Showing 72001 words to 75000 words out of 112373 words
Chapter 25 - AGE MATE'S Complete Document book by Momy Fareesa .txt
 office na gaidashi baya Amsawa hakan yasa na dena gaidashi"sai mugun kallo kawai zakiga yana jifata dashi"Ahaka zan Auresa nayi zaman bak'in ciki? Innalillahi wa inna ilaihir raju'un! kodai kin masa wani abun ne?"nifa tun ranar da mahuta da k'anwarsa suka saceni daga ranar na rasa gane kansa.ta shiga labarta mata komai harda zuwansa na k'arshe da yadda sukayi"ta d'ora da fad'in zan iya rabuwa da kowa sbd broth"Aciki harda shi"bazan b'oye miki ba Khairiyyah wlh broth nakeso bana son Abdallah"zuciya wata irin Abace"ko a mafarki banyi zaton zan so Age mate d'ina ba Khairiyyah "gashi wuri ya k'ure mana"inda Abdallah be canza mun ba dana hak'ura na rungumi k'addara na zauna dashi Amma kash! sai ta saki kuka"wlh k'awata tuni na fahimci doctor sonki yakeyi"ban yarda yana sonki ba saida aka saceki yaje "gashi kema da kike masa tutsun kin kamu"saidai gaskiya wannan ba matsalar da za'a yi shiru bace"dole Asasan taku ko kuma idan be sonki ba dole ya Amshi kayansa Allah ya had'a kowa da rabonsa"bani wayarki na kirashi"wlh bazaki kirashi da waya taba yayi zaton ko nice zanyi mgn dashi"shikenan samun number nasa Awayata"ta fad'a tana mik'a mata tata wayar"ita kuma ta Amsa ta saka number ta mik'a mata "Atake Khairiyyah ta kirashi"sai gab da zata tsinke ya d'auka yayi sallama ta Amsa ta gaidashi"kafin tace"Khairiyyah ce k'awar Ahyaan "saida ya yamutsa fuska kafin yace"to sai Akayi me?"ikon Allah!"to dama ba wani abu bane yasaka na kiraka, nazo wajen Ahyaan muyi mgn game da batun cards na gayyah "sai tace baka bugo ba"shine nace bara na kiraka naji,kuma yaka mata muyi mgn da friends naka sbd wuri yafara k'urewa"sai mgn ta k'arshe na fahimci kaida Ahyaan kun d'an sami matsala"idan har ba damuwa kazo gidan yanzun Ina can zamuyi mgn "numfashi ya sauke murya bbu Alamar wasa yace"batun event's na biki na sokeshi ba'a yin wata bidia "sannan ni yanzun inada Abinda nakeyi Agabana sbd ku bazan Ajiyesa nazo ba"idan ita wacce ta sanar miki da matsalar ta damu saita ce ta fasa taga zan dena rayuwa sbd babu ita ne.....kai Abdallah ka iya bakinka! Khairiyyah ta katsesa Afusace "kafin taci gaba da cewa"k'awata ta wuce wulak'anci wlh"kai muka fi buk'ata kace ka fasa kaga bazata samu wanda yafika ba"iyayenmu ba k'ananun mutane bane sbd haka kasan me kake fad'a"mitsssssuww Aikin banza kawai"in sha Allah sai kayi dana sanin Abinda kayi"ta fad'a Ahassale tana yanke wayar....��
wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
 Acc n  2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251
dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba 
Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn
Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba
#Mommyn fareesa 
#Dr Nura Darma
#Ahyaan 
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: � *AGE MATES* ��♀�
*53&54*
*Littafin kud'i ne!*
