo me wuyar fassara AA Mashi ya bisu dashi ba tare daya yi mgn ba "yayinda mu'az ya danne dariyarsa sbd kishin daya gani k'arara afuskar ko wannan su"daga Dr darma har AA Mashin"Ahyaan kuwa bata damu ba ta d'ago kanta suka had'a Ido dashi ta yamutsa fuska tana cika Dr darma tace broth muje ko?"yana wani hura hanci had'e da shan k'amshi yayi gaba ba tare daya ce komai ba"da hannu AA Mashi yayima police d'in Alamar suje sbd dama bbu kowa cikin parlourn..... Ahyaan kina ganina shine zaki wuce kibi wani?"cak! ta tsaya ta juyo ta kallesa sama da k'asa tana yamutsa fuska tace"waye wanin?"oh naji wani ne bah"Amma yafika tunda ya Ajiye kome yakeyi yazo nan cikin k'ila wa k'ala ba tare daya damu da Abinda zai samesa  me kyau ko Akasin hakan ba."idan har kai na tsaya zaman jira da kafin kazo komai marar kyau yafaru dani"yanzun kayi Adalci kenan Abdallah?"matsayinka na mijin da zan Aura har saika zo da police ?"meyasa ba zaka fara zuwa ba su sun biyoka daga baya ??sai kuma ta girgiza kanta zata wuce....kin gama?"haba Ahyaan ! ya kikeso nayi da raina?"sadda naga sak'onki lokacin kusan mintina 20 da kika turosa"bayan na gani natafi police station nayi musu bayani "Agabana sukayi treaking na number d'in shine mukazo"Ashe ban miki gwanin taba?"niba raggo ko matsoracin namiji bane"iya Abinda na sani gara komeye ace da sanin hukuma"idan nazo nika d'ai Abu marar kyau yafaru ko kuma dani dake duka aka cutar damu me gari ya waya??"numfashi ta sauke sbd ko yaya tad'an gamsu da kalamansa"shikenan kayi hak'uri "dama shima broth na tura masa sak'onne  shine saiya zo"muna nan yanata fad'a dasu saiga police d'in da Abokinsa yazo dasu"shikenan naga Abubakar mahuta me hakan ke nufi?"labarin me tsayi ne muje bakin get muyi mgn "banaso ka bari ya sub'uce daga hannunsu shida k'anwarsa"kasan dai yanada kud'i da power,hakama mahaifinsa??"tabbas nasan da hakan muje na kira Abba na masa bayani(mahaifinsa)"batace komai ba suka fice daga cikin parlourn "saidai koda suka iso bakin get babu su Dr darma da mu'az"sai ranta yabata suna police station "tunanin hakan yasaka ta shiga motar AA Mashi suka d'auki hanyar police station d'in"tana kuma yimasa bayanin tun farkon had'uwarta da mahuta da kuma yadda Akayi k'anwarsa tasan Dr darma "ta kuma sanar masa taji Dr darma na masa zancen kwanaki yasacesa"okay zamuji daga bakin shi Dr d'in taya yasaka Aka sacesa? "Okay ta fad'a"motar ta d'auki shiru"can ya kalleta yace"Amma Abinda kikayi d'azun kin kyauta Ahyaan?"ya fad'a fuska bbu walwala yana yin parking gaban police station d'in "menayi daban kyautaba?"saida yatab'e baki kafin yace" Ajikin wani na sameki,shi Dr Nura d'in muharramin kine da har zaki masa irin wannan rungumar??"ki had'a jiki dashi Akan me?karki d'auka ko bansan Alak'ar ku bata jini bace.....kaga dakata Abdallah! ban damu da koma miye ka d'auki Alak'ar muba"iya Abinda nasani Ina jinsa tamkar su Affan da muke ciki guda"ban rungumesa da wata manufa sbd nafika sanin waye shi"na rungumesa ne sbd kukan tausà yin kaina da Abinda yafaru ya jajirce bayan bbu kowa nawa Awajen sai shi."idan kai ka d'auka da wata manufa nayi hakan to mubarshi Ahaka"ta fad'a tana bud'e k'ofar ta fito ranta Ab'ace "tsaye ta hango Dr darma shida mu'az Agefen motarsa"hannun nasa dake zubar jini An d'aure masa shi da wani k'yalle"fuskarsa babu Alamar rahama cikinta"yanata cika yana batsewa"yana ganin Ahyaan ta nufo inda suke ya k'ara had'e rai"tun kafin ta Ida isowa wajensu ya nuna mata bayanta da hannu tare da cewa"karki k'araso  nan juya ki koma daga inda kika fito"mu'az ya girgiza kansa dama tun d'azun da yaga yana hakan yake bashi baki Amma yak'i saurarensa sai cewa yakeyi zai fita harkanta....haba broth! dame kakeso naji?"Abdallah nata cab'amun mgn sbd kai "nazo wajenka kaima kana neman ka b'atamun rai kayi hak'uri dan Allah kaji?"sai kuma ta saki kuka"mu'az da yaga haka sai kawai ya basu waje ya wuce cikin police station d'in "wanda Atare da AA mashi suka shiga ciki"kuma shima yana lura da Ahyaan wajen Dr darma ta nufa sai be kallesuba ya wuce Abinsa ciki kawai.....wani irin zafi da rad'ad'i yaji Azuciyarsa sakamakon jin sautin  kukan nata, besan lokacin daya matso dab da ita ba yana furta to wai miye Abin kuka Anan Ahyaan ?"bakai bane kak'i hak'ura"shikenan na hak'ura ki dena kukan to"shikenan muje gida mana"ta fad'a tana goge hawayenta "yanata kallonta yana jin kamar ya mannata Ak'irjinsa ya girgiza kansa Ahankali yace"zamuje Amma sai idan munji yadda case d'in zai kasance"sanin kankine zasu iya burkitasa"sannan munyi waya da mamy na mata bayanin komai"dukta damu tace na maidoki gida"dama nasan dole mamy nah ta damu"bansan meye wasu daga cikin mutane masu dukiya suka d'auki kansu da rayuwa ba??"dama wannan banzar k'anwarsa ce?"Eh yafara labarta mata zuwansu Asibiti kwanaki da irin yarfin daya musu"ka kyauta broth"ta fad'a tana murmushi"sai kuma tace"Amma meyasa daya d'aukeka kwanaki baka sanar mun ba?"ta fad'a suna had'a Ido "d'an tab'e baki yayi kafin yace"lokacin naga bana gabanki kuma kina gaba dani.tana k'ok'arin mgn sukaji muryar mu'az Abayan su yana fad'in Abokinah kuzo kaida bestie naka a office d'in AC yana son mgn daku"yana fad'in hakan ya wuce bejira cewar suba"Dr darma ya kalleta yaga tunanima takeyi"kinji me yace?"uhmm"iya Abinda Aka tambayeki zaki bada Amsa"inkin san zaki kula saurayinki Acan to kije ke kad'ai....haba broth wane irin mgn kakeyi haka?"Eh kokin manta d'azun yakira ni da wani?"wato nine wani Awajenki ko?"yafad'a cikin zafin zuciya yana hura hanci"wai bakace ka hak'ura ba?"kumafa na nuna masa be kyautaba "yayi shiru "kaji bestie?"murmushi ya sub'uce masa saiya gyad'a mata kansa suka wuce ciki Atare.
       sun kwashe kusan mintina 30 suna tattaunawa Acikin office d'in AC"har mahaifin Abdallah Mashi da Abokinsa wani minister suka k'araso "sai gashi k'aramin case yakoma babba"wanda badan sbd mahaifin AA mashi ba da Mr mahuta ko Awa bazaiyi ba a cell daga shi har k'anwarsa "koda suka fito daga cikin office d'in kai tsaye cell d'in da Mr mahuta ke ciki Ahyaan ta nufa"yana tsaye ya cire malun malun nasa yana tura sak'o ta text message "yana jin motsin tsayawar mutum yasaka wayar Aljihu ya kalli daga gaban k'ofar suka had'a Ido da ita "tana binsa da mugun kallo "Amamakin ta sai taga ya kama b'abb'aka dariya yana nunata da yatsa bbu wani d'ar yace"Ina Mai tabbatar miki da cewa nanda 20 minit saina bar nan wajen"dake da banzan d'an uwanki na kalan dangi dashi wanda zaki Aura duk sai kun gane kuranku"sannan Ina kan bakana Akan ki saina yaga miki rigar mutunci"na lashi takobin kota tsiya kota Arzik'i saina huta dake...d'an murmushi Ahyaan ta saki Anutse tace"idan Allah ya yiwa bawansa sutura da rigar mutunci babu wanda ya Isa ya keta masa"inaso nanda 10minit kabar nan bama 20minit ba "Ina kuma me tabbatar maka da cewa daga kaina ka gama shiga harkan wata"daga kai har k'anwarka da shaye shaye ya gama lalata ma brain"karka manta Ina tare da kariyar ubangiji nah kai baka Isa ka cutar dani ba"ko nassarar saceni da kuka samu to dama Allah ya rubuta hakan saiya faru....K! dallah ya Isa haka kije mana"ni banga Amfanin zuwanki Anan ba"iya Abinda na sani ba'a game dani Atashi 0-0 ko 1-1"saidai Atashi 0-1"okay ba damuwa Allah yakaimu Monday lafiya zakaga firanmu dakai Ayanzun tana yawo"wawa lusarin namiji kawai ! kuma k'aramin d'an bariki...tana fad'in hakan tayi gaba"Mr mahuta ya zaro Ido yana y'an kalle kalle Acikin cell d'in gabansa na fad'uwa "jikinsa na bashi Akwai CTV camera kenan?"Atake jikinsa ya fara keto zufa"sai yaji beda k'warin gwiwar tura sak'on dayake so yatura..... Ahyaan kuwa ranta fari k'ar ta fito daga cikin police station d'in"dama Abdallah Mashi ne  yabata shawaran suyi haka ranar monday Awatsa vedio d'in a news daga nan kowa yasan waye shi harda iyayensa "kafin su shiga koto"ta hakane zai gane yayi kuskuren had'o wasansa da y'an jarida....Dr darma da mu'az na tsaye gefen motarsa suna mgn "Abdallah Mashi shi kuma suna mgn da Abbansa da Abokinsa"cikin jin nauyi Ahyaan ta k'araso ta sanar masa komai ya kammala"Abba yabita da kallo yana jin kunyar yarinyar ta burgesa"shi dama besan taba Azahiri a TV yasan itace d'an nasa zai Aura....tun kafin AA mashi yayi mgn Ahyaan ta wuce wajensu Dr darma sbd tasan ita suke jira"bestie! ta fad'a tana kallonsa"mu'az yayi mamakin jin sunan data kirashi dashi"yayinda me gayya me Aiki beyi mamaki ba sbd d'azun ma da haka ta kirashi"saiya kalleta ta turo baki tana fad'in mungama mu tafi gida ko?"okay Abokinah zamu wuce"saima lokacin ta tuna