........ Ahyaan ta bita da kallo tana furzan da wani zazzafan huci daga bakinta ta girgiza kanta cikin k'unar rai tace"kin gani kin kuma ji ko?"sbd haka Ina Mai tabbatar miki da cewa koda ya Aureni wlh bazan bari yataka niba....ah ah Ahyaan bana miki fatan kiyi Auren da zaki fito kamar yadda nayi ba"gara kiyi Auren da mak'iya zasuji haushi ba dad'i ba"ni Aganina ki kira mamy na sanar mata mana"idan daddy zata yima mgn saita masa mgn" Akirashi Aji idan bazai Aureki ba yafad'a shikenan"da dai Azo Ayi Abinda za'a yi dana sani"Ahyaan ta girgiza kanta tana fad'in gaskiya bazan iyaba Khairiyyah"dadai tun Abaya yaka mata nayi hakan banyi ba"zan cigaba da Addu'ar zab'in Alkhairi kawai"bbu wanda zai koma kiransa har ranar bikin yazo"uhmm !Ahyaan kenan" karki manta na rigaki yin Aure nasan Abinda baki sani ba"ni bana so kizo kiyi Aure daga baya ki fito"Amma kiyi nazari na baki kwana 2"sannan ki dage da Addu'ar neman zab'in Alkhairi "k'ilan ma dakin yarda da shawarata Anyi mgn idan  yafasa Aurenki sai kucigaba da soyayyar ku da Dr Nura ko?"harara ta ballah mata tana fad'in kinga ki dena mun zancensa ,shima bbu ruwana dashi"bazan biyema son zuciya sbd wani burinah ba"tabbas Ina son broth Amma banaso sbd Ina sonsa na dakushe wannan Auren ta dalilin son nashi"nafiso koda za'a fasa to afasa sbd gazawar Abdallah badan sbd tawa gazawar ba.shiru na wani lokaci Khairiyyah tayi tana jin matuk'ar tausayin Aminiyar tata"tasan Ahyaan yarinya ce me hankali da hangen nesa tun suna secondary school"saidai wasu suna fassara halayenta dame girman kai da izzah da sauransu"saidai sun kasa gane raini ke bata d'auka...ta kalleta tace "in sha Allah komai zai wuce k'awata"Allah yana tare dake yasan zuciyarki da niyarki"na tabbatar idan watace kodan sbd Dr Nura zaki lalata maganar Auren Amma gashi bakiyi ba"ki dage da Addu'a nima zan tayaki.bara na wuce gida yamma tayi kar Hjy tamun fad'a "jiki Asanyaye Ahyaan tace to shikenan bara na sako hijab na rakaki"hijab ko mayafi?"kayan sun kamani fa"yanzun nan idan na fita da mayafi broth yagani zaita fushi yana b'ata rai "murmushi kawai Khairiyyah tayi batace komai ba, yayinda Ahyaan ta wuce ciki ta sako hijab  ta fito tana cewa bakima duba kayan lefen bako? ki barshi kawai tunda wanda ya kawo ba mutumin kirki bane"ni kaina ban dubaba har yanzun nama tsani kayan"shima broth be gani ba"ta k'are maganar suna fita Atare....sai gab da sallar magrib mutumin naku ya shigo cikin gidan Agajiye"saidai duk irin gajiyar daya kwaso idanunsa nason tozali da ita"koda bazasu yiwa juna mgn ba"yaso ya dake ya sabama kansa da rage shak'uwa da ita kodan sbd zata tafi tabarsa Amma yakasa"gaba d'aya zuciyarsa Akarye take indai Akan Ahyaan ne.murya can ciki yayi sallama ya shigo"tsaye yayi ya toge daga bakin k'ofar parlourn yana binta da kallo"tana zaune tayi tagumi! kallo d'aya ya mata ya fahimci tanada damuwa"yasan kuma be wuce shima irin  damuwar dake damunsa bace ke damunta"wato Auren da zatayi"Ahankali yanufi gabanta ya duk'a ya cire mata tagumin"ta sauke Ajiyar zuciya tad'an kallesa "ya sakar mata murmushi"ta shagwab'e fuska ta sunkuyyar dakai k'asa.menene ke damunki bestie?"Idanunta cike da k'wallah tace ba fushi kakeyi dani ba?"Aina huce dukda baki bani hak'uri ba"tayi shiru"ya cire hular saman kansa wacce tayi shige da zaren  da Akayi Aikin yadin jikinsa ya Aza mata saman kanta yana fad'in baki son d'aura d'an kwali "ta d'ago kanta ta turo baki sai kuma murmushi ya sub'uce mata"yanata kallonta yace ta miki kyau"nidai broth ka ciremun kar mamy ta fito"nidai gaskiya bazan cire miki ba"tukunnah ma miye ke damunki kikayi irin wannan tagumi kinsan kuma bana so ko bestie?"tayi shiru Idanunta na kawo k'wallah "bestie kuka da gaske?"saiya saka yatsansa manuniya ya fara goge mata hawayen nata yana kallonta yana jin kamar ya rungumeta Atsakkiyar k'irjinsa ko yaji sauk'in rad'ad'in da zuciyarsa keyi."cikin sanyayyan muryanshi yace"tashi muje daga waje"ya k'are maganar yana kama hannunta ya mik'ar da ita tsaye"da kansa yacire mata hular Ahankali ya maida saman kansa ,kafin ya d'auki hijab nata dake Ajiye saman kujerah ya mik'a mata "ba musu ta Amsa ta saka"koma kama hannun nata yayi suka fito daga cikin parlourn "daga ita har shi yanzun idan jikinsu ya had'u wani irin yanayi suke tsintar kansu Aciki"sab'anin Abaya basa jin hakan....daga gefen tape suka tsaya ita ta jingina Ajikin bango shi kuma yana tsaye daga gabanta"ya zuba hannunsa guda cikin Aljihun wondonsa yana Aikin kallonta"bestie! yakirata murya can ciki"uhmm! fad'amun meke damun ki da zakiyi kuka?tayi shiru "kinaso nima na shiga damuwa?"da sauri ta d'ago kanta suka had'a Ido ta girgiza masa kanta"sai kuma ta saki kuka mecin rai ta rungumesa.....rintse Ido yayi da k'arfi yana jin wani irin mugun shock A duk illahirin sassan jikinsa"ya lumshe Ido ba shiri"ya tabbatar suka k'ara mintinah 2 Ahaka shida ita zai iya yin Abinda zaiyi dana sani"saiya d'ago kanta murya a sark'e ya furta ya Isa haka Ahyaan "cikin dubara yad'an janyeta daga jikin nasa murya can k'asa tace"broth ni bana son wannan Auren"meyasa bestie?"dukda laifinki ne dakika zab'esa A matsayin miji ,Amma sam baku dace da bak'in mutumin nan ba"wani Abu ya miki ne?"ah ah kawai bana son Auren ne"meyasa to?"to zanyi kewarku ko?"ya girgiza kansa yana sakin murmushi me ciwo yace"nafiki damuwa da Auren *sarauniya* "zaki tafi kibar *sarki* ko? shiru tayi"kiyi hak'uri ki manta da batun Auren ki cigaba da walwalar ki"ki kuma dage da Addu'a zan tayaki"kanta ta gyad'a masa cikin jin gamsuwa.zo muyi Alwallah kar mamy ta fahimci kinyi kuka"kinga zata tambayeki ko?"kanta ta gyad'a masa "ya zare hularsa ya kama hannunta yace"to rik'emun nayi Alwallah "to idan Aka idar da sallar gida zaka dawo ko?"chemist zanje bestie "tayi shiru"ko bakyaso naje ne?"uhmm"to shikenan da an idar da isha'i zan dawo gidan"ya fad'a yana zare Agogonsa duk ya mik'a mata yana fad'in zonan kiyi gadinah na gama"kai broth !  sai kace wanda za'a sace ko kuma wanda kejin tsoro bayan nasan kai d'in jarumi ne.uhmm bestie irin wannan yabo haka"ya fad'a yana yin bissimillah ta bud'e masa tape d'in yafara Alwallah d'in"yanayi jefi jefi yana kallonta yana watso mata ruwa"itadai tana satar kallonsa tana murmushi"sai yabon kyawun halittar sa takeyi Aranta"saida ya idar ya matso dab da ita yace"to zoki d'auramun Agogon ko?tayi shiru tana turo baki"yayi murmushi yace"kinsan Allah saikin d'auramun"ya fad'a yana mik'a mata hannunsa yad'an ja hannun rigar"Atake damtsan hannunsa me gargasan gashi jajir ya bayyanah"saida taji k'irjinta ya buga ! da k'yar hannu na kirma ta d'aura masa"thank you! *Allah yasa wata ran ki d'auramun ki samu lada* "da mamaki ta kallesa ya d'age mata gira....wai Ahyaan kina Ina ne?"sukaji muryar mamy"da sauri ta matsa daga kusa dashi"gata nan zatayi Alwallah mamy"Nina tafi masallaci"ya fad'a yana gyara takalminsa ya kalli Ahyaan data fara Alwallah yace"bestie saina dawo "kanta ta gyad'a masa"ba Addu'a?"Allah ya tsare"shine zaka ja tana Alwallah tayi mgn?"cewar mamy tana komawa cikin parlourn"Ahyaan ta d'ebi ruwa ta yarfo masa"haba yarinya zan dawo Ai"yak'are maganar yana fita sbd beson yatsaya karma Alwallah d'insa ta k'arye.....bayan sallar isha'i tana zaune a tsakkiyar parlourn gabanta plate ne rufe da jug Agefe da cups"tana sanye da k'ananun kaya da mini hijab sai k'amshi takeyi fuskartar tayi haske da shek'i"hankalinta nakan waya "hamza na gabanta yana k'ananun kuka"ta d'ago kanta ta ballo masa harara tana fad'in koka fi k'uda k'wak'wa baza kaci wainar fulawar nan ba"nida broth keda ita"haba Ahyaan ! yanzun kin kyauta yaron na gani ki hanashi ki bama nurah k'ato dashi.dr darma daya shigo cikin parlourn ya karb'e zancen da cewa" haba mamy nine d'in k'ato "kai dallah tashi kabama mutane waje kona mareka"jikin hamza na b'ari ya nufi kusa da mamy ya rak'ub'e"yi hak'uri Autah kabar ni dasu"da safe tunda week end ne zan maka kafin katafi islamiya "Ahyaan na murmushi ta kallesa ta masa Alamar ya zauna"saiya nok'e kafad'arsa yamata Alamar shine babu sannu da zuwa?"da Ido ta nuna masa wai ga mamy na zaune"saiya zauna gefenta ta bud'e plate d'in wainar "da yake da fripan ta soyata saita d'auki guda ta saka cikin plate tace zodai badan halin kaba ka Amsa"mamy tace shikenan da Ina cewa shi zai miki zaman d'aki "na yafe gaskiya mamy"sukayi murmushi Atare "ta d'auki cup ta zuba masa sob'o me sanyi dake cikin jug d'in"wanda yaji kayan had'i yanata k'amshin plabo"saida ya mintsineta A hannu data mik'o masa zai k'arba"sai tayi kamar bata ganiba....wow !yayi dad'i bestie Ak'ara mun pls"ya fad'a yana tsotsar red lips nasa" sai kaci wannan zan baka"kin san fa bana shan yaji ko?
      shiru tayi tak'i yin mgn taci gaba da cin wainar da taji yanke yanke ga yaji gefe"lura da idan beciba bazata kula shiba sai ya saki d'an murmushi ya d'iba yafara ci Amma banda yaji"shi rabonsa da yacima wannan Abin yama manta.... bestie ki rage cin yaji ! yafad'a k'asa k'asa "miye Aibunsa ?"itama tayi maganar k'asa k'asa "zan sanar miki idan baza kiji kunya ba"to na fasa basai ka fad'a ba"wannan ne kuma baki isaba saina fad'a"sharesa tayi,shi kuma yazuba sob'on da kansa ya fara sha yana lumshe Ido "Aransa yana yaba baiwar iya girki da Allah ya bata"har suka gama mamy na zaune bata tashi daga cikin parlourn ba"daga k'arshe yatura mata text wai ta hau on-line sannan ya fita....
      shirye shiryen biki Aka cigaba dayi babu kama hannun yaro"ita dai Ahyaan ta nama y'ar kallo kamar ba ita bace Amaryar "tun sauran kwana 10 Aka fara yimata gyaran jiki"zuwa sati d'aya tayi mugun canzawa "k'amshi ya zauna Ajikinta"fatarta tayi laushi da sulb'i tana d'aukar Ido "saidai tayi y'ar rama sbd fargaba da zulumi"kusan kullum suna waya da Khairiyyah sbd taji ko Abdallah yazo"saidai zatace mata ah ah"gefe guda kuma mamy ta fara zaton tsakanin Ahyaan da Abdallah Akwai matsala "sbd ta tambayeta game da events na biki tace ba'a yin komai sai wa'azi "hakan yasa mamy da kanta ta saka Aka bugo invitation card"wa'azi da yinin biki kawai Aka saka"ta kuma sanarwa da daddy tana zaton Akwai matsala tsakanin Ahyaan da Abdallah"sai yace Abarshi sai ranar Tuesday da safe zai kirashi yazo suyi mgn dama Aranar za'a yi jere washe gari Friday Ad'aura Aure... Agefen Dr darma kuwa ba k'aramin tursasa zuciyarsa da kansa yakeyiba wajen jure rashin Ahyaan "kullum Addu'a yakeyi Allah yabashi ikon hak'uri da juriya da kuma dangana game da ita"baya so bayan Aurenta yaci gaba dason matar wani "sbd yasan illar hakan da zunubin dake Akwai....
     Ayau Alhamis Aka gudanar da wa'azi wanda ya girgiza zuciyar Ahyaan"har kuka saida tayi"Ayanzun tayi dana sanin k'in bin shawaran Khairiyyah ga biki saura kwana 1"sai bayan sallar magrib gidan yad'an rage hayaniya"kasancewar daga sashen su mamah har zuwa nasu mamy cike yake da jama'a"gashi Anyi gyare gyare na biki harda fenti Akayi.gefen ummah kuwa tanata murmushi da farin ciki Abinta musammun data fahimci ba'a je wajen jere ba"gashi gab da magrib taga Abba ya shigo cikin damuwa"hakan ya k'arama zuciyarta k'warin gwiwar An fasa bikin"sai walwala takeyi da yada yadan mgn"duk mamah na lura da ita"wacce itama tanaso Abban yanutsu taje suyi mgn taji dalilin da ba'a je wajen yin jere ba?....wajen k'arfe 7:18 pm Dr darma na zaune cikin parlourn shida Ahyaan da mamy "ba wata fira sukeyi ba"ita tana danna waya "shi yana binta da kallon k'asan Ido,mamy kuma tana kallon TV"wani irin rauni zuciyarsa tayi musammun da yaga irin gyaran da Ake yiwa Ahyaan ya canza ta.kamar daga sama Abba ya shigo cikin parlourn babu ko sallama yana fad'in Maryam ! Alh kabeer d'in be shigo bane?gaban mamy ya fad'i "sbd tasan tun saninta dashi be tab'a shigowa kai tsaye irin haka ba sai yau"sbd Abaya in zai shigo sai yayi sallama sau biyu daga waje"kuma saita Amsa yake shigowa"hakan ya tabbatar mata da cewa babu lafiya...be shigo ba Alh inaga sai bayan sallar isha'i koka kirashi ta waya ne"yana k'ok'arin yin mgn sukaga ya fad'i rikicah daga bakin k'ofar parlourn "gaba d'aya suka saki salati"Dr darma yayi hanzarin tashi ya nufesa ya d'ago sa yatab'a saitin zuciyarsa "yaji yana motsi"ya sauke Ajiyar zuciya yana fad'in karku damu suma ce zai farka "kafin yayi mgn sukaji sallamar daddy"sai kuma yasaki salati yana fad'in lafiya ?"mamy ta sanar masa,yayinda Ahyaan ke kuka"daddy yace"nurah kamashi muje parlou nah kamasa dubarunku na likitoci koya farka"dato ya Amsa suka kamashi suka wuce dashi ciki "saman 3 seeter Aka Azashi Dr darma yaje d'akinsa be jimaba yadawo da Abinda yake dashi dazai iya Aikinsa.cikin k'ank'anin lokaci Abba ya sauke Ajiyar zuciya "numfashinsa na dawowa"Dr darma yamasa wasu Allurai gefen kafad'a "daga nan yasamu bacci"ya dubi daddy Ahankali yace"karka damu daddy zuciyarsa ce ta buga! Allah ya sama bashida hawan jini da fad'uwar da yayi yanxun komai zai iya faruwa"Akwai wata mgn da Aka sanar masa marar dad'i itace ta haddasa masa bugun zuciyar"Amma yanzun Ana buk'atar ya huta"kansa kawai daddy ya gyad'a masa cikin damuwa"yayinda Dr darma ya fita daga cikin parlourn yana tunanin wace irin mgn ce Aka sanarwa Abba marar dad'i da har zai shiga irin wannan yanayin??
      k'arfe 10:5 pm haka Agogon dake cikin parlourn ya nuna"daddy ya kalli Abba da baifi mintina goma da farkawa ba yace"Alh iliyasu kai nake saurare ka sanar mun meke faruwa?wace irin mgn ce ta tashi hankalinka harka zube haka?"idanun Abba jajir yace"Akan maganar Auren Ahyaan ne Alh kabeer "Ashe yaron nan yaron banza ne ba shida mutunci"iyayensa k'ananun mutane ne"yazo d'azun da yamma sbd na kirashi batun yakawo motoci Aje inda Akayi order d'in kayanta su kwashe Aje Ayi jere"Abin b'acin rai wai sai gashi da zancen dan Allah nayi hak'uri wlh yanzun bazai iya Auren Ahyaan ba"badan ta masa wani abu ba kawai yaji bazai iyaba..... innalillahi wa inna ilaihir raju'un! wace irin maganar banzace wannan?"wlh kuwa"babban tashin hankalina meyasa be sanar da wuri ba saida wuri ya k'ure?munyi gayya gobe d'aurin Aure"gashi yana so ya zubar mun da mutunci da mutuncin y'ata"yanzun me kake zaton wasu zasu d'auka Akan wannan maganar na fasa Auren Alh kabeer ? wlh ko mahaifiyar yarinyar nan ban sanarma da wannan tashin hankalin ba"ban nuna masa na damuba sbd ban gaji da y'ata ba"nace kawai yaje gobe da safe yazo ya Amshi tsiyar lefensa"dama Allah yasa bata tab'a komai ba Aciki"saidai bayan ya tafi na kira mahaifinsa ta waya na sanar masa. hankali tashe yace be san komaiba suma shirye shiryen bikin sukeyi Amma bara yajirashi yazo suyi mgn baza'a fasa ba"nace ah ah nima na fasa bada y'ar tawa suzo su Amshi kayansu kawai"ban gaji da itaba,bazan bayar da itaba inda ba'a bukatarta"tunda ya nuna haka koda Anyi Auren bisa tursasawar iyayensa baza tayi wani farin ciki ba.wannan gaskiya ne! Ina goyon bayanka d'ari bisa d'ari daka nuna musu haka"Aure kuma baza'a fasashi ba da izinin Allah"Allah be kunyatar dakai ba bbu wani mahaluk'in daya Isa ya kunyatar dakai"dukda Abin yazo Amakare Amma wannan ba wani abu bane"goben in Allah ya kaimu za'a d'aura Auren nasu da Nurah "sbd dama Abaya na fahimci suna son juna dashi"bedai furta bane"bayan haka Ina ganin shak'uwa me girma tsakaninsu"bana zaton zamuyi dana sanin wannan had'in "Ajiyar









